Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 64

Chapter 64

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,301 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ki zuba ma fiyah ta karya amman kidan kamata ta wanke bakinta." Yesmin tace "bari na taimaka mata ita ta xuba abincin kafin ta fito,daker take tafiya don gabaki daya jiri takeji,ahaka fa wanke fuskarta da bakinta tayo Alwallah suka fito,capet din dake malale tsakiyar dakin ta zauna sama tana jingina bayanta da bango,idonta nason kallon Alfah Amman tanajin nauyi,tana bukatar nazari don kusan duk abunda ya faru kamar tana sani kamar tanajin wasu abubuwan,amman girman Allurar yahana ta gane meke faruwa amman idan bazata manta ba,wasu kalamai suna mata amsa kuwaa ciki kunnenta da kanta,zakiyya jiki asanyaye ta ajiye komi gaban fiyah bakinta kamar anmata dole tace"yajikin naki" Ko kusa bata dago ta kalleta ba,saidai ta ansa mata cikin voice dinta data dishe bata fita sosai. "I'm feeling better" Daga haka bata sake ce wa komi ba,yesmin ke tayata tana cin abicin,kamar bata so. "Zan wuce office Alfah tunda jikin yayi sauki,ko akwai abunda za,ai" Bakinsa yake gogewa da tishu yace"jirani mutai,ka saukeni gida nayi wanka,duk rintsi yau zanje station dinan" Mikewa yayi yana saka wayarsa gaban aljihu yace"zanje na dawo idan ma bandawo ba driver zai zo ya maidaku gida Allah ya sawake" Kanta akasa tace"nagode amman kabarshi zamu shiga taxi,ga yesmin nan ai" "Okay" Yawuce kurin,zakiyya tashi tai itama tana cewa"Allah ya sawake" Uffan fiyah batace ba saidai yesmin ta ansa mata,daga ita sai yesmin adakin sunyi shiru kowa da tunaninsa. "Adda su waye wadannan" Bata bata ansa ba tana tsakurar dankalin kamar bata so. Tace"nima ban sansu ba,karki isan da tambaya" Nurse ce tazo ta mayar da drip din daya rage ba,a idasa saka mata ba,fiyah tace ma yesmin ta zauna tayi break tasan bata yo ba. Ahankali suke firarsu har rafeea tazo suka cigaba da firar,tana cewa ta auna arxiki sunada interval kwana uku aida abun baiyi ba, feea tace ai tabaro mama na shirin tahowa ita dasu Anty jamila harda kanen mijinta. Wata faduwar gabace ga samu fiyah badai muhseen bane zai zo,innalillahi Allah yasa to Abdoul karya dawo. Malik ya sauke alfah ya wuce wajen aikin shikuma yashiga yayi wanka ya dauki kamshi,yayi masifar yin kyau kananan kayansa yasaka t-shet dark blue sai black trouser,combus dinsa blue and white color,yau babu fesin cap dinsa.zakiyya dake falon zaune tana kallo wanda gabaki daya hankalinta ba kan tv yake ba,ta luka duniyar tunani,taji kamshinsa ya mamaye falon Tsaye yake yana daura agogo ga waya kare ga kunnensa ya makale ta da kafadarsa yana magana,shagala tai dakallon sa wani mahaukacin sonsa yana sake cika ruhinta,dandanan kwallarta ta cika idonta yanzu ace duk yadda wannan guy din yake zai iya zama haramiyarta,wace irin kaddarace wannan data raba tsakaninta da masoyinta,ada Alfah bashida wani buri daya wuce kasancewa da zakiyyarsa,yasota wanda shi kanshi baisan adadi ba. Ita kanta alokacin har mamakin kaunar da suke ma juna take,ashe akwai lokacin dazai zo saidai ta ringa tunawa. Ganin zaifita yasa ta dawo natsuwarta tai saurin ringanshi isa wajen kofa tana tare hanyar,idonta da kwalla tace"Bazan bari kafita gidan nan ba yaya Abdoul sai kagaya mun matsayina,na gaji da hakin da kake nuna man acikin gidan nan.gabaki daya ka daina sona kadaina damuwa dani,ka dauki gurbina ka maye da wata watacan da batasan darajark............"inkika sake furta makamanciyar irin wannan kalmar akanta zan baki mamaki,matsa bani waje kafin tafin hannuna yasauka afuskarki,kije kiyo karatun tanatsu inkina son magana dani,stupid girl" Yasa hannu yajanye ta ya wuce yana jin haushinta har cikin ransa, Station din yaje ya samu dpo din wajen sukai magana,yake