Chapter 34
Chapter 34
kidawo" A haka suka rabu tafice don inba haka tayi mata ba balbalin masofarta ma sai ya hana fitar. Mrs bbce. Mom muhseen [9/17, 3:37 PM] Fauziya Madaki: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSER* *(ALFAH)* WRITING BY. MRS BB MOM MUHSEEN. WATTPAD NAME HUMAIRA7531. *DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB AND ALFAH FANS* 🅿️.........25 Tana fitowa sukai cibis da yaya Jalal shida wani abokinsa sunxo ganin baby,wani duka kirjinta yayi don wlh yana iya hanata fitan ma gabaki daya. Kallonta yake Sama da kasa cike tuhuma,ita Kau banda yak'e babu abunda take,ta gaida abokin nashi ya na tambayarta baby tana ansa mashi cikin kulawa. "Yaya ashe zakazo nai zaton yar taka ma bazaka zo ganinta ba." "Ina zaki haka da yamma?" Bazata banbanta karyar da tayi ma Anty da wadda zatayi ma shi ba ana iya samun Matsala,."yaya na gaya ma Anty zanje makaranta kasan exams tataho shine Zan anso handout in fara karatu." "Salan kikai dare,naga take takenki kafafunki sunfara sanin gari kin iya yawo." "Bazan Kai dareba yaya Amman don Allah kakara man kudin taxi wlh basu isata wannan." Kafinma yafiddo abokin yaciro Dari biyar yabata,godiya tayi mashi sosai sannan suka shige. Wucewa tayi itama tana murmushi itadai ai hankalinta ya kwanta tunda tayi nasarar ficewa,text din data turo mata babujima ta shiga dubawa. _ina nan magic land,inkinzo ki kirani saina zo na shigo dake._ Dandanan ta tari taxi ta gaya ma shi inda zai Kai ta,jingina tayi da kujerar da take tana tunanin hikimar daxatayi Mata anfani da ita wajen shawokanta harta gaya mata abunda take bukata,Amman muddin taji gaskiyace zatafada bawai karyaba dole zata kunna recording,don shine abumafi sauki damutun zaiji yayarda dakai,Yakuma yi amanna da cewar wancen bashida laifin komi sharrine na mahassada. Duk da cewar abunda take shirin fadan tanajin faduwar gaba kuma tana tsoron faruwar wani abu,Amman dolene tayi hakan don shine hanya mafi sauki data dace tatunkari zakiyyar. Amman harga Allah tana tsoron wani abu guda dayake mata yawo cikin kai,wata xuciyarce takegaya Mata "inaruwanki safiyyah,kedai ba burinki gaskiya tafito ba to inaruwanki da duk abunda zaifaru tsakaninsu." Ajiyar xuciya tayi tana jin wani zuka cikin kirjinta,duk da haka dai batason hakan ta kasance. Har bakin Kofar shiga wajen ya sauketa ta salameshi ta fito, Kiranta tayi awaya saigata ta fito,wannan ne karon farko da tahadu da ita.....gabanta taji yafadi ganin zakiyyar kyakkyawar gaske duguwa Mai dirarren jiki,gaskiya dole Alfah take rikicewa akanta,aman tana tantamar idan gaskIya tafito tabbas wannan tsuhuwar soyayyar zata iya tashi. Wani lugude taji kirjinta yayi Mata saitaji haka kurin tana tausayin kanta,murmushi shimfide akan fuskar zakiya Wanda ya sake bayyana ainahin ruwan kyanta,Amman kuma azahiri safiyya tacewa zakiyya kauban wuri Amman saboda wani abudake ranta yasa ta kasa tantance itada zakiyyar waye yafi wani. "Assalamu alaikum." Zakiya tafada tana mikawa fiyah hannu. Cikin rashin kwarin jiki ta na mata yake ta mika mata nata hannun tace"Wa,alaiki salaam,zakiyya muazzam ko?" Cikin Fara,a tace"haka yake sunan,muje ciki to nima har kinsanar dani naki." Jerawa sukai suna tafiya hakanan zakiyya taji fiyah ta kwanta mata arai,Ku ma ta yardarma ranta bazata cucetaba. "Ai tun ranar dana kiraki nafada maki sunana kindai manta ne" Cewar fiyah dake kusada ita tana kallon wajen gwanin burgewa. "Ohhh anyi haka,Amman wlh na manta kasancewar abubuwa sunmun yawa." Fiyah tayi murmushi tace"haba aiba komi kasancewar ki amarya aianama amare uziri hidima ce tayi masu yawa." Dandanan fuskar zakiyya ta canza,yanayinta ya canza sosai harta kasa cewa fiyah komi akai. Tun anan fiyah taharbo jirgin,zarginta ya tabbata cewar zakiya bata son auren Alh kwangila,to meyasa zata auresa.? Wajene ta tanadar masu Mai tsananin kyau da burgewa,kuma wajen is save zasuyi maganarsu cikin sirri babu Wanda zaijisu ko yasa musu ido. Zama fiyah tayi tana ajiye jikkarta agefe,ta tsurama zakiyya ido