Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 61

Chapter 61

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,293 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

shine yasa har Abdoul yaji yana sonta don ta na niyyar cetoshi,mema yasa tai saurin yarda fiyah tasan lokacin son kara saka Abdoul din cikin kwayar idonta duk ya rudeta yasa dandanan ta fayyacema fiyah komi,yazatai tagyara wannan barakar tana tsananin kishin Abdoul ko wata bata son taga ya kalla inhar sunan ta mace,to balle fiyah yarinyar da kallo guda zaka mata katabbatar da tsananin kyawunta,bata kwalliya afuska amman hakan bai hana ruwan kyanta bayyana ba.kodan wannan Dole Abdoul zai haukace akanta wai har tsawon yaushe haka tafaru.rushewa tai da kuka tana cewa"Allah ya isa fiyah,bazan yafe maki ba kin sace mun zuciyar Abdoul,to yakike son ninayi bacin na gaya maki bana iya rayuwa mai dadi muddin babu shi cikin rayuwata.........kamar ta haukace haka taita kuka abakin titin,mutane na kallonta kamar daga sama saiga malik yazo wucewa kamar ance yakalli gefen hanya idonsa akan zakiyya,zaro ido yayi yai saurin parking gefen hanya yafito. "Zakiya!kina lafiya kuwa?mekike anan kekadai kuma kika zauna akasa bakin hanya kina kuka kanki guda kuwa?" Kukan take tace"yaya malik kabarni nayi kukana don shine kurin abunda zan yi nasamu sauki,wallahi bansan safiyya munafuka bace sai yau,ta yaudareni bazan yafe mata ba tana shirin rabani da numfashina,yaya malik Andoul shine numfashina meyasa kuka sanyota cikin rayuwarku gashinan tayi dalilin rabani da rayuwata.........." Kallonta yake cike da mamaki shi gabaki daya baima fahimci abunda take fada ba,jan hanunta yayi tana biyosa tana cigaba da kukanta,ya bude motar ya sata yarufe surutunta take tana kuka,bai sake mata magana ba don bama zata natsu tayi mashi bayanin abunda yake tambayarta ba,saida yaje gida ya sauketa yaga Abdoul baya nan,wayarsa ya lalubo sai lokacin yaga missed call dinsa har guda biyar,fitowa yayi yakirasa lokacin shi yana can har lokacin ba afito da fiyah ba daga dakin gaggawa. Duk ya yamutse ya tashi hankalinsa daker ya iya daukar kiran. "Malik ina kashiga na shiga halin taimako na kira baka dauka ba,ganinan *care life hospital* na kawo sofiyya." Cike da tashin hankali malik yace"safiyya kuma?meyafaru badai wata matsala ko ganinan xuwa innalillahi wainna ilaihir raju,un." Yakashe yashiga motar bai tsaya xuwa company ba duk da bakin dake jiransa kurin sai yanufi asibitin............duk ya rude wannan wace irin masiface daga wannan sai wannan,mekuma yafaru da ita Allah karka saka mummunan abu ya sameta. Yanata wannan surutun har yaje asibitin,daker ya gano Abdoul din. yadda yaganshi saida hankalinsa ya ninka tashi,duk ya rikice yariko hannun sa yace"Alfah meke faruwa?ina safiyyar me yasameta ka kwantar da hankalin ka babu abunda zai faru da ita." Malik bai sake rudewa ba saida yaga Alfah yana fitar da kwalla muryarsa na rawa yace"malik,inajin tsoro inajin tsoron faruwar wani abu akanta,ta dalilina da zakiyya ta saka rayuwarta cikin hadari,dazun na kirata............ya zayyane mashi duk abunda yafaru yana hawaye,yace "tsorona kar ace sun mata injection,saboda hada yukurin fyade suka so yi mata Allah bai basu dama,yanzu haka suna can station sonake sainaga farkawarta kozan je" Lallashinsa yake yana goge mashi kwalla lallai Alfah ya fara dawowa Alfah dinsa na ainahi,baya ma abu kuka duk tsananinsa tun bayan da bunda yafaru agidansu,amman yanxu akan mace duk ya gigice yafita daga natsuwarsa. Yanxu ne yafahimci maganar zakiyya,kallon Alfah yayi yace"can na gamu da zakiyya bakin titi tana kuka sai surutu take wai safiyya ta yaudareta Allah ya isa bata yafe ba,meyafaru ne " Dogon tsaki yaja yace"kyale wannan mahaukaciyar,wai da safiyya zatai kishi harta ikirarin inhar ita zata kaita asibiti wlh bata zuwa,Allah ya kyauta saidai ta mutu.ni bantaba