Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 69

Chapter 69

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,271 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

mahaifinsa inajin tsoron kar xuciyarsa tajashi wani abu yafaru awajen shiyasa amman bari naje kaima inkana da time mu hadu can." Ai malik najin haka ya kafa kai ya shanye sauran costand din ya zari wayarsa don bazai fita da mota ba,addua yaje Allah yasa kar yaje ya aikata abunda bashine ba. Taxi ya tara yagaya mashi inda zai kaishin. Station Yana isa yaga motoci har guda uku yasan Abbin ne ya iso,fitowa yayi ya sake hade fuskarshi murtik kamar an aikobmashi da sakon mutuwa. Wani dan sanda ne yake bakin kofar shigar yasaka kafa ya ingijeshi yashiga. Biyosa yayi a fusace yana finciko rigarsa ta baya "uban waye kai da har zaka ingijeni kai makahone ehy..............naushin da ya kai mashi shiya janyo duk hankulan mutanen dake cikin station din. Saida Abdoul yafasa mashi baki sannan ya wurgar dashi yana huci. Abbi dayayi ido hudu da yaron nashi,duk zafin daya debo don juyewa akanshi saiyaji xuciyarsa ta karye,bayan shekara shidda ashe zai sake yin ido hudu da dansa,gudan jininsa.jikinsa yaji har wata rawa yake saboda tsuma da son rungumeshi ajikinsa,saidai yasan hakan bazata yuwuba yadda yagansa cikin wanna zafin ba tantama idan ya tabosa abun bazayyi kyauba,daman ga yanjarida canawaje sunajiran kiri sushigo sudauki rahoto. Watairin kaunar dan nashi yaji ta kamashi idonsa kamar zayyi kuka yaje inda yan sanda suka kakkamashi yace"ku sakeshi karkuji mashi rauni mana,ai laifin sane baiga ayadda yashigo wajenba ne zaiyi jaking dinsa." Sakale sukai da bakisuna kallon sa don sun san ba haka ya shigo ba yana zage zage ya shigo yana cewa duk ubanda ya bada umurninkar abada belinsa akirasa yanajiransa.amman gashi yanzu kuma sunga ba haka ba,shiyasa wani daga cikinsu ya nemo yan jarida yasan zai samu wani abu idan suka amu wannan labarin. Idon Abdoul yayi jaa yana kallon Abbin nashi can kasan ransa yana jinwani irin feeling amman sabkda abubuwan dasuka ringa dawo mashi na can baya sai yadanne yafixge daga rikonsu yana zakuda kafadarsa cikin bala,I yace"ina ruwanka da koma me zasuyi man?nace meye ne yasha feka dani muazzam,kabari suyi mun koma miye mana meye hadin kifi da kaska." Abbi jiyayi zuciyarsa tana ragargajewa rauni yana sake kamata wata irin nadama da dana sani suna shigarsa,matsawa yake inda Abdoul din yake muryarsa tana rawa yanason rikosa "daina daga murya yarona,nine fa Abbinka Abbinka ne maionka........dalla malam dakata anan karka sake ka nufoni,don zan maka rashin mutunci nace karka matsoni ko wlh zan maka abunda baka taba tunani ba." Alfah ke fadara haka yana hawaye,yanajin kamar ya dunga buga kanshi da bango. Hankulan mutane yafara yowa nan wajen. Abbi tuni idonsa yafara zubar da kwallar yana cewa"nine babanka Abdoul karka manta dani kar xuciyar ka ta saka maka tsanata,zoga babanka kajiko matso." Ja baya Abdoul keyi yana sake cewa"wlh idan ka matso inda nake saina kashe kaina,yafige wata bindiga daga hannun wani dan sanda yana saita kanshi da ita,daidai isowar yan jarida kenan da kuma zuwan dady da malik. Cikin rudu da rikicewa Abbi ya rike hannun dady yana kuka kamar ba babba ba yace"kaimashi magana karya halbi kanshi,kaje ka anshe bindigar yana iya halbawa tsoro nakeji inhar kana sona karka barshi yayi abunda yake niyya........ina sonsa ina son dana kaceceshi." Riko duka hannayaen Abbi yayi dadyn yana cewa"kwantar da hankalinka bazai aikata ba,ka natsu don Allah kalla fa kaga mutane yadda suke kallonka haba yallabai." Malik ne yayi saurin rike hannun Abdoul dake saita kanshi da bindigar yana sakin iyakar karfin sa,yana koklwar ansarta. Bilhakki da gaskoya kuka yake yana cewa, "Wallahi