Chapter 50
Chapter 50
kuma tana tunanin wani abun nadaban,tana tuno hirarsu da zakiyya ta farko da suka hadu. _"Kiban kwana biyu zan nemeki akwai wani abu danake son ganowa suna kitsawa Abbi wata makarkashiya ne"_ Tabbas aikinsune nafarko kila suna son kasheshi su kwashi dukiya,na biyu wannan yaron mamman da suka biyo zakiyya umma tana son ya maye gurbin Alfah koma ince ya mayen,suna ganin asirinsu nangab da tonuwa yasa suka yanke wannan hukuncin,tunda har suka iya farautar ran zakiyya ta silar haka to kau babu makawa shima farautar ran nashi aka biyo yi don su smu cimmabumtr su sugudu.lallai akwai marasa imani cikin mutane dayawa,har ki iya saka wa akashe yarki sannan kisa abi mijinki shima akashe saboda abun duniya,wannan rayuwa abun tsoroce yayinda rai ya zama ba abakin komai bamutame sun maida kudi sune rayiwar duniya,akansu babu abunda bazasu iya ba. Har suka isa asibitin tana wannan nazarin. Dakin da aka kwantar da baban suka tambaya,dalha yake masu jagora har xuwa dakin. Togewa mama tai tana hawaye bata san mezata tarar ba,tanajin tsoron ganin abunda zuciyarta bazata iya dauka ba.......riko hannunta fiyah tayi cikin lallashi tace"mama kiyi hkr ki natsu babu abunda yasamu baba mai girma insha Allah kisaka natsuwa cikin ranki kar kitada mashi hankali" Da haka ta kwantar mata da hankali suka tura kofar suka shiga, Kwance yake yana bacci har lokacin ga kafarsa nan andaure da bandage,alamun itace keda matsalar. Kallonsa suke cikeda tausayawa yesmin har lokacin kuman take likitanne yashigo. "Sannunku kunxo ganin mai jikiko" Dalha ne ya iya bashi ansa yace "eh dr,yajikin nashi" File dinsa ya shiga dubawa yana cewa"he is very lucky,bulet din bai shigeshi sosai ba don kadan ya hana bai bita cikin kashin kafarsa ba,wanda da hakan ta faru sai anyi mashi aiki sosai.amman anyi sa,a hakan bata faruba ku godema Allah don cikin sati guda zai iya warkewa insha Allah.inhar yana shan magunguna yadda ya kamata,gasunan ma har ansiya tun dazun.yanzu da ruwan nan ya kare zai iya tashia amman bazamu baku saama yanzu ba akallai zai kwana biyu anan din." Ajiyar xuciya mama ta sauke tanajin sanyi cikin ramta Allah abun godiya dayasa babu wata babbar matsala. "Dr waye yasiyo magungunan?" Inji safiyyah "Alh ne ya bayar da kudin komi harna tsawon lokacin da za sallamai,shima mun bashi gad don shi ciwon da sauki bai kai ma wannan bawan Allah ba" Mamaki ya kama su sudukan mama har bakinta saida ta hangame saboda tsananin mamaki,Alh muazzam din zai iya yiwa baba wannan abun,to dalili dame? Mehakan ke nufi mamadai ta shiga shakku tace"likita anya kasan mekace kuwa" Daroya yayi yace "hajiya kenan to menene,koba shiba kowaye zai iya yin fiye da hakan akan mutumen dayayi saving rayuwarsa,yaji dadine kuma na tabbata ba iyakar abunda zai yi ba kenan bari dai har ya warke,don bacin mijinki hajoya bana tunanin iyanzu Alh muazzam ba,ai janazar sa ba" Kallon karin bayani suke mashi amman sai ya nufi hanyar fita kafin ya juyo yace"kuna iya zuwa kudawo anjima sai kudawo yafarka zuwa karde biyu amman kina iya barin wannan saurayin" Kowa da kalar tunaninsa akan wannaa sabon al,amarin. "Dalha ka zauna da baban ku zamuje gida in aka gama hada kalacin sai akawo maka." "Aa mama ki zauna ke sautai tare da su safiyyah idan suka hada sai akwo maki nakin,idan nakwo maki saikitai ni inzauna" "Toshikenan kuje din" Tafiya sukai gidan akabar mama wajensa. 