tana kallo tana sake karantarta tsaf. Zakiyya zaman tayi itama Amman gabaki daya fuskarta ta canza babu wannan walwalar da tazo da ita afarko. Hannu tasa tana dafeda fuskarta natsayin wani lokaci kafin ta iya dagowa tana cewa cikin sanyin murya. "Bari akawo maki a bun ta'bawa ko." Cikin kulawa tace"Aa zakiyya,kibarshi har nakoma gida ban bukaci wani abunba,yanzu dai ga pos dinki duba kiga komi dakika San yana ciki yana nan yadda yake." Murmushin karfin hali tayi tana cewa"bama sai na duba ba nayarda dake gani nafarko dake,nasan bazaki cuceni ba." Murmushi fiyah tayi tace"karkiyi saurin yarda dani taya kikasan bazan cutar dake bah." Ajiyar xuciya zakiyya taja tace"nasan ki ai,sunanki ne kurin ban rikeba Amman yadda nasan gidan dakika fito ya tabbatar mun bazaki cuceni ba,duk da ganin danayi maki baiwuce uku ba." Cikin mamaki fiyah "inakika sanni." Dariya tayi tace"nikinga banzanyi mamaki ba da kika sanni,dafarko nayi lokacin dakika kirani,Amman ganina dake yasa mamakin yafita,don unguwa daya ba wasa bace gidanku yana opposite danamu kohar yanzun kina mamaki." Jinjina Kai tayi tace "nabar mamakin yanzu ai" Shiru sukai fiyah tana jinjina halin kirki da rashin wulakanta mutane irin na zakiyya,Sam batayi Kama da yangidan masu kudin dasuke wulakanta Wanda sukasan kasansu Yakeba. "Kince zamuyi magana dake,tundaga ranar hankalina baisake kwanciyaba har yanxu,sonake naji abunda kikeson muyi magana akai." Sadda Kai fiyah tayi tace"inhar kinyi amanna dani cewar bazan cucekiba, zakiyya kiyimun alkawarin cewar duk abunda nake da bukata zaki fadamun gaskiya." Kallonta take tana nazarinta kafin ta iyacewa"mezai hana,ai koda kingujeman gidanku bazai gujemun ba,balle nasan ba zaki yi abunda zasakani cikin damuwa bah." "Karkiyi saurin cawa haka zakiyya,don kuwa abunda nazo dashi zaijefaki cikin damuwar da wata kila kinyi bikin binneta cikin ranki,abunda nazo dashi zaifama maki wani ciwo da kikatabaji cikin ranki,Amman Ina maitabbatar maki yadda na fama makishi haka insha Allah zanwarkar maki dashi ki bani yardarki da kuma amanarki." Cikin dokantuwa dason jin abunda fiyah tazo dashi zakiyya tace"kin sakamun kwadayin jin wannan lamarin,koma miye nayi maki alkawarin baki yardata dakuma amanata,nabarmaki wuka da naman,don nayi imanin kinfini sanin yadda zakiyi dani." Gyara zama fiya tayi tace" I know kinsan *ABDOULNASSER MUAZZAM CANJI*" wata irin razana da gigita ce tashiga zakiyya,yayinda dandanan kwalwarta tashiga yomata tariyar duk abubuwan dasuka wuce abaya,tsawon shekara shidda kenan. Dandanan idonta yawanke fuskarta DA ruwan hawaye,zuba kawai sukeyi babu kakkautawa........har lokacin idonta yana kan fiyah hannunta tasaka tana rufe bakinta,Wanda kukan dake tahowa zai iyajawo hankalin mutanen wajen Kansu. Fiyah batayi yukurin dakatar da ita ba don so take ta yi kukan tagama sannan sucigaba da maganar. Kwantar da kanta tayi bisa table din wajen tana kuka sosai maitaba zuciya,magana take cikin kukan ta na cewa"Ina kikasansa?Ina kikasan indayake rayuwa don Allah,hakika yau kin tayarmun da mikin da kullum nake dannesa cikin raina,Abdoulnasser shine duk wani farincikina shine duk wani burina,Zan iyace maki magabaki daya shine jigon rayuwata............Amman rana guda lokaci guda komi yawargaje komi yalalace,yabarni nabarsa alokacin damuke tsakada tsananin dokin juna da bukatar juna. Abdoul shine haskena dake haskaka duniyata,shine Wanda idan inacikin duhu yake haskakamun gabana.Amman nawayi gari babushi banajin muryarsa,ba ganinsa wani abunma dazai tuna mun dashi Ana kokarin ganin annesantani dashi........kiyiwa Allah da manzonsa kigayaman wajen Da ABDOUL yake.inason sa hargobe bazan iya daina sonsa ba.koda naman jikina za,ayanka zuciyata bazata dakata daga tunaninsa ba,shiyasa sukayanke mun hukincin da ko inso kobana so dole zanbar Abdoul...........kuka yaci karfinta. gabaki daya jikin fiyah yayi Mata wani mugun sanyi,kwalla sukacika idonta natausayi. Zakiyya Ashe ba tamanta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101