muffin yah I nasarar ceton wadancen yan ta addan saina yi abunda zaisaka dagani harshi mukare rayuwarmu agidan yari.taya zaoyyi yukurin ceton mutanen dake da hadari cikin al,umma masu satar jama,a suna yimasu allurar maye........kasakeni kafin kaima nayi maka illah...........wani gigitaccen mari dady ya sakar mashi yana sake lafta mashi wani marin,don baida wata dubara da ta wuce haka,yayi gigiceqr da baya saurren kowa. Shirune ya raysa wajen ya juya ga yan jaridar yace ma yan sandan duk wanda kuka kama cikinsu ku garkame shi tunda neman labari suke sai subada nasu yan iska ,basu da aiki sai neman rahoto suje su yayata." Abdul silalewa kasa yayi yana wani irin numfashi kirjinsa yana dagawa kamar zakifita daga jikinsa,inbada rawa babu abun da jikinsa keyi dole malik ya cikashi suna xuba mashi ido. Don Allah kuyi hkr wlh yau nashiga busy ga bakuwa danai ga hidimar gida shiyasa kuka samu wannan kuyi hkr plss. [9/24, 5:37 PM] Mom Muhseen: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSEER* *(ALFAH)* WRITTEN BY MRS BB MOM MUHSEEN FOR SALE 300 NAIRA ONLY 09034722970 🅿️........50 Dady ne yace"malik kamashi ku wuce gida,indan kan sune kake wannan haukan to ubanwa ya gaya maka zasu kubuta,bana son hauka da shirme comon get up" Mikewa yayi idonsa jajawur yana kallon Abbinsa,yana jin wata suya cikin kirjinsa bangare guda kuma yana jin wata irin kewa da soyayyarsa suna sake narkewa cikin ransa.nunasa yayi da hannu yajinjina kai har zai fita ya juyo yace"dady safiyya fa sukai kidnapped,suka mata allurar maye hankalinta ya gushe,kasan me likita yace akai?cewa fa yayi taci sa,a jininta yana da kyau in wasune har haukatar dasu take,wlh tallahi da wani abu ya sameta na rantse da Allah saina cirewa kowanensu yan yatsu,sannan na zuba dalma cikin kunnensu to kugode Allah babu abunda ya sameta. kaikuma yanuna Abbin sa,sai kuma ya girgiza kai yana ficewa daga wajen,malik yana bin bayansa. Ansar tukin yayi don yaga alamar zai iya saka su accident, Huci kurin yake yana dukan hannunsa da dayan hannun,ya kwantar da kansa jikin makarin kujerar yana jin xuciyarsa tana tafasa soyake ya samu wanda xaima dukan mutuwa,soyake ya huce hanshinsa ko akan waye soyake yaga yafitar ma dawani jini ga fuska ko ya samu sauki cikin ransa,malik ya juyo yana kallonsa yace"ka ringa sassauta ma ranka wannan xuciyar Abdoul wahala zaka ringa sha abanza awofi,karshe ciwon ka yatashi ka samu a uku" Harararsa yayi yana jan tsaki,malik dariya ya danyi yana cewa"ko akaina zaka huce ne" "Idan kacigaba da bata mun rai babu mamaki na huce akan ka tunda neman wanda xan hucen nake" "To bismillah sarkin karfi kai naga alamar ma kafi doki karfi" Yafada yana dariya cikin fada da masifa yace"ba doki na giwa ce ni,karka sake hauda fushin da bana ka ba bazakaji dadi na ba wlh" "Sorry sir" yafada yana sara mashi. Tsaki yaja yana rufe idonsa kurin,har sukaje gida bai sake magana ba malik ma bai tanka mashi ba. ********** Cikin kermar murya Abbi yake cewa dady. "Abdullahi wacece safiyya,ya take wajen Abdoul dina meyasa su mamman suka yi kidnapped dinta?" Bubbuga kafadarsa yake cikin nuna kwantar da hankali,yace wa dpo din "koda wasa bance a sakesu ba,inda hali acigaba a basu horo har sai sun fadi wanda ya sasu wannan aikin" "Yes sir" "Sannan ko kusa kar wanda yazo neman belin su abayar don sudin yan ta adda ne bama wannan kadaine laifisu ba,acigaa da asu horo mai kyau" "Okay sir" Riko hannun Abbi dady yayi suka fito. "Ina zaka dani baka gaya man abunda nake tambayarka ba" "Yi hkr yaya sonake muje inda zan baka ansar,don bama ita kadai kake bukata ba ansar akwai ansoshi da dama dakake bukatar saninsu." "Ina zamuje yanzu" "Gidana dake gwarumfa zamuje sonake yau kasan wata

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});