Chapter 55
Chapter 55
ta da kallo mamar tai tana jin babu dadi canzawarta,fita sukai da rafeea yau taxi zasu shiga bata fito da mota ba. "Baki tambayeni ba fiyah bacin nasan kin gane ina cikin farin ciki." Fiyah nata kokarin yin kira awaya tace"kinsan ai dole ne zan tambayeki don haka kibar saurin tambayata akwai abunda ke damuna nima,aman kiyi hkr bazan sanar dake ba" Murmushi feea tayi tana cewa"kobakice ba na gani afuskarki kuma daman ba tambayarki damuwarki zan ba,nasan idan kinyi niyya zaki gaya mun." Motace ta tsaya gabansu ni,imah ce driver ya fito da ita babu bata lokaci fiyah tace "muje ga sauki ya samu" Bata tambayeta ba itama ta bude bayan tashiga suka cigaba da tafiya,ni,ima na gaba tace"Anty ina kwana" Cikin murmushi tace mata"lafiya lau qanwata ya mami ta kwana" Murmushi tayi da alamar dai yau tana cikin farinciki tace"tana gida itama yau tana cikin farinciki tace ma na gaidaki sosai da sosai,kuma ta gode kwarai Allah yayiwa rayuwari Albarka" Wani sanyin dadi ya kama fiyah tace"Naji dadin adduar nan qanwara kice ngd sosai Allah ya kuma wanke mata bakin cikinta na tsawon shekaru,kuma kice mata cikin kwanan nan zataga suprise." Haka suka ringa fira tsakaninsu,feea dai tayi shiru tana mamakin meya hada fiyah da diyar gidan Alh amman datai nazarin maganganunsu ta gane cewar ta dalilin Alfah yasa,kuma babu mamaki a ni,imar zata kai wajensa.Allah sarki fiyah nada wata irin xuciya da mutane kalilan suke da ita,hakika tayi namijin kokari kuma Allah ne zai mata sakayya.ita tunda tasan Alfah ya mata nisa tasawa ranta salama,akwai wani d'an d'an kanwar mominta yake masifar sonta tana gwalesa,yanzu ta sassauto sunma daidaita kansu,tana ma fiyah fatan ace Alfah ya aureta don aurenta dazai shine kurin abun da zaimata ya saka mata..............sunxo bakin asibitin da aka kwantar da Alfah,fiyah taji wani ciwo cikin ranta inama taje ta ganshi,Amman babu wannan damar tayiwa kanta alkawarin dakatarwa hakanan,Amman tasan tsawon muamalarsu zuciyarta tayi wani mummunan raunin da bazata taba warkewa ba,illa tayita fatan Allah ya sassauta mata halin da take ciki. "Anty bazaki shigo ba ke" Girgiza kai tayi tana jin kwalla na tarar mata tace"aa ni,imah makaranta zanje exam gareni lokaci ya kusan wucewa kigaida shi da jiki kinjiko,sannan karkiyi kuka ki daga mashi hankali room 136 male ward zakije saiki ringa duba dakuna zaki ga daki mai no. 136 Sai mun yi waya byyyy." Suka sauka suka hau taxi suka wuce makaranta,kuka ta kamayi cikin mota feea bata ce mata komi ba,don ga dukkan alamu fiyah na cikin halin kaunar *ABDOULNASSER ALFAH* batai mamaki ba don daman hakan zata iya kasancewa,amman tasan ita kanta fiyar ba ganewa tai ba. Duk dokin sanar da ita dawowr mominta da take saita hkr har saita dawo natsuwarta. *don't share it pls I beg u* [9/17, 3:42 PM] Fauziya Madaki: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSER* *(ALFAH)* WRITING BY. MRS BB MOM MUHSEEN. WATTPAD NAME HUMAIRA7531. *DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB AND ALFAH FANS* 🅿️.........39 Exams tayi dadi sosai wajen fiyah,batai tunanin zata iya ansa duka question din ba,ganin yadda suke da yawa basu samu kansu ba sai bayan la,asar feea ta kira waya driver yazo yatai dasu. Acikin motar ne fiyah tace"baki gaya mun farin cikin dakike ciki ba feea" Murmushi tai tace"dazun naga baki cikin mood mai dadi shiyasa,daman ince maki momi ta dawo shekaran jiya,dady dakansa yaje ya dauko ta,kuma maganar aurensa babu ita don ta gudu yarinyar ance ba,asan ma inda take ba shikuma dady yace sadda akaganta ayi inkuma ba aganta ba shikenan,ya hkr.mafarin yaje yadawo da momi kenan,nhd fiyah duk nasan yana daga cikin komarinki Allah yabaki abunda kike nema,kema Allah yabiya maki bukatunki yaba baba lafiya." Murmushi fiyah tai