Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 46

Chapter 46

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,283 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

tayi taga sunan malik,da dai kamar ta share amman sai xuciyarta takasa yin hakan. Ahankali ta dauki wayar tana sawa ga kunnenta. "Qanwata ban sanki da haka ba,yaushe kika b'aci da fushi ban sani ba" Turo baki tayi kamar yana gabanta ta haye kan gado tana jingina bayanta ga allon gadon cikin sassanyar murya tace"yaya haka ma zakace bacin,bacin abunda akaimun har zaka ce kar nayi fushi" "Ni bance karkiyi fushi ba,amman saiki yi mashi uziri abunda ya sakashi yin hakan kinsani meyasa bazaki mashi uxiri ba," Sake sunburo bakin tayi kamar zata yi kuka tace"yaya malik Amman basai yazo ya ban hkr inshiga ba amman fa gabansa na tsayar da taxi natafi baiyyi yunkurin dakatar dani baya kyaleni natafi" "Sorry qanwata zaibaki hkr Amman saiya samu sauki" Gabanta yafadi rasss "yaya malik baya da lafiya ne" Iska yafesar yana gyara kwanciyarsa yace"fadowa yayi daga kan gado ya suma xuciyarsa ce ta halba numfashinsa ya tsaya,amman ya samu sauki don gashi can likita ya saka mashi oxygen.xuwa safe zai farka cikin koshin lfiya insha Allah" Kwalla suka zubo mata cikin kermar murya kiris yarage ta fashe da kuka tace"yaya malik ka tabbatar yana lafiya,ya samu sauki sosai yaya malik nice na bata mashi rai ko?wlh yaya malik ni banson hakan zai bata ransa ba kuma wlh ni kai nakoira bashi ba,amman sai kurin naganshi yazo.......kasa cigaba tayi da magana don kukanta ya kusa fitowa" Jinjina kai yake yajiyo sautin kukanta tabbas safiyya ta kamu da abunda yake zargin cewar shima Abdoul din ya kamu,duba da yadda duk yabi ta rude ta tashi hankalinta. "Kuka kike fiyah,miye na kukan to?bakison wani abu yasamai ne" Shashshekarta ce ta fito fili takasa ansashi murmushi yayi yace"ki kwantar da hankalinki babu abun da zai sameshi,kiyi mashi Addua daya farka da safe zan kiraki sai kimasa ya jiki ko" Shiru tayi tana jin kamar tayi tsuntsuwa tazo ta ganshi,amma bata son Yaya malik ya fahimci kotana jin wani new feelings akan Abokin nashi. "Kinyi shiru qanwata" "Saida safe yaya malik zan kwanta" Murmushi yayi yanajin ina mace shine yayi dacen samun wannan tsadaddar yarinyar mai kunya da tarbiyya. "Shikenan qanwata Mma i promise u immediately daya tashi zan kiraki kizo ki ganshi,sannan zakiyya na asibiti ta samu sauki itama da safe ko zuwa yamma zata iya farkawa ai zaki xo ganinta ko saimuyi magana daganan" Daker ta iya ce mashi "oky,goodnight" Ta sauke wayar tana silalewa saman gadon tana jawo filo tana kwakwumeshi ga kirjinta. Plssss kuyi hkr gobe ba zaku samu posting ba saboda muna aikin suna sorry plsssss nasan ba zakuji dadi ba,amman inhar nasamu lokaci zanyi maku Pls don't share it i beg [9/17, 3:41 PM] Fauziya Madaki: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSER* *(ALFAH)* FOR SALE 300 VIA KISIYA KISHA KARATUNKI CIKIN NATSUWA. GA MAI BUKATA TA TUNTUBI WANNAN LAYIN 09034722979 WRITING BY. MRS BB MOM MUHSEEN. WATTPAD NAME HUMAIRA7531. *DEDUCATED TO ALFAH FANS GROUP* 🅿️.........33 "Anty bazan iya zama har kigama wanka ba,kinga exams ke gareni ina bukatar inje na natsu gida nayi karatuna,kiyi hkr nidai kibarni natai tunda kinga wlh yya muhseen baxai barni nasake ba inhar yasan ina nan gidan gara dai na tai can gida." "Shikenan,Bari na dauko maki naman ku kowa na mashi kullinsa don haka babu wata rigima,halinki nasani kan nama idan na sake na hadaki dana yesmin wlh kwararta xakiyi,har gara inkeda mamane wanan tana iya ma raba nata biyu takara maki ita ko baba,don naga dagaske kin anshe ma yesmin fadarta" Dariya fiyah tayi tana yiwa little fiyah rawa tace"uhm shedar da zakiyi