Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 32

Chapter 32

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,266 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

sit din gaban ya silale ya kwantar da bayansa da kansa,idonsa rufe ruf. Jin malik yatashi motar yasa shi magana batare daya iya bude idonsa ba . "Kasan nan zaka barta meyasa kazo da ita?" Daman haka yake jira ya bude motar yafota ya iso wajenta magana zai mata ta juya ta barsa wajen. Gudu gudu sauri sauri haka take hadawa don isa inda zata samu abun hawa...........jitai kamar tana bisa iska zuwa sadda zata dawo cikin hayyacinta saidai tajita anyi jifa da ita cikin mota.........sannan suka tafi. Wai ashe Alfah ne yabiyita yadaukota kamar yar tsana yasata motar,don yayi imanin kafin ma ta isa inda zata samu taxi sai kafarta ta kusan cirewa don ciwo........shiyasa kawai yaje yadaukota don idan suka tsaya janjani zata bata masu lokaci,shiyasa kawai yayi mata haka. Kuka ta fashe dashi don tama rasa me zatayi tama hana zuciyarta yin wani tunani ta kuntace ta waje guda,babu mai magana amotar don su ukune yaran sa sun wuce company da kayan d suka duko. Sutin kukan kurin kakeji mai cike da bakin ciki kafin ta gaza jure k'un cinta take cewa. "Allah ya isana ban yafe ba mug.........kasa idasa mugun tayi tana shashshekar kuka Alfah dake gaba kwance idonsa lumshe jinta kurin yake murmushi yayi mai sauti har saida malik ya juyo yana kallonsa, "Malam Kalli gaban ka karka zubar damu." Dole malik ya kauda kai don shi yau Alfahn duk ya zamema sa kamar wani sabon mutun. "Haka kawai ka samun wana kazamin bakin naka mai shan giya,gashinan ji nake kamar zanyi amai wlh kaida Allah ban yafe ba." Sika sakejinta tana fadar haka. Bai motsa ba yace"naga dai alamar giyar nan sonta kike kina sha,awar d'an d'anawa karki damu zan baki kisha." Bata sake magana ba har suka isa gidan su Malik,don babu abunda taki jinin ji daga garesa irin yace zai bata giya,tasan kadan daga cikin aikinsa ne tsaf zai danneta ya dura mata ita.wai Allah da tashiga ukunta kau. Fitowa tayi tana sharben majina ta wuce titi bata saurari kowa ba ta tari taxi ta wucw gida.........koda taje anty tace ta huta tayi masu girkin dare cewa tai bata da lfiya,dole sai Mai aikinsu ce tayi masu. Mrs bbce Mom muhseen 09034722970. [9/17, 3:37 PM] Fauziya Madaki: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSER* *(ALFAH)* WRITING BY. MRS BB MOM MUHSEEN. WATTPAD NAME HUMAIRA7531. *DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB AND ALFAH FANS* 🅿️.......... Wannan dare safiyya bata iya runtsawa ba ta tayi kiskuren runtse idonta sata ganshi yana lashe mata kumatu,dandanan zata ji tsikar jikinta tatashi tayi zunbur ta tashi zaune ta rabka tagumi..........ga baccin yana cinta amman bata son ganinsa cikin baccita,meyasa ya tsaya man garai ni fiyah?meyasa wulakancin sa bai tsaya man sosai irin yadda salonsa ya tsaya mata ba.hatta kayan jikinta yau ta gagara musanya su saboda kamshinsa dake jikinsu,dandanan Allah yasa mata kaunar turaren.daga ta mirgina can saita mirgina can har dai mulmulowa tayi kasa bata ma san tayi ba saida tajita tim kasa.........dafe kai tayi tana mamakin kanta wai meke damuna ne yau,akan wancan dan rainin hamatar na ke duk wannan,aa ba zai yuwuba shidin banza da wofi wlh saina yi baccina yau insha Allah. Koma wa tayi kan gadon tana sake wata adduar tana gama wa ta tofe ko ina ta shafe jikinta ta kwanta. Duk yadda take dambe da zuciyarta abun yaci tura,amman haka ta daure ta runtse idonta gam da tsiya sai baccin ya dauketa. Ganin babu sarki sai Allah yasa tatashi tayo Alwallah tazo ta fara sallah,saida tayi raka,a shidda sannan tadauko qur,anin ta tafara jero karatu cikin tsantsar tajwidi.........saida ta shafe akalla awa daya da rabi sanan ta ajiye ta koma ta kwanta.......dan danan baccin yazo ya sureta. 