Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 55

Chapter 55

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,303 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ta da kallo mamar tai tana jin babu dadi canzawarta,fita sukai da rafeea yau taxi zasu shiga bata fito da mota ba. "Baki tambayeni ba fiyah bacin nasan kin gane ina cikin farin ciki." Fiyah nata kokarin yin kira awaya tace"kinsan ai dole ne zan tambayeki don haka kibar saurin tambayata akwai abunda ke damuna nima,aman kiyi hkr bazan sanar dake ba" Murmushi feea tayi tana cewa"kobakice ba na gani afuskarki kuma daman ba tambayarki damuwarki zan ba,nasan idan kinyi niyya zaki gaya mun." Motace ta tsaya gabansu ni,imah ce driver ya fito da ita babu bata lokaci fiyah tace "muje ga sauki ya samu" Bata tambayeta ba itama ta bude bayan tashiga suka cigaba da tafiya,ni,ima na gaba tace"Anty ina kwana" Cikin murmushi tace mata"lafiya lau qanwata ya mami ta kwana" Murmushi tayi da alamar dai yau tana cikin farinciki tace"tana gida itama yau tana cikin farinciki tace ma na gaidaki sosai da sosai,kuma ta gode kwarai Allah yayiwa rayuwari Albarka" Wani sanyin dadi ya kama fiyah tace"Naji dadin adduar nan qanwara kice ngd sosai Allah ya kuma wanke mata bakin cikinta na tsawon shekaru,kuma kice mata cikin kwanan nan zataga suprise." Haka suka ringa fira tsakaninsu,feea dai tayi shiru tana mamakin meya hada fiyah da diyar gidan Alh amman datai nazarin maganganunsu ta gane cewar ta dalilin Alfah yasa,kuma babu mamaki a ni,imar zata kai wajensa.Allah sarki fiyah nada wata irin xuciya da mutane kalilan suke da ita,hakika tayi namijin kokari kuma Allah ne zai mata sakayya.ita tunda tasan Alfah ya mata nisa tasawa ranta salama,akwai wani d'an d'an kanwar mominta yake masifar sonta tana gwalesa,yanzu ta sassauto sunma daidaita kansu,tana ma fiyah fatan ace Alfah ya aureta don aurenta dazai shine kurin abun da zaimata ya saka mata..............sunxo bakin asibitin da aka kwantar da Alfah,fiyah taji wani ciwo cikin ranta inama taje ta ganshi,Amman babu wannan damar tayiwa kanta alkawarin dakatarwa hakanan,Amman tasan tsawon muamalarsu zuciyarta tayi wani mummunan raunin da bazata taba warkewa ba,illa tayita fatan Allah ya sassauta mata halin da take ciki. "Anty bazaki shigo ba ke" Girgiza kai tayi tana jin kwalla na tarar mata tace"aa ni,imah makaranta zanje exam gareni lokaci ya kusan wucewa kigaida shi da jiki kinjiko,sannan karkiyi kuka ki daga mashi hankali room 136 male ward zakije saiki ringa duba dakuna zaki ga daki mai no. 136 Sai mun yi waya byyyy." Suka sauka suka hau taxi suka wuce makaranta,kuka ta kamayi cikin mota feea bata ce mata komi ba,don ga dukkan alamu fiyah na cikin halin kaunar *ABDOULNASSER ALFAH* batai mamaki ba don daman hakan zata iya kasancewa,amman tasan ita kanta fiyar ba ganewa tai ba. Duk dokin sanar da ita dawowr mominta da take saita hkr har saita dawo natsuwarta. *don't share it pls I beg u* [9/17, 3:42 PM] Fauziya Madaki: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSER* *(ALFAH)* WRITING BY. MRS BB MOM MUHSEEN. WATTPAD NAME HUMAIRA7531. *DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB AND ALFAH FANS* 🅿️.........39 Exams tayi dadi sosai wajen fiyah,batai tunanin zata iya ansa duka question din ba,ganin yadda suke da yawa basu samu kansu ba sai bayan la,asar feea ta kira waya driver yazo yatai dasu. Acikin motar ne fiyah tace"baki gaya mun farin cikin dakike ciki ba feea" Murmushi tai tace"dazun naga baki cikin mood mai dadi shiyasa,daman ince maki momi ta dawo shekaran jiya,dady dakansa yaje ya dauko ta,kuma maganar aurensa babu ita don ta gudu yarinyar ance ba,asan ma inda take ba shikuma dady yace sadda akaganta ayi inkuma ba aganta ba shikenan,ya hkr.mafarin yaje yadawo da momi kenan,nhd fiyah duk nasan yana daga cikin komarinki Allah yabaki abunda kike nema,kema Allah yabiya maki bukatunki yaba baba lafiya." Murmushi fiyah tai tace"Alhamdulillah insha Allah dady bazai sake yunkurin wani auren ba,dagashi sai momi" Dariya sukai asibiti aka wuce da ita saida feea ta gano baban sannan tawuce gida. Tunda tashiga asibitin take ta duba no din dakin da fiyah tace mata,kafinma idonta yagano dakin tayi tozali da malik.rabonta dashi bazata iya tuna wa ba,kwalla suka silalo mata aguje ta isa inda yake ta rungumesa ta baya tafashe dakuka,baisan hawaba kurin yaji mutun juyowa yayi idonsa akanta,ajiyar xuciya yayi yana rikota sosai. "Ni'imah!A U OKY kinga daina kukan haka karki tara jama,a xomuje ai ba kuka zakiyi ba dariya da tsalle zakiyitayi yaugaki ga yaya Abdoul ga yaya malik dinki,oya zo muje daman nafito neman dr ya sake duba jikinsa,muje to" Riko hannunta yayi suka wuce cikin dakin. Jingine yake da filo yana shan tea marar zafi sosai ga plet agefensa yana cin dankali kamar baya so. Bude kofar da akai yasa idonsa ya sauka wajen,daman yaji ajikinsa zaro ido yayi kamar zai fixge drip din yazo ya rungumeta,malik yayi saurin dakatar dashi. Aguje ta karaso ta rungumeshi ta fashe da kuka. "Yaya.............."sai kuka Runtse ido yayi yanajin zafin kukan nata wata irin kewartace ta kamashi,tausayinsu ya lillibeshi dandanan yaji kwallah suna sauka shima ga fuskarsa,sunfi karfin minty talatin haka dr yazo ya samesu,yaja gefe yana kallonsu cike da tausayi. Dagota yayi yana kallon fuskarta yana share mata kwallar yace cikin muryar marasa lafiya. "Ina mamina,tasan zakizo nan waya gaya maki inanan karfa Abbi yaji kinzo kishiga matsala" Tana goge kwallarta tace"Dady ne ma yace intaho babu wanda zai san nazo,mami tace ingaidaka tana kewarka har bakinta bazai iya furtawa ba,yaya yaushe zaka dawo gida wlh muna bukatarka mami kullum bata lafiya saboda rashinka,gashi Abbi yadaina kulamu har mancewa muke dashi agidan,saidai dady ne yake hidima damu." Yana rike da hannu ta cike da damuwa yace"karki damu zanzo watarana kice ma mami nima ina kewarta sosai,tacigaba da hkr watarana sai labari kinjiko,yajikin Abbin yake kinje kinganoshi" "Eh naje jiya acan ma na hadu da wata fiyah,itace tace inshirya zata kawoni wajenka,tare muke dasu.............jekice tashigo ya zaki barsu waje. "Aa yaya tatafi tace jarabawa gareta,amman ince maka tana maka yajiki Allah yasawake" Dafe goshinsa yayi wani irin feelings din yarinyar yana taso mashi,ta ko ina tagama mashi komi arayuwa. "Yaya lafiya" Daker ya bude idonsa yace"kinsan inda take ne,imean gidansu" Daga kai tayi tace"eh yaya muna opposite dasu gidan malam kabir el-ladan fa take" Tsura mata ido yayi kamar zaiga wani abu akan fuskarta,malam kabir el-ladan safiyya diyarsa ce daman,innalillahi akwai damuwa ya tabbata yadda yasan tsohuwar gabar dake tsakanin sa da mahaifinsa bazata taba bari yasameta ba. "Ka riga ka ansheta matsayin abun kaunarka kuma wacce kazaba ta zamemaka matsayin matarka???"tambayar da xuciyarsa tayi masa kenan nan take. Shiru yayi ya kasa magana malik shima nazarin maganar ni,ima yake tabbas shima yasan abbi baya hudda da su,shi sai yanxu yake gane ma mahaifin fiyar. Dr yace"lokacin bacci yayi karka takura kanka a dogon tunani,munbada sallahun maganinka jiya dr hisham yatai malesia nasan zai samo,don wanan bai wuce yayi maka five days ba.kuma bama son ya katse maka akallah kasha na kwana talatin,kullin kasha muga Abunda Allah zaiyi." Cire mashi drip din yayi yana mashi Allurar bacci,idonsa akan ni,ima gani yake kamar daya rufe ido bazai sake ganin taba. Riko hannunta yayi yace"zakixo gobe ko?karki damu zan samu lafiya,kikoma gida banson wani abu ya sameki,ki anshi no din malik sai kikirashi inkinje wata kila asallameni zuwa gobe,sai kixo gidanmu ko" Daga kai tayi tana rike hannunsa ta sumbacesa tace"Allah ya sawake yaya bari natai" Malik ya

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});