mun kenan Anty?kuma ai dama can fadata ce tana zuwa naga alamar da niyar juyin mulki tazo saina zage don kar na rasa matsayina,amman duk da haka Anty Ai yesmin tafini fada aji wajen mama,da dai babane wannan nasan bai bari abunda zai bata raina,don ta nama ma saiya hkr da nashi yabani incinye" Tafada tana dariya antyn dake cikin daki tace"wlh karma kifara,kowa anbashi nashi kiji tsoron Allah kibarshi yaci,haba safiyya wlh nasan zaki aikata don Allah karkiyi haka" Tana dariyar tace"to inbaki so inyi nawa yafi na kowa yawa aradu" Fitowa tai da babar lea viva ta ajiye gabanta,ta fido wata bakar leda cike tab daker aka kulleta tace"wannan na kine kici kiyi kashi don ubanki,wanna kuma na mama gashinan nayi alama,wannan kuma na baba shima ga shedar shinan,inna balaraba tunjiya suka wuce da nasu banda su anan ciki,ga na yesmin ga na yaya jalal asaka mashi akitse tunda ya tafi randa ya dawo sai yaci" "Kai Anty,saikace dole nidai gaskiya ki kyale yaya kiban shi in cinye in yadawo sai inbashi hkr" "Uban hkr zaki bashi wallahi karnaji wannan labarin kinji dai na gaya maki,kodayake ma bari kigani." Ya daukeshi daga cikin sauran tace"nizan ajiye mashi dakaina" Suna cikin haka uncle ya shigo yace"safiyya badai tafya ba?" "Wlh uncle tafiya zanyi,inje na natsu infara karatu lokaci yana kure mana" "To gama bari nazo na saukeki,muhseen baya nan da nasaka ya kaiki." Aranta tace"nagode Allah" Sunyi sallama da Anty jamilar tana tayi mata godiya akan hidimar da tai mata,kamar zatai kwallah haka taji don dan zaman da sukai saitaji inama taita zama da qanwar tata,koba komi sunyi wasa da dariya kuma ta rage mata ayyuka,amman tasan baba bazai yarda ba kuma itama fiyar tafison kusada mama da baban. Suna tafiya yana janta da hira tana biyesa,har yazo kan maganar abokinsa. "Nikau safiyya ina kika san Alfah,ayadda na fahimta ranan ba bankeki yayi ba,karki boyemun inason in sanine saboda wani dalili" Saitaji bazata iya boyewa uncle din nata ba ta sadda kai ta fara bashi labarin haduwarsu da kuma dalilin shigarta rayuwarsa,har kawo abunda ya tsayar da ita bata dawo gida da wuri ba,harda cigaban da ya samu tadalilinta. Shiru yayi yana jinjina kai kafin yace"niyyarki mai kyauce safiyyah,amman kinsan hakan akwai hadari ga rayuwarki,wannan aikin namiji ne ya dace dashi ba ke mace ba,saboda yadda amana tayi karanci cikin rayuwar nan,kuma nima nasan da wannan labarin,shiyasa na tambayeki tabbas nima raina ba yadda Alfah zai aikata haka ba,duk da kowane lokaci mutun zai ita canza wa,amman da kamar wuya gaskiya.don haka ki kula ki kiyaye ya dace tun farko ki sanar da mama koyaya dai in wani abu yabiyo baya duk da ba fata ake ba,atleast tasan mekike ciki" "Uncle wlh bazata barni na taimakesa ba saboda abunda ya faru tsakaninsu da mahaifinsa,gabace maitsawo tunma ba aifemu ba muduka,abun ya faru shiyasa duk unguwar babu mai kulamu bamu banda yan tsirarunsu,shiyasa na boye abun babu wanda yasani cikin gidan mu don kar ahanani kuma Alhamdulillah komi yana zuwa da sauki nanda dan lokaci komi ya kammala,nima inhuta in samu natsuwa." Murmushi yayi baice komi ba don yayi imanin shigarta rsyuwar Alfah baya nufin ta fita,don ga dukan alamu ita dashi kowa yana jin wani abu game da dan uwansa,shiyasa bai bada karfi wajen ganin muhseen din sa ya sameta ba,yana da burin ta dawo da abokin nashi cikin hayyacinsa,kuma zaiso ace sunyi aure sauran halayyarsa ta idasa daidaita shi,shiyasa ma zaifara nema wa muhseen din Auren yesmin,don bazai so ace ya rasa daya daga cikinsu ba,don yarane da suka samu kyakkyawar tarbiya yadda ya kamata. Sauketa yayi suka shiga ya gaida mama lokacin baba bai dawo gida ba,yaba fiya dubu goma ladar

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});