Chapter 49
Chapter 49
rashin kunyar ba KO?" Kamar wata sakarai nadaga Kai kurin,girgiza kanshi yayi yace"magana zakiyi" Kanta ta sadda kasa yasaka hannu sa ya dago habarta yace"look at me saiki min maganar" Kamar zata kurma ihu saboda abunda takeji cikin ranta. Daker ta lalubo maganar don muryarta ta dauke d'af kasa saka idonta tayi cikin Nashi din dan abun Yafi karfinta. "Bazan sake ba I'm sorry" "Kallona nace kiyi" Girgiza kai tayi tace can kasan murya"bazan iya ba" Koma wa yayi jikin kujerar motar yajingina yakasa tabuka komi gabaki daya jikinsa ya mace mat, "Inason wucewa gida kar amun fada" Ta fada kamar maikoyon magana. Bude motar yayi zuwa lokacin ruwan yayi sauki. "Babu bankwana" Har lokacin kanta akasa tace"sai anjima" Hannunta ya riko yana kallon xoben dake jikin yatsanta,idan bazai manta ba shiya siyesa kuma malik ya ba ajiyarsa tun wasu kaya da akakawo masu company yaganshi yayi bala,in burgesa yaji koba komi yana son sa duk randa Allah yasa yaji zai iya aure,saiyaba matar da Allah yacida ita har takawo matsayin matarsa. Wani irin kyau xoben yayiwa hannunta,inama zai iya sumbatar sa Amman ya akai yazo gareta,dole zaiwa malik wannan tambayar. Yagama kallon hannun nata yasaki fita daga motar yayi yarufe kofar. Silalewa tai ta kwanta tama rasa in da zata dora wanan abu cikin xuciyarta. Kuyi hkr wlh waya ta keban Matsala shiyasa najima bakujini ba,maganar yawan typing banyi maku alkawariba gaskiya,Amman Zan kokarta hidimarce dayawa wlh. Don't share it pls I beg Bcos its for sale,inkina ra,ayi Kituntubi wannan no din09034722970. [9/17, 3:41 PM] Fauziya Madaki: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSER* *(ALFAH)* WRITING BY. MRS BB MOM MUHSEEN. WATTPAD NAME HUMAIRA7531. *DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB AND ALFAH FANS* 🅿️.........35 Har karfe goma nadare babu baba babu labrinsa,tun abun bai damun mama har ta kasa tsaye ta kasa xaune. Yesmin ce kurin tayi baci amman fiyah da mama idonsu biyu fiyah nata karatu mama kuma tana jan carbi,amman zuciyarta rawa take tana jin tsoron ko wani abunne ya sake faruwa da baban. "Mama bakijin bacci ne" Yake tayiwa safiyyar tace"zan kwanta yanzu" Cigaba tayi da karatun tana satar kallon mamar ganin duk tafita hayyacinta,agogo ta kalla tace" mama har yanzu baba baidawo ba lafiya" "Wallahi safiyya ban sani ba duk dadewar sa baidawo ba bai wuce tara da rabi amman gashinan har shadaya saura baidawo ba,babu kati wayata kiraman shi da taki" Saurin dauko tata tayi itama tanajin tashin hankalin,laluben sunan baban take cikin jerin sunayen kiransa tashiga yi amman wayarsa akashe,gabanta yasake faduwa tana kallon mamar cikin rashin sa,a "mama kashe take gabaki daya ma" Xunbur mama tai tatashi tana nufar waje biyota fiyah tayi cikin tashin hankali. "Mama ina zaki dare yayi kiyi hkr insha allah baba yana lafiya." Kamar zata fashe da kuka tace"safiyyah zan je ga dalha idan yanada number wani daga cikin wajen aikinsa ya kira mana yaji lafiya,hankalina ya kasa kwamciya wlh" Tare suka fita suka bubbuga shagon da yake kwana don har ya kwanta. Bayan yabude ya fito cikin bacci-bacci yace"mama,safiyyah lafiya?" Fiyah idonan har yacika da kwallah tace"yaya dalha babane baidawo gida ba har yanxu inkana da wata number ta wani daga cikin abokan aikinsa don Allah kabani nakira muji ko lafiya" Dan danan damuwa ta wanxu kan fuskarsa yace"wlh mama,safiyyah banda wata number amman aiga mashin dina nan bari inhau inje inji ko lafiya hakanan ai baba baya kai goma balle har shadaya." Saurin rikeshi mamar tayi tace"aa dalha bazan barka kafita wannan unguwar ba cikin wannan daren,muyi hkr har xuwa sadda Allah zai dawo dashi,inkuma