ganin butulun mutun ba irinta,ubanwa yajefa safiyyar cikin wanna matsalar inba itaba,ba ta dalilin ceto zakiyyar suka ganta ba har haka ta kasance,to wallahi inbatai wasa ba zan bata mamaki,mahaukaciyar baza da batasan abun arxikiba"mtsss yaja tsaki malik yayi ajiyar xuciya yace "dole zanje na sanar agidansu,nasan suna can suna jajanta har magruba bata dawo ba,ko zaka zo muje" Girgiza kai yayi yana shafa kanshi har lokacin baya cikin natsuwarsa shi xuciyarsa ma ciwo take"bazan je maitama ba ahalin yanxu,kaidai kaje din" "Shikenan kakula da kanka,zan biya na sallami baki acan company" Cikin yanayi marar dadi yace"kayi waya kace asalallamesu sun dawo gobe baka da lokacin zuwa company yanzu malik," Murmushi yayi yace"ok sir"yadda yayi harda sarawa yasa murmushi ya kubcewa Abdoul badan yashirya ba,fice wa yayi yatai wajen mota yana tunanin shiga unguwar,shekara shidda rabon dayaje ko kan titin unguwar balle bakin get din estate din. Jan numfashi yayi ance ranar dole sai dole yaja motar yatai. 💞💞💞💞💞💞💞💞💞 Baba ne ya gama sallar magriba yace"nikau maman su kin kira uwata kinji inda ta tsaya hankalina ya kasa kwanciya tun dazu," Fitowa mama tai daga daki itama cikin yanayi marar dadi ta zauna gefen baba saman tabarma tace"wallahi babansu tun karfe shidda nake kiranta wayarta arufe,na kira jamila tace gaskiya bataje ba na kira balaraba tace ita rabonta da safiyha tun sunan jamila,shirun danai na dauka kafin kayi magana ta dawo,addua kurin nake tunda nashiga daki nai salla." Juyowa baban yayi yana kallonta cike da damuwa yace"haba maman su,meyasa tun dazun baki fada ba da ban tura dalha yaje can akaramtar yaji abunda yafaru ba." Sadda kai tai tace"kayi hkr babansu,na tura yesmin gidan su rafeea tunda tare suka tai data dawo tace mun ai rafeea can tabaro safiyyah basu gama ba wajen hudu da rabi,shine saina tura dalha nace yaje yagano mana ko lafiya,na boyene gudun tashin hankalinka." Shiru yayi yana tunani sai kuma yaji ta bashi tausayi,mace mai kulawa da gidanta da iyalinta.duk abunda tasan zai daga mashi hankali kokari take ta kiyaye wannan dinma don yafi karfinta bata da wata mafita. "Shikenan Allah yadawo da dalhan lafiya yasa kuma babu wata matsala,tunda bata kai har kamar yanxu inhar ba gidan jamila tabiya ba" Shiru sukai yesmin sarkin kuka har tafara xubda hawaye mamace ke lallashi ta itama jitake kamar tayi kukan,gabanta ke faduwa bana jin safiyya ba lafiya ba. Tunda ya shigo unguwar abubuwa dayawa suka ringa dawo mashi,unguwar ta canza sosai fiye da dacan,gine gine da abubuwan cigaba duk sun samu kasancewar unguwace ta yan siyasa da masu hannu da shuni,tafiya yake yana kallon gidajen daya bayan daya har idonsa yakai ga gidan da bazai taba mancewa dashi ba,gidan da ya canza mashi rayuwa ya fiddoshi daga cikin kangin talauci da kakanikaye.kwalla yaji ta fito mashi xuciyarsa ta karye abubuwan da suka faru ranar da ya dawi daga tafiya,ina ma ya bude idonsa yaga komi mafarki ne ba haka yake ba.amman ina wannan rayuwar tafi gaban mafarki. Kallon gidan dake opposite da gidan su Alfah yayi yajima yana kallon gidan,kafin yayi parking kofar gidan unguwar babu kowa amman hansken fitilu ya haske ko ina kamar ba dare ba. Tsaye yayi jingine jikin motar yana kallon gidan,ashe nan ne gidan su qanwarsa fiyah ko yaya iyayenta zasuji wannan labarin abun bazai masu dadi ba duba da jiya aka sallamo baban su daga asibiti. Mashin yaji yatsaya bayansa ya waigo yaga wani matashin Saurayi ya sauko yana kallonsa,isowa yayi yaba malik hannu suka gaisa yace"kana neman wani agidan" Malik yace"inadai son ayimun iso ciki zanyi magana da mutanen gidan" Dalha yana kallonsa yace"bari nashiga to muje bismillah" Gaba dalha yayi malik yana binsa abaya dalha yayi salama cikin gidan,dandanan mama da yesmin suka mike suna hada baki wajen tambayarsa. "Ina take tare

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});