gaya mashi . "Ai yallabai wadannan yaran kangararrune,tunda aka kawosu ake gana masu azaba akan su fadi wanda ya sasu wannan aikin amman wancen shegen yana hanasu,wai muddin suka fada sai yayi ajalinsu." Iska Alfah yaja yana fesarwa ya kalli inda aka kulle su idonsa akan mamman,wanda ya canza kammani daga kamanninsa nada. Yadai samu darajar anmashi aikin kafarsa ancire bulet din,anyi dressing. Shafa kanshi yayi yana kallon dpo din yace"to waye yace kace saisun fadi wanda ya sasu,ai bama bukatar wanda ya sasu.tunda abun afili yake kucigaba da cin ubansu har sufita hankalinsu,har sanda zan sake dawowa." "Yallabai sau uku ana zuwa neman belin su muna hana wa,saboda girman laifinsu,aman idan aka sake dawowa zamu iya sakinsu gaskiya,duba da cewar mai zuwa belin babban mutunne" Kallon dpo din Alfah keyi ransa yana sake baci xuciyarsa ta fara hawa jiyake kamar ya shakesa yaringa naushin dan isaka. Cikin bala i da rabon dayayisa yajima yace"to kubada din,billahil azim saika rasa wannan yar jskar kujerar,koma ubanwa ye yazo kace ni nace ban lamunta ba,inbanda rashin hankali irin naku har ku bada belin yan iska irin wadannan bacin kuna da tabbacin sudin hadarine,to wlh ka maida hankali na dawo gobe babu su." Juya wa yayi har yakai kofa dpo din yace"yallabai mahaifinka ne fa" Cak ya tsaya bai jiyoba yana jin wani emotion yana zagaya wa dashi,wani rauni yana kama zuciyarsa har hakan ya shafi muryarsa yace"koma waye ban lamunta ba,inya sake xuwa just call me zanzo da kaina" "Okay yallabai" Ficewa yayi yana jin kamar ya fashe da kuka me hakan yake nufi,da saka hannunsa aka sace fiyah,kokuma yazo ne yayi belinsu don yana dan uwan matarsa,to koma ubanwaye din matarsa wallahi wannan karon saidai ayi uwar da za,ai bazai daga kafa ba.inma ace shine suka farauta zai hkr aman badai rayuwarsa ba safiyya kenan. Asibitin yayiwa tsinke don yasan drip din ya kare yana son sake ganin yadda jikin nata yake. Rafeea ta jima sosai saida su mama da anty jamila suka zo sannan tatafi,don ita tana da exam da yamma. Sosai jikin fiyah yayi sauki. Hira suke da su mama da anty jamila little fiyah tana wajenta tunda suka zo,sai wasa take mata suna dariya tare tana son babyn yadda take da fara,a kamar dai iyayenta. Muhseen ne yashigo shida uncle yahya,wata gaduwar gaba ce ta sake riskarta,kauda kai tai tana rokon Allah yasa kar Abdoul ya dawo.tarasa gane dalilin dayasa bata son yasan meke tsakaninta da shi. Gaida uncle tayi yana mata sannu. "Safiyya ashe kuma haka abun ya kasance,to Allah ya rufa asiri ya kyauta gaba kuma" "Amen uncle nagode sosai" Yace ma Anty jamila "kitashi muje rana tayi sosai,komun isa da wuri" Fiyah tace"Au Anty unguwa ma zaku ko" Tace"eh wai kaduna zamushiga zamuyo dubiya kanwar hajiyarsu bata da lafiya" "Allah ya bata lafiya man abarmun little anan nidai"dariya sukai muhseen idinsa kamar zaifado saboda wani salon kallo dayake ma fiyah,mama tace"bakida kangado,yarinyar nashan nono abarta wajenki sabkda daukar alhaki" Uncle yace yana murmushi"Aa mama ai tana da madara sai abarta kawai tunda ta rage kukan banza yanzu" Yesmin tace"eh wlh uncle to abarta" Hararar ta mama tai face"ankiya din kuda bakuda gaba,jamila anshi diyarki ku wuce kinji nima tashi zan naje na dora sanwa har daya saura." Goya little Antyn tayi sukai masu saisun dawk sukatai,muhseen ne yace "mama muje na kaiki ko" Tace"aa barshi muhseen naga ruwan ya kusan karewa saika taho dasu ko" Kokadan bata so haka ba wai meyasa sukeson hadasu,tsaki taja kadan tace"aa mama kije yakaiki nifa akwai ma wani ruwan da za,a sake sakawa,kuma yaya Abdoul da yaya malik sunce zasu dawo karsuxo bamunan" Kallonta mamar keyi na tsayin lokaci,ita kuma ta kawar da fuska don karta karanci wani anu

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});