Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 20

Chapter 20

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,282 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

yi sofiyyah,kawai kuyita mashi addua itace kawai mafita,munyi iyakar yinmu amman mutanem nan sun runtse idonsu akan baza su bari ma muganshi ba,Allah shine maganinsu shine kawai." Mama na gama jin haka ta wuce taje tayo alwallarta tashige d'aki shima tashin yayi yafita. Kuka yesmin da fiyah sukeyi sosai daker sukai sallar magruba,rokon Allah kau sunyisa kamar me akan Allah ya kawo masu mafita ya kuma saka ma baba. Ranar abincin kirki ma babu wanda ya iya sawa ga baki,anayin isha,i kowa ya wuce masaukinsa don ko hirat da suka saba yi bayan sallar isha,in yau babu natsuwar yinta.damuwar da suke ciki tafi karfin hirar. Bayan yesmin ta kwanta saida fiyah taga tayi bacci sannan tafiddo wayarta ta kunna,ta shiga kiran malik. Suna tare da Alfah yana mashi bayanin kudaden sa zasu fitar don yin tafiyar dasuke so,sai shan mur yake daker yake maida mashi ansa,don tundazun abun da yafaru bai wuce mashi ba,jiyake inama yasamu damar karya shegiya. Daker suka gama tattaunawar sun tsayar da lokacin tafiyar wayar malik tashiga ringing,kallon Alfah yayi yana murmushi yace"mutuniyarka ce kozaku gaisa." Wani jakin kallo ya watsa mashi ya tashi yabar falon,dariya malik yayi yana daukar wayar. "Yadai matsoraciya." Cikin halin kunci tace"yah malik inaciki tsananin tashin hankali." Cikin mamaki da rudewa yace"kina lafiya dai ko badai yaji maki mummunan ciwo ba." Cikin zubar kwallah tace"Aa ba Abdoul bane mahaifinsa ne ya kama mana babanmu,yana can caji office sun ma hana ganinsa balle aji ta bakinsa,suma kuma basuce komi ba sunce kuma bayanxu zasu sakeshi ba." Kuka take k'asa k'asa. Cikin tausayawa yace"yi hkr fiyah,daina kukan insha Allah baba zaidawo yanzu kinga dare ne kiyi bacci zuwa safe saimuyi magana.ai kinada class gobe ko." Cikin shashshekar kuka tace eh ina dashi 9:00am to 12:00am imfact sai hudu zan dawo gida kila." Yace"don't worry kisa ma xuciyarki natsuwa kiyi bacci insha Allah xantai makamaki zuwa gobe." Godiya tayi mashi yace"Abdoul dai baiji maki rauni ba ko?" Tace"targade ne amman zan gasa dasafe inshafa magani." "OK sorry Allah ya sawake muhadu goben ki kwantar ma da mama hankali babu abunda zai faru." Haka dai yayita lallashinta da tausarta sukai sallama tayo Alwallah tayi nafila sannan tayi karatun qur ani ta kwanta. Washe gari kowa sukuku daker ma yesmin tasha koko taci waina gira sannan jalal ya bata kudin taxi tatafi jarabawar ta.don ma xuwa jibi suke gamawa. Ta riga fiyah tafiya ita saida ta gama ayyukanta tanayi tana tausar mama,tana kara bata hkr da kalamai masu sanyaya zuciya har ta samu tayi kalaci don cewatai azumi tatashi dasi d'ore. Jalal da fiyah suka tilasta mata ta ajiyesa don zata sha wahala tunda batai sahur ba,ga damuwa kuma har saida fiyah ta ragewa mama ayyukan gidan,har jajjagen kayan miya tai mata ta gyara shinkafa ta dora mata ruwan zafin wanka. Albarka kawai mama ke samata don sofiyyah badai kokari ba,tana da tausayi fiyeda sauran yarata. Don saida ta makara ma don wajen tara da kusan rabi ta samu tafiya bayan ta gasa k'afarta ta shafa magani. Fuskarta yau babu walwala sosai daka kalleta kasan bata da walwala sosai,makaranta ta wuce taci sa,ar malamin baida zafi yabarta tashiga,rabida kwatar lectures din ta yau basu shigeta ba yadda ya ka mata,haka dai ta samu ta silale duk da yadda feea ke son yin magana da ita,amman ta sace ta barta don abunda ke gabanta yafi tattauna wa da feea muhimmanci. Bata ma sanar da malik cewa tana hanya ba,kawai dosar gidan tayi saida tazo bakin kofar shiga abunda ya faru jiya itada Alfah ya fad'o mata arai. Turus tayi kirjinta yana dukan tara tara,wayarta ta fiddo ta maka mashi kira tace"Allah yasa wannan tafasheshshen abokin naka baya nan,don wlh inhar yana nan baxan shigoba ya idasa karya mun k'afa." Yar dariya malik yayi yace"oh matsoraciyar kanwata to baya nan kina iya shigowa." "Aa yaya malik karkamun wayau kamar jiya." Dariyar yake yace"Allah I'm serious he is not here" Ajiyar zuciya tayi ta shiga da bismilah don bata shirya wata hayaniya dashi yanxu ba,har saita ga baba ya fito. Yana cikin main falon su akan computer yana aiki daga shi sai singlet. Kunya taji ta kamata ta d'an juya baya,murmushi yayi ya jawo rigarsa dake gefensa ya saka yace"to sarkin kunya kina iya juyowa yanzu." Idonta ak'asa ta idasa shiga falon tana yabawa da tsarinsa zama tayi kan oneseater tana kallon wani chanis films da sukeyi wata tasha. Gaisawa sukai yana jajanta mata akan abunda ya faru dasu,taji dadi sosai malik yana da kirki,kuma ya iya mu,amala da mutun kallonsa tayi tace"ina wannann mugun yake." Shafa sumarsa yayi yana idasa aikinsa kanan ya rufe computer yace"yau Alfah yaje supervision na store d'insa da company,yau ya tashi da rigima daker idan bai kori wasu ba,don ni banma san fitar sa ba saida nakira drivern sa yace suna tare." Tab'e baki tayi kurin tana wasa da yatsunta kamar ba ita ta tambayesaba.........mukullin mota ya dauko yace "zomuje akwai inda zamu yanzu,kash ko ruwa ban baki ba sorry don Allah." Tashi tayi tana smile dinta kamar yadda ta saba tace"no karka damu yaya malik banga tashan ruwa ba tukun,muje bana jin k'ishi bare yunwa." Fita sukai yaja motar suka bar gidan,wata unguwa suka nufa maidan nisa,sanan suka tsaya bakin wani get aka bude masu suka shiga,gida ya had'u sosai do fiyah irin wadannan gidajen ba bak'inta bane don duk irinsune a unguwarsu. Bai bata halin tambayar inasuka zo ba.ta bisa abaya suka shiga kofar da xata sada su da cikin gidan,duk jami ai sun kewaye gidan da alama dai babban mutunne ubangidansu. Babban falone mai kujeru royel set biyu sai k'amshi yake,zama sukai yana danna wayarsa zuwacan yakafa ga kunne yace"eh Daddy munzo muna nan main falo." Daga haka ya kashe wayar kallonta yayi cikin tsokana yace"wajen yankar kai na kawoki mai cire kan yana zuwa yanzu." Duk da ta san wasa yake hakan bai hanata jin faduwar gaba ba,yak'e tayi tace"uhm yaya malik kenan,zatonka zanyi tunanin wani abu ko?ai yardar dana maka ba raguwa bace na yarda dakai 100% don haka duk inda zaka ce muje bazan maka jayayyaba,don nasan bazaka iya salwantar da ran kanwarka ba." Kalamanta sunyi masifar faranta mashi har ya kasa cewa komi ya dora mata idanunsa yana kallonta,murmushi akan fuskarsa. Kawarda kai tayi gefe kafin suji alamun shigowa,wani kukune d'auke da tire na wasu kuloli masu kyau da plax da cups. Ajiyewa yayi yabar falon yama gaidasu still har lokacin idonsa akan fiyah,wadda takejin duk ta takure saboda kallonda malik yake mata,fitowar Daddy ya ceceta daga kallon da malik yake jefanta dashi. Duk saukowa sukai daga kan kujerar suna gaidashi.......cikin fara,a da karramawa yake ansa masu yace sukoma su zauna amman suka k'iya dole ya k'yalesu. "Abdoulmalik bakuci komi ba naga." Kansa akasa yace "Daddy nidai i'm oky wlh." "To ai ka yi serving din ta ita ko." Fiyah cikin ladabi tace"Aa daddy wlh nima na k'oshi kayi hkr." "Shikenan tunda kun k'icin abincin gidana,malik naji duk abunda ka sanar dani jiya abunda yasa nace kazo mun da yarinyar don naji ta bakinta." Malik yace"fiyah ki sanar dashi abunda ya faru yadda zai fahimta." Cikin natsuwa ta fada masa iyakar abunda tasani wanda taji bakin mama,katseta yayi cikin mamaki yace"kardai kice mun mahaifinki malam kabir

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});