Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 3

Chapter 3

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,313 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

masifar jaa cikin voice d'insa mai firgitarwa yafara magana cikin dakiya, "Wlh wlh wlh kajidai rantsuwa uku ko in kasake gigin anbata mun sunan wani cikinsu saina kashe kaina,har sau nawa zan jamaka kunne ne wai ehy." Furzar da iska yayi yana huci ya matsa daga kusada malik yana jan numfashi,duk da tsananin tsoran temper dinsa da yake,hakan bai hana shi sake magana ba,don yana ganin inyace zai ringa kyale shi bazai ta6a sauraren sa ba,balle har ya samu zuciyarsa tayi sanyi. "Wallahi Alfah kome zakai saina fad'a maka gaskiya,ayanzu bakada wani wanda zaigaya maka gaskiya saini,dole nafada maka kokayi aiki da ita ko karkayi nidai saina sauke nauyin alkawarin mahaifiyar.............wani uban naushi ya kawo wa malik,yayi aurin kaucewa azafafe,yanzu ma bangon ya kaiwa bugu amman saboda zafin rai bai damu da halin da hannun nashi yake ciki ba. Cikin wani irin yanayi ya ya kalli tiren daya malik shigo dashi,wata yar wuk'a ya gani baiyi wani tunani ba ya daukota,babu wani jinkiri ya saita hannunsa ga6ar hannunsa na dama ya yanke jijiyar dake wajen.dananan jini ya 6alle kamar an kunna famfo. Wata k'ara malik ya fasa yana tunkaro inda yake,shikuma yana ja baya yana cewa"karka nufoni,indan ka iso nan wlh saina sake yanke wata jijiyar,kafita anan inb fita ba nizan fita malik karka matsoni,kabarni na mutu kabarni natai inda zan fi samun jindadi,kuka malik keyi yana cewa"Alfah waya gaya maka mutiwa hutuce,mekayi wa Allah daza katai dashi matsayin guziri,inhar kamutu ahalin yanzu wlh wuta ce makomar ka......karka fita Alfah katsaya katsaya nace..........amman bai saurari malik ba ficewabyai daga cikin d'akin,waje ya nufa yannunsa jini kurun yake fitarwa b kadaba........kfi Malik yafoto tuni alfah yafice daga gidan,tafiya yake baisan inda yake jefa k'afarsa ba.........ko minute biyar bai da fitowa ba zai tsallaka titi,mota tayi sama dashi ya zube wajen babu numfashi. _back to story_ Likitanne yashigo yace"bai tashiba kenan,"malik yayi ajiyar zuciya yace"eh dr gashinan naga ma kun cire jinin,gashi ruwan shima ya kusan karewa.......akwai sauran ruwan da za asake saka maine." Dr have"sauran leda biyu hudu ce ansaka biyu,saura biyu da wani abune?" Shafa kai malik yayi yace"bani son ya farka ba agama saka ruwan ba,don ba lallai ya zauna ba daya farka zai iya fixge carnula ya fice." Jinjina kai yayi yace"wane irin mutunne shi haka,na lura yana da wata irin zuciya amma da gani akwai abunda ya faru dashi baya,don nidai nasan wannan fuskar sai yanzu na tuna inda nasanta.watarana na bar wajen aiki nan ina sauri zanje gida saboda maidakina tamun waya gidan babu lafiya,saurin danake yasa har nabanki wani mai anoconder kuma nai mashi babbar 6anna.........dandanan titin ya cika yafito yana ta bala,i saina biyashi gashi ko sisi ban dashi ga aljihuna,ga shi yaci kwalata duk hkrin da ake bashi ya rufe ido cewa saina biyashi,saiga wannan bawan Allah cikin mota shida driver sa,fitowa yayi yana tambayar lafiya? don titin ya cinkushe babu hanyar wucewa. Bayani nai mashi da halin da nake ciki na sauri inje ga iyalina.wlh malik check ya rubuta ma mutumen,na five hundred thousand bacin kuma kudin duka dubu