tace"Alhamdulillah insha Allah dady bazai sake yunkurin wani auren ba,dagashi sai momi" Dariya sukai asibiti aka wuce da ita saida feea ta gano baban sannan tawuce gida. Tunda tashiga asibitin take ta duba no din dakin da fiyah tace mata,kafinma idonta yagano dakin tayi tozali da malik.rabonta dashi bazata iya tuna wa ba,kwalla suka silalo mata aguje ta isa inda yake ta rungumesa ta baya tafashe dakuka,baisan hawaba kurin yaji mutun juyowa yayi idonsa akanta,ajiyar xuciya yayi yana rikota sosai. "Ni'imah!A U OKY kinga daina kukan haka karki tara jama,a xomuje ai ba kuka zakiyi ba dariya da tsalle zakiyitayi yaugaki ga yaya Abdoul ga yaya malik dinki,oya zo muje daman nafito neman dr ya sake duba jikinsa,muje to" Riko hannunta yayi suka wuce cikin dakin. Jingine yake da filo yana shan tea marar zafi sosai ga plet agefensa yana cin dankali kamar baya so. Bude kofar da akai yasa idonsa ya sauka wajen,daman yaji ajikinsa zaro ido yayi kamar zai fixge drip din yazo ya rungumeta,malik yayi saurin dakatar dashi. Aguje ta karaso ta rungumeshi ta fashe da kuka. "Yaya.............."sai kuka Runtse ido yayi yanajin zafin kukan nata wata irin kewartace ta kamashi,tausayinsu ya lillibeshi dandanan yaji kwallah suna sauka shima ga fuskarsa,sunfi karfin minty talatin haka dr yazo ya samesu,yaja gefe yana kallonsu cike da tausayi. Dagota yayi yana kallon fuskarta yana share mata kwallar yace cikin muryar marasa lafiya. "Ina mamina,tasan zakizo nan waya gaya maki inanan karfa Abbi yaji kinzo kishiga matsala" Tana goge kwallarta tace"Dady ne ma yace intaho babu wanda zai san nazo,mami tace ingaidaka tana kewarka har bakinta bazai iya furtawa ba,yaya yaushe zaka dawo gida wlh muna bukatarka mami kullum bata lafiya saboda rashinka,gashi Abbi yadaina kulamu har mancewa muke dashi agidan,saidai dady ne yake hidima damu." Yana rike da hannu ta cike da damuwa yace"karki damu zanzo watarana kice ma mami nima ina kewarta sosai,tacigaba da hkr watarana sai labari kinjiko,yajikin Abbin yake kinje kinganoshi" "Eh naje jiya acan ma na hadu da wata fiyah,itace tace inshirya zata kawoni wajenka,tare muke dasu.............jekice tashigo ya zaki barsu waje. "Aa yaya tatafi tace jarabawa gareta,amman ince maka tana maka yajiki Allah yasawake" Dafe goshinsa yayi wani irin feelings din yarinyar yana taso mashi,ta ko ina tagama mashi komi arayuwa. "Yaya lafiya" Daker ya bude idonsa yace"kinsan inda take ne,imean gidansu" Daga kai tayi tace"eh yaya muna opposite dasu gidan malam kabir el-ladan fa take" Tsura mata ido yayi kamar zaiga wani abu akan fuskarta,malam kabir el-ladan safiyya diyarsa ce daman,innalillahi akwai damuwa ya tabbata yadda yasan tsohuwar gabar dake tsakanin sa da mahaifinsa bazata taba bari yasameta ba. "Ka riga ka ansheta matsayin abun kaunarka kuma wacce kazaba ta zamemaka matsayin matarka???"tambayar da xuciyarsa tayi masa kenan nan take. Shiru yayi ya kasa magana malik shima nazarin maganar ni,ima yake tabbas shima yasan abbi baya hudda da su,shi sai yanxu yake gane ma mahaifin fiyar. Dr yace"lokacin bacci yayi karka takura kanka a dogon tunani,munbada sallahun maganinka jiya dr hisham yatai malesia nasan zai samo,don wanan bai wuce yayi maka five days ba.kuma bama son ya katse maka akallah kasha na kwana talatin,kullin kasha muga Abunda Allah zaiyi." Cire mashi drip din yayi yana mashi Allurar bacci,idonsa akan ni,ima gani yake kamar daya rufe ido bazai sake ganin taba. Riko hannunta yayi yace"zakixo gobe ko?karki damu zan samu lafiya,kikoma gida banson wani abu ya sameki,ki anshi no din malik sai kikirashi inkinje wata kila asallameni zuwa gobe,sai kixo gidanmu ko" Daga kai tayi tana rike hannunsa ta sumbacesa tace"Allah ya sawake yaya bari natai" Malik ya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101