💞💞💞💞💞💞💞💞💞 "Bafa ka isa kace zaka ajiye mun wannan yarinyar ba,inbacin inda sauran xuciyar imani wallahi bazan kaita asibiti ba saidai ta mace acan bisa titin,sannan taci darajar wannan yarinyar wallahi da ko sake bi ta kanta bazan ba,don haka inhar kana son muzauna lafiya ka dauketa daga cikin gidanna,inba haka ba bollah azim nizan fita kuma bazan sake dawowa ba,au kinci nasara wancen lokacin bai isheki ba akaina har sai kin sake biyoni cikin duniyar dana sake kin chaza mun kwalwa ko,to baki isaba tunda naga take-taken ki bakison kiganni ina rayuwa adoron kasa,to karya kike kinci karya kin kwana da yunwa wallahi." Tunda yafata balbalin masifarsa tana durkushe kasa tana kuka bilhakki da gaskiya..........malik kallonsa yake cikin takaici amman har yau baiga laifinsa ba akan abunda yake ma zakiyyar,laifinsa anan dayake hakikancewa lallai lalai bazata zauna agidan ba. "Yanzu ina kake tunanin zan kaita,shin kana ringa lissafi mana Alfah,wannan xuciyar karinga sassautama kanka ita kanada ciwo tare dakai kasan da wannan,don haka mubar tada jijiyar wuya akan wannan,zakiyya tana nan gidan bazataje ko ina ba" Kukanta ya tsananta tana cikin bakin cikin Yadda Abdoul dinta ya koma,tsanarta tayi guri tatare cikin ransa taya zata iya fahimtar dashi cewar bata da saka hannu cikin lalacewar rayuwarsa. "Fine,nandai zata zauna dai ko shikenan" Hanyar barin falon yayi cikin zafin rai,dagaske tafiyar zai kuma yayi alkawarin bazai dawo ba...........kamar antsikareta tatashi aguje tabi bayansa tana shashshekar kuka,part dinsa ya nufa yabanka kofar cikin fushi,don da ace ba kofar kirki bace saita balle. Akwati ya jawo yana hada kayansa,ko likewa babu cusawa kurin yake idan ya cirosu daga hanger. Shigowa tai cikin dakin Kamar anjehota tana nishi,rike hannu sa tai muryarta na rawa tace"na rokeka yaya Abdoul karka tai,muddin kabar nan bazan iya yafewa kaina ba,bacin wancen mikin dana sawa xuciyarka bazan iya daukar wannan ba,yaya Abdoul na gwammace ni inbar maka gidan inhar hakan zai saka kaji salama cikin ranka,zantai zantafi inyaso kome suke so suyi da rayuwata suyi mun,na cancanta da hakan." Ta durkushe kasa gabansa tana rike da kafarsa guda sosai take kuka mai tsuma xuciya. Wani irin ciwo yakeji cikin ransa,bai zaton har akwai sauran feelings game da zakiyyar ba cikin xuciyarsa,wani tausayi-tausayi yakejin yana tao mashi,yanajin kukanta har cikin kokon ransa.mezaimata?mezaice mata?bazai iya hucewa da wuri haka ba xuciyarsa yaudararsa take akan hakan,amman zakiyya bata cancanci yafiya da wuri ba. Tuntse idonsa yayi yana jin wani radadi,kalamanta suna sake dawo mashi cikin kunne. _yaya Abdoul na gwammace inbar maka gidan,inhar hakan zai saka kaji salama cikin ranka,zantai zantafi komi zasuyiwa rayuwata suyi mun na cancanta da hakan_ Su waye?me zasuyi mata?metayi masu.tsoro ya kama shi akan hakan,karsu cutar da ita dandanan yaji bazai iyabarinta tabar gidan ba,shima kuma ya hkr da barin gidan zaijira har koma me suke kullawa malik da wannan yarinyar ya bayyana,kafin ya san mizanin da zai dora zakiyyar. Juyowa yayi yasaka hannu riko kafadunta yadago ta,biyosa tayi idonta yayi jaa saboda kuka hawaye share share,take kallonsa da mamaki ko kadan batai tunanin zai saurareta ba balle har ya iya tabata. Malik yana bakin kofa yana kallonsu,murmushi yayi yana jinjina kokarin fiyah,na sassauta zafin ransa da saukowa da wuri. Zaunar da ita yayi bakin gadonsa ya juya baya don baison kallon idonta,don zata raunana mashi xuciya har yayi abunda bai niyya ba. "Kina iya zaman nan din,har xuwa sadda komi zai lafah sannan karki daman da wani ban hkrinki,kirike abunki bana bukata." "Bazan zauna ba inhar kaima zaka bar gidan don bakaine zakabar gidan ba nice" "Babu inda zanje inkinga kina iya zaman ga fili nanda dakuna" Ficewa yai yabar malik tsaue yana binsu da kallo. Isowa yayi gabanta yana mika mata hanky yace"ki kyalesa zai sakko,inha Aah komi aksan uwa karshe." Girgza kai tayi tana tace"zasu kashe Abbi sutsara yadda zasu farmashi,ban sani ba ko harma sun aikata abunda suka shirya din,saboda
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101