bai dawo ba da asuba saika fita kaje kajiyo mana lafiya" Ahaka suka dawo cikin gida karatun da fiya bata karasa ba kenan,wannan daren haka suka ganshi babu wanda ya rintsa cikin su. Asubar farko kau dalha ya fita yatai can wajen aikin su baban,ya tadda ogan wajen kurin ya zo wajen ma yake kokarin budewa. "Yallabai barka da safiya" Inji dalha. Juyowa yayi yana ansa gaisuwar da cewa"saurayi kana tambayane" "Eh yallabai malam kabir ladan nake tambaya jiya bai kwana gidaba shine nazo inji ko lafiya naga kuma wajen babu kowa" Ajiyar xuciya yaja yana zama saman wani benci yadafe kanshi cike da damuwa yace"zauna saurayi abun bai zaiyuwu daga tsaye ba" Jikin dalha yayi bala,in sanyi ya sauko daga kan mashin dinsa yana zama kusa da shi jikinsa har rawa yake saboda tashin hankali. "Kanaji ko,wlh jiya wani bala,i ne yasamu wajen nan yan dabane suka suka biyo Alh muazzam canji lokacin daidai tashin mu nida malam kabir don daman mukadai ake bari saimun gama tattara kaya sannan mu samu mutai. Bansan abunda ya faru ba amman na shiga kai kayan katako cikin shago,najiyo wani uban burki antaka bakin titin nan da kake gani,kabir ladan ne kurin wajen sadda zan fito ban ganshi ba,amman ga mota nan an ajiye akunne bama daidai akai parking din ba,daga can kuma ya nuna mashi wajen wani kango yacigaba motocine sunkai uku aka ajiye na fito ina naman malam kabir,don ban kai ga sallamar sa ba na nemai sama ko kasa ban ganiba.haka naringa zagaye area wajen babu shi babu alamarsa,dawowa nai naxauna ina tunani har na hakura zan tai na rufe wajen na hau mashin dina naga motar asibiti ta wuce ambulance kenan.........hankalina yayi kanta natada babur din nabi bayanta...........tafiya mukai mai nesa kafin muka iso wani waje,binsu nai har inda nafara ganin jini hankalina yayi mummunan tashi,muka cigaba da bin jinin har muka kawo kan inda abun ya faru,malam kabir ne kwance baya numfashi,ga Alh muazzam ya tusasa yana kuka harbine a bindiga ga kafarsa shikuma Alh muazzam yankane akai mashi ga kirjinsa sai goshinsa daya fashe yana fitar da jini,dan danan aka kwashesu akai ciki dasu. Har asibitin na bisu na tabbatar saida naga ya farfado likitoci sunyi masa aiki ancire bulet din sannan na tafi gida,yanzu haka so nake nanrage ayyuka naje na dubashi asibitin. "Nagode sosai amman ya sunan asibitin don inje insamar da iyalansa suganosho hankalinsa ya kwanta." Gaya mashi sunan yayi sannan ya hau mashin din sa yabar wajen,yana mamakin meya kai baba da shiga huddar da batashi ba,har hakan ya haifar da tsautsayi akanshi. Koda yaje gida kasa masu bayani yayi yace sushirya zasuje asibiti,tunda yafadi haka yesmin da fiyah suke kuka mama kau karfin haline yasaka bata xube kasa ba,don rudewa da firgici. "Kai dalha me zamuyo asibiti,waye ba lafiya in wani abunne yake faruwa daure ka gaya mana ba komi duk abu da ya samu bawa da sanin ubanhiji sai munemi sassauci daga garesa" Tafada cikin karyewar murya kwalarta na ka boyuw sunlalowa. "Malam dinne ya mutu kokuma wani abunne ya samai" Tausayin su yaji ya kama shi dole ya zauna yana lallashin su fiyah, tare da yi masu bayanin da ogansu baban yayi mashi. Kukan su ya karu fiyah tatashi ta rarumo abaya tana yin waje duk suka fito aka rufe gidan suka wuce bakin hanya suka tari taxi,mama da fiyah suka shiga taxi dalha ya goya yesmin ga bayan mashin dinsa,sannan suka nufo asibitin kowa da abunda yake nazari daga abunda sukaji bakin dalha. Suduka tunanin fiyah yasha banban da nasu don mama tana tunanin Alh muazam ne yasaka aimashi haka itada yesmin tunaninsu guda,dalha kuma yana ayyana taimako baban yazo yi wannan abun yafatu. Fiyah
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101