dari uku ne..........naita mashi godiya ba karamin dadi najiba kullum ina adduar allah ya had'ani dashi inyana neman taimako nima nataimaka mashi." Malik ya yi ajiyar zuciya yace"Dr labarin mai tsayine kuma bazan iya baka shi ahalin yanzu ba,saidai ko nan gaba,amman tabbas Alfah yana cikin halin taimako,wlh nikad'ai bazan iya shawo kanshi ba." Gyara tsayuwa dr yayi yace"na fahimceka malik,karka damu ga ID card dina nan duk sanda kake bukatar taimakona,ga address dina nan ajiki da contact dina,insha Allah nima zan bada tawa gunmawar karka sare kacigaba dayin iyakar kokarinka har mukai ga ci...............shiru sukai ganin yana jujjuya kai yana ya mutse fuska,kafin ya bud'e idinsa yana kallon rufin d'akin..........idonsa ya sauka kan Malik da dr suna kallonsa suma. Da alama yana nazarin abunda yafaru dashi ne.duk sunyi zuru suna kallonsa gaban malik na fad'uwa saboda gudun abunda yake tunani.......ai baigama nazariba yaji wata irin shak'a da ya kawo mashi ya gama shi da bango,idonsa saboda tsabar masifa da zuciya kamar anzuba mashi garwashin wuta. "Meyasa kakawoni nan ehy,banace karka sake ka tab'ani ba,meyasa bazaka barni nabar masu duniyarba!"cikin tsananin tsawa yake maganar ya cigaba da cewa"malik!ka cuceni kacuce ni nace,yafada yana jijjigashi kafin ya tunkud'a shi ya fad'i. Kallon carnula dake jikin hannunsa yayi yayi mata wani irin fizga,dandanan ini yace yaga hanya k'ofa ya nufa atsananin fusace ya bude yafice tare da bankota da mugun karfi........Dr da malik binsa sukai agune don ahalin da yake ciki komi zai iya faruwa dashi yadda yake tafiyar zaka gane cewar gentle guy ne kuma k'ak'k'arfane.........gudu suke yana sauri shikuma amman sun kasa kamoshi,har sun bar titin asibitin sun yanki wata hanyar daban,duk yadda suka zo iskeshi abun yacitura........titin nasarawa suka hangoshi zai tsallaka kenan wata mota ta rugo da mugun gudu jikake..........kuuuuuuuuu karar burki da cin taya. Command share pls. Mrs bb ce Mom muhssen [9/17, 3:34 PM] Fauziya Madaki: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSER* *(ALFAH)* WRITING BY. MRS BB MOM MUHSEEN. WATTPAD NAME HUMAIRA7531. *DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB AND ALFAH FANS* 🅿️.......3💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSER* *(ALFAH)* WRITING BY. MRS BB MOM MUHSEEN. WATTPAD NAME HUMAIRA7531. *DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB AND ALFAH FANS* 🅿️.......3 Iya kar karfinta ta taka burkin,hankalinsu inyayi duba ya tashi.don sunyi tunanin sun banke shin,amman sadda ta bud'e idonta taganshi tsaye yana jiran motar tabi ta kanshi........daidai sadda su malik suka karaso wajen sai shashshekar gudun dasuka yi suke,da sauri suka fito daga cikin motar duk sun rud'e.don *FIYAH* tuni ta fara kwallah don gwanace wajen tsoro ........cikin sa,a Dr ya rik'esa gam yana kallonsa,idon nan nashi ya canza launi ya tausasa murya yace"plsss Alfah miye haka ya kakeyin abu irin na marasa hankali,meyayi zafi har haka ka tausayawa kanka kakuma ji tausayin wannan bawan Allahn abokin naka." Rafeea duk ta tsure saboda tunaninta ta bankesa saboda yadda ta taka burkin daf da shi sosai. "Assalamu alaikum,bawan Allah bakaji ciwo ba dai ko,kuyi hkr wlh ina saurine shikuma ya hau titi bai duba gabansa ba." Wani kallon wulakanci yajefa mata ya fixge hannun sa daga na