💞💞💞💞💞💞💞💞💞 Tunda suka shigo ya wuce ya watsa ruwa sanan yyi sallar magrub a cikin dakinsa yunwa yakeji da gajiya baison yin magana kwata kwata yanzu,soyake ya kwanta yana bukatar tunani. Yasan malik inzai shigo zai taho masu da abinci tunda kukun nasu baya nan. Kasa ya kwanta yana filo da hannayensa idonsa rufe kafafunsa ya dora su bisa wani dan table,yayi crossing dinsu yana girgiza guda. _haka kawai kasa mun wannan qazamin bakin naka mai shan giya gashinan ji nake kamar zanyi amai wlh.kaida Allah ban yafe ba_ Murmushi ya subuce masa mai shegen kyau,har fararen hakoransa kyawawa suka bayyana. Kafin Annurinsa ya fara b'acewa saboda kalamanta na farko. _ur highly welcome drinker guy_ Runtse idonsa yayi yana jin zafin kalamin cikin ransa,tabbas yasan ankirasa da wadanda sukafi wadanna ada bama da ba har yau akwai masu yi mashi wannan kallo,amman zuwa sadda ya rikice ya daina jin zafi da dacin kalaman shine lokacin da ya kulla damarar shanta.daga lokacin baya jin haushi baya jin radadi don ance masa mashayi.........ammman yanzu da yaji din rad'in kansa ya barta bari na har abada,sai yaji kalaman basu dace dashi ba,Allah shike ganin zukatan bayin sa amman yasan badan wannan yarinyar yabar giya ba,saidai yasan cewa kalamanta suntaka rawar gani wajen taimaka barinsa da ita,don tunda yaje Australia daya shata ma sai yayi amai kuma sai yayi masassara,lokacin ya dan gana da asibiti don radin kansa wanda shi knsa yayi mamakin ganinsa gaban likita wai ya kawo kansa,bacin kullum hanyar da zata lahanta rayuwar yake nema. Amman baisan meyasa yanzu yakejin yashirya yin rayuwa mai kyau koda shokadaine cikin duniya,yaji haushin kansa lokacin da dr yohana yake gaya masa cewar wine din takai limit din da bata kara iya daukar hunhunsa,saboda ta mashi rauni a wajen wanda muddin ya sake yasha ta ko yasha lemo mai gas yana iya rasa ransa,haka zalika ya hana shi shan abu mai zafi sosai da kuma mai sanyi sosai,don zasuyi mashi lahani........sannan abun daya sake bashi mamaki da haushin kansa wai arne da baisan kansa ba wanda bai yarda da Allah da manzon sa ba yake mashi nasihar zaman duniya,da kuma abunda zaiyyi maikyau da marar kyau. Ranar yayi kukan da tunda yabar gidan iyayensa baiyyishi ba,yayi nadama da dana sani yafi akirga,saida ya kwana biyu baifita ma aikin daya kawoshi ba. Mafarin ya fara ansar magani daga shi dr yohanan yace masa duk bayan wata uku yazo aduba shi don zai iya yuwiwa amai aiki,idan kuma yana warkewa to basai anyi aikin ba......duk sanda ya tuna wannan lamarin saiyaji kansa yana sarawa,hakika yayi sake yabari shaidan da sherin zuciya sunyi galaba akansa.meyasa abunda ake masa kallo dashi bayyi yunkurin kiyaye kanshi dashi ba,yanzu kenan da Allah bai sa ya bar sauran shaye shayen dayayi ba Allah kadai yasan abunda zai faru da rayuwarsa.da mezaice ma mahaliccinsa baida bakin da zai iya kare kansa. Hawaye suka silalo mashi yaji wata kaunar malik ta cika mashi zuciya,tabbas malik abokine na musanman duk wanda yasamu aboki amini irinsa yadace yayi dacen da har tutiya ma inyayi babu laifi. Don yasan irin wuyar dayasha kafin ya rabashi da sauran kayan mayen.sannan binciken dayasa akai mashi ya nuna mashi cewar shine ya kawo wannan yarinyar cikin rayuwarsa,don ta taimakeshi yadawo dashi daidai..........meyakai wannan arayuwa inda wanine fita sabgarsa zaiyi yaje koma me zayyi yayi aiba dan uwansa bane ko wami nashi.........wannan dalilin yasa yaji zuciyarsa tayi sanyi tayi cool dinda baisan rabonsa dajin haka ba,yaji natsuwarsa na dawowa yaji happenes dinsa cikin kaso dari kashi arba,in yana dawo wa

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});