Chapter 16
Chapter 16
malik Gaskiya abokinka yaga rayuwa,ko ince yana cikin gani meyasa haka ta faru waye da alhakin wanan,wlh zan iya rantsewa bazai aikata haka ba.ayadda naji halayensa naji araina akwai wata ak'asa don Allah ka karasa man na yafe test din anmun makeup." Dariya yayi yace"rufan asiri kije kiyi test dinki wlh,kodai malamin saurayinkine da har zaiyarda yayi maki wani make-up." Murmushi tayi had'ad'd'e tace"aa yayan qawata ne kawai muna mutunci." Mik'ewa yayi yana kiran wani dake wajen yace ya hade abubuwan yayi takeaway dinsa,ya je ya nad'o naman dubu uku mai zafi. "Kitashi Allah bazan bari ki rasa test din kiba,muje ga mota na can saina saukeki." Ana kawo mashi ya jawo jakarta ya saka kallonsa tayi tace"yah malik duk nid'aya don Allah kabarshi za,amun fad'a agida fah." Hanya ya bata yace"no karki bari amaki fad'a in kinje school kici keda qawar fadan Alfah." Dariya sukai suna dosar inda motar sa take. *inhar banga comment daya wa ba bazan kara typing ba har sai sabuwar shekara.* Mrs bb ce Mom muhseen. [9/17, 3:36 PM] Fauziya Madaki: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSER* *(ALFAH)* WRITING BY. MRS BB MOM MUHSEEN. WATTPAD NAME HUMAIRA7531. *DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB AND ALFAH FANS* INA TAYA DUK KANIN MASOYANA MAZA DA MATA MURNAN BARKA DA SALLAH,FATAN ANYI SALLA LAFIYA UBANGIJI ALLAH YAYI MANA TSAWON RAI DA LFIYAR GANIN SHEKARA MAI ZUWA MOM MUHSEEN TANA MAKU FATAN ALKAIRI. 🅿️.........13 MALIK har cikin makarantar ya sauke ta tana masa godiya tare da cewa. "Yah malik sai yaushe kenan" Shafa kansa yayi yana murmushi yace"i think sai kin samu time,don naga satar hanya kike." Dariya tayi tace"wlh yah malik kamar kasani,amman insha Allah gobe zan kokarta infito don hankalina bazai kwanta ba har saina naji karashen wannan labarin,wlh yah malik abokinka yayi matukar ban tausayi,anya zan iya bacci kuwa?wlh labarin yasa na sakejin tausayin sa na kara jin kwarin guiwar taimakonsa." Jinjina kai yayi yace"karki damu kiwuce karki bata lokaci good luck Allah ya sa ki cinye Duka." Tana dariya sukai sallama ta wuce ciki bin bayanta yayi da kallo yana ayyana wani abu aransa,murmushi yayi mai tsananin kyau yace "wannan takun ma zai bada kala,zai taimakemu sofiyyah." Tashin motar yayi yabar cikin makarantar,gida ya wuce don duba Alfah. Motar Daddy ya gani alamar yazo parking yayi ya fito ya doshi cikin falon. Alfah na durk'ushe gaban Daddy shikuma Daddy yana ta faman yi mashi fad'a kamar zai ari baki,waje ya samu ya zauna yana kallonsu gaida shi yayi yace"rik'e gaisuwarka Abdoulmalik,yanzu gabanka Abdoul-Nasser yake shan win amman bakai kokarin sanar dani ba,giya fah giyar ma d most high one wadda zata iya kashe sa cikin k'an k'anen lokaci." Cikin biyayya da taushin murya malik yace"Daddy wlh Allah yasani nayi iyakar yina,nayi nayi da Abdoul akan shan giyar nan amman kamar tunzura shi nake,nasha kwashe duk na cikin frig din gidannan in zubar amman saiyayi kamar bazai barni da raina ba akan haka,sannan yaje ya kwaso wasu wlh Daddy ban san yadda xan da shi ba,gashinan baya jin nasiha baya yarda da hukuncin Allah,yaki hkr yaki fawwala ma Allah lamarinsa,saboda an masa k'azafin shan giya to bari yasha d'in dagaske.kuma har likita yayi mun bayanin cewa yaci sa,a babba da matsalar da take kokarin bashi ba babba bace,don duk mai ta ammali da wannan giyar baya kai labari." Jinjina kai Daddy yake cike da b'acin rai yana kallon alfah da ya sadda kai k'asa yana jin kamar ya kamasu yayi masu shegen duka. "To yayi kyau,ni zan kwashe su na zubar don Allah ka sake siyowa kaji ko,nace ka sake siyo wasu kaikuma muddin baka sanar dani ba halin da yake ciki kaida Allah.idan shi yaya ya wofintar dashi hakan bai nufin Abdoul baida sauran na gaba dashi,don haka duk abun da yake ciki ka sanar dani zan dauki mataki mummuna akanka." Ya tashi malik na tayashi suka kwashe duk wata giya dake cikin gidan suka je suka zubar............ko ajikinsa don ya sa aransa saidai giyar tayi ajalinsa,amman bazai daina ba. Bayan tafiyar Daddy malik ya dawo cikin falon amman abunda yabashi mamaki cup ne hannunsa da win din aciki yana kurb'a yana lumshe ido........... Sorororo yake kalon sa yana mamakin ina ya b'oye wannan har basu ganta ba,takowa yake cikin falon ya iso har gabansa ya durk'usa gabansa yana dafa guiyawunsa cike da karyewar xuciya yace"haba Abdoul,meyasa meyasa bazaka barmu muhuta ba,bazaka bar kanka ya huta ba.duk abunda muke munayi me don gyaran gobenka,ina tsoron mutuwa ta riskeka acikin wannan halin,Allah babu ruwansa da kazafin da aka maka,har ka yanke wannan hukuncin,don babu ina haka yazo acikin qurani balle hadisi.kayiwa rayuwarka gata ka dawo cikin hayyacinka,kadawo kakoma ga mahaliccinka duk wannan zafin rai bazai canza komi ba,kakoma ga Allah ka rokesa ya bayyana gaskiya.amman ba ka nemi kaucewa addininka ba." Saika rantse bada Alfah yake ba,shan win dinsa yake idonsa rufe yana girgiza k'afa,nan kuwa banda tafasa babu abunda zuciyarsa keyi,jiyake kamar ya cirota ya jefar,yana shanye win din yayi wata irin jifa da cup din yana bude idonsa akan malik. Saboda masifa da tsananin xafin rai idon nan yayi wani irin fitinennen ja,da sauri malik yaja baya biyosa yayi shikuma yana sake ja baya,har yayi nasarar shak'osa ya dagane sa dabango idon nan kamar zai fado yake mashi wani irin kallo,cikin kakkausar murya yace. "Bazan bar shan giyar ba,ehy nace bazan bari ba kabarin mu guda ne? to kashiga taitayinka ina d'aga maka k'afa baka gani ko,to kuskuren da zakai muyi hannun riga shine sanar da Daddy Wani abu akaina marar dadi." Ya watsar dashi nan kasa ya nufi hanyar fita falon,har ya kai k'ofa ya juyo yana kallonsa yace"inhar na sake ganin fuskarta agidannan saina kasheta ka sanar da ita wannan." Mekenan yaga fiyah kenan rannan,Oh Allah na gode maka da bai zo yayi mata wata illar ba,kai wannan bawa naka ya Allah ka kawo mashi sassauci. A makaranta fiyah sun had'u da feea,take mata maganar Alfah. "Wai fiyah kinko sake ganin guy d'in nan." Fiyah na duba question din da suka gama test akanshi yanzu ta ga ko ta ansa daidai,tace mata. "Ni kuwa ina zan ganshi rafeea,wannan dan zafin kai ai haduwa dashi hadarine." Dariya tayi tace"haka maganarki take amman kinsan tun daga wannan rana kullum yana cikin raina,tausayinsa nake sosai,inama zan iya taimakonsa inama ace ya dawo cikin natsuwarsa wlh ina jin kamar ina sonsa." Dagowa fiyah tayi tana kallonta cike da mamaki da al,ajabinta tace"kina cikin hayyacinki kau feea,kirasa wanda zaki kamu da sonsa sai wannan guy d'in,to wlh ki shiga hankalinki inba so kike kirasa jinki ko ganin ki ba.yo daki tunkari wannan damisan mutumen ba gara kin rungumi transformer ba ki huta kawai." Me feea zatai ba dariya ba,yitake har tana duk'awa saboda dariya. Itama fiyah dariyar tayi tace'wlh kau kedai kiraba kanki da wahala kurin,kii da d'an salim dinki." Haka suka ringa hirar suka wuce gida tare. Sanda ta je gida har yayansu jalal ya dawo ta iske uwar tsaraba,rabin buhun dankalin hausa dana turawa,ga kayan miya kamar banza,ga ayaba da yayo masu kayanta. Sai takalma na mata masu shegen kyau itda yesmin sai dinkunan baba kala uku hada babbar riga. Duk na sallah ne dake gaba towa don azumin baifi saura wata daya ba,mama kuwa atamfarta maikyau da tsada da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101