Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 39

Chapter 39

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,275 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

abu aranki game dashi" "Ohhhh niban saka komi cikin raina ba Abdoul na zakiyya ne nace maki ko" (😄😄fiyah ta zare aradu) Haka wannan daren ya kasance wa safiyyah har asuba,kuma kokadan ta nemi baccin tarasa tashi tayi taje tayi sallah sannan ta dora ma maijegon sanwar ruwan wanka,sannan ta koma daki tana karatun kur ani. Sanda gari zaifara haske tashiga ta hada break miyar kwaice da kabeji tayi musu da ruwan tea mai na,a na,a da lemon grass sai citta da kanun fari kamshi kurin yake,ta soya dankalin turawa sannan ta hauda ferfesun naman kaza bata so aikin ya kaita ga takwas ba,shaf shaf ta yi nata break din tayi shara da mopping bata tsaya wanke wanke ba ta dauki akwatinta tayi get. Karo sukai da muhseen ya shigo gidan, Tsaki taja cikin ranta tana mitar "ko ubanme yazo yi tunda uwar safiya" "Ah fiyah ina zuwa haka tun da farar safiya." Yake tayi mashi tana gaidashi. "Gida zanje na kai kayana anjima kadan zan dawo." "Oky to muje na kaiki daman break nazo nayi wajenki tunda kuma baki nan shikenan" Don dole take murmushin tace"ah wlh kashiga kayi ainariga na gama hadawa,bazama zanyi ba gidan" Ansar akwatin yayi yana yin gaba yace"no muje kawai ai ganinki ma yasaka naji yunwar ta tafi idan na kaiki saina dawo nayi." Ya zatayi da shi da alama wanan naci garai kamar magan disu. Shiga tayi gaban motar tana yaba tsarinta da kyanta,gashi sai kamshi take. Zagayowa yayi yashiga yatada suka dauki hanya. Duk sai tajita atakure shikau jiyake yau kamar amashi bushara gashi ga safiyyan sa,cikin janta da fira yace"ko sannu da zuwa bakiyi mun ba safiyyah." Saitaji bata kyauta ba cikin kunya tace"sorry pls andawo lafiya" Murmushi yayi yace"no karki damu aike bakya laifi safiyyah,nayi hkrin kuma nadawo lafiya fatan kuma na sameki lafiya." Ya ta iya dashi dole ta sake tana ansa mashi hirar tashi."komi lafiya yaya muhseen" Cikin kwarewa yake jan motar yana sarrafa sikiyarin yace"Amman sanda na tafi Anty bata baki sakona ba" Wayar hannunta ta kalla tace"wannan?" Girgiza kai yayi yace"no ba wannan ba,i mean bata yi maki wata magana akaina ba" Sai yanzu ta gane inda ya nufa, Girgiza kai tayi tace"Aa gaskiya kilan ta manta" "Kokuma kece kika manta ba,don munyi magana da ita sosai har idan muyi waya wani lokaci tace ashe muna waya dake ban gaya mata ba,to kasancewar nasan kingaya mata ne don kitsira daga masifarta yasa nima nake kokarin kareki,sai kawai nace mata eh munayi sosai ma.Aman tambayata anan safiyya itace meyasa kika mata karya." Shiru tayi tana jin kunyarsa na kamata,hakika muhseen yana da kirki kuma duk wasu qualities da ake bukata ga namiji ya nadasu kawai dai kowa da nashi ra,ayin itadai bai mata ba batajin zatayi soyayya dashi balle aure. "Kayi hkr" Abunda tace dashi kenan. "Ba maganar nayi hr bane kinsan me?nifa In my life duk abunda zanyi direct nake yinsa,kuma duk abunda yake raina ina fadarsa don idan nafadan ina samun saukin xuciya,don haka babu boye boye tsakanina dake inasonki kema kuma kinsan ina sonki kawai dai kilan ban maki ba shiyasa kiketa yimun hanya hanya,kin ban wuya.watana uku abuja ina godalan inganki muhadu in sabunta soyayyata amman kikakiya safiyya,aman saboda ina kaunarki bazan iya fushi dake ba gani na sake dawowa,don haka bazan koma ba sai kin gaya mun abunda kike nufi dani." Gabanta yafadi gaskiya bazata iya kallon cikin idonsa tace masa bata sonsa ba,kuma bazata kwari kantaba tace tana sonsa bayan kuma ba haka abun yake ba. Na bani yazanyi da shi. "Karki damu kanki u have enough of time da zakiyi tunani don zan jima ban koma ba,amman kafin kigama nazarin nawa zan iya zuwa wajen baba don neman izinin zuwa zance?" Wayyo tashin hankali ba,asaka mashi rana,muddin maganar taje ga baba shikenan bata da miji saishi,don inbazata manta ba haka akai da uncle yahya da Anty. YAZANYI NI SAFIYYAH? (TO FOYAH NA NEMAN MAFITA ALFAH FANS KU WARWARE MATA YADDA ZATAI,KO YAN ZAUREN MRS BB) MRS BB CE MOM MUHSEEN. [9/17, 3:38 PM] Fauziya Madaki: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSER* *(ALFAH)* WRITING BY. MRS BB MOM MUHSEEN. WATTPAD NAME HUMAIRA7531. *DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB AND ALFAH FANS* 🅿️.........28 Tsare ta yayi da ido bayan da sukai parking kofar gidansu,sadda kai tayi tace"kaban lokaci zan yi tunani" Relax yayi jikin kujerar yana shafa kansa yace"yanzu neman izinin zancen ma fiyah saikice sai kinyi tunani,gaskiya zaki wahalar da zuciyata,kenan bazan zo zance ba bacin ko awaya bama gaisawa." "Aa yaya muhseen indan wannan zamu ringa waya amman kabar maganar zuwa wajen baba yanzu saina shirya don Allah." Ajiyar heart yayi yac"shikenan na hkr amman gaskiya idan naji bazan iya jurewa ba saidai kiji sallama nazo zance." Ansar no din ta yayi yana zuwa ya bude mata sannan yafiddo mata kayanta daga cikin but,godiya tayi masa ta wuce cikin gidan kadan yahana ta banki baba dake tahowa zai fita. "Ah baba yi hkr ina kwana" "Safiyya kece tunda uwar safiya haka,yo ya akai naganki da kaya kamar wacce tayo yaji." Sadda kai tayi tana jin kwallah na zubo mata,ansar mata akwatin yayi yana cewa sushiga gida tau. Shiga sukai mama dake shara cikin gidan kaji ta fito tana ajiye tsintsiyar,biyosu tayi cikin gidan yesmin na ganinta ta rogo ta rungumeta. "Nayi kewark Addata,ya su Antyn ya kuma babyn." Daker take ansawa yesmin ansoshinta baba yace"yanzu mukai karo zaure naganta da akwati natambaya kuma ta fara kuka,shine nace tashigo ciki tayi mana bayani." Mama ta iso tana zama gefen fiyah dake matsar kwalla,ita masifar da Anty tayi mata ce tasaka tayo yajin,don baiyyuwa tana mata bauta amman bata iya mata uziri. "Safiyya dake nake magana nace meya faru keda jamilar?" Kuka ta saka tana gaya mata abunda yafaru jiya"mama Anty kullum bata canzawa da yaya muhseen bai saurin tareta ba duka na zatai fa,yanzu mama ban wuce duka wajen anty ba ai nai zaton zata tambayeni dalilin dadewata." Baba ya shafa kanta yana lallashi yace"jamila bata kyauta ba kuma nima gara dakika dawo bazan yarda ana cutar mun da uwata ba,yesmin kaimun akwatinta daki ko sunan ba kizuwa." Mama tace"Ba ayin haka babansu,komi jamila tayi wa safiyya ai kanwarta ce kuma yanzu saita baro gidan sunan tataho nan sabida Allah,idan banda yaya balaraba da yaranta wagareni dazan tura ya kama mata inaba dan safiyyar,komi tayi maki aibakin baro ta kitaho nan ba,kayi hkr anjima inta huta saita koma,kuma zanyiwa jamilar fada ita daman matsalarta kenan shegiyar xuciya da rashin uziri,haka dai yahaya yake fama nasani." Kuka na saka ina murje murjen kafafu nace"nifa mama kiyi hkr,sokike inje tayita hantarata wlh Anty ta kara lalacewa da masifa duk hkr na yau ta kureni alqur an." Murmushi baba yayi shida yesmin mama tace"haba Ansafiyyan mama kiyi hkr yanzu ma zan kirata nayi mata fada,aibakin barota ba kiyi hkr anagama hidimar ni daso nai ma kizauna har tagama wanka." Kukana nake ina murzar ido yesmin sai dariya take mun. Kafinma mama ta dauko wayar kira yashigo tace"kingani ma itace take kira." "Wlh mama idan bata bani hkr ba bazan koma ba" Bata kulata ba ta dauki wayar baba yace"zata baki uwata kwantar da hankalinki." "Yanzu jamila sakayyar da zakiyi mun kenan?na turo diyata don ta ragemaki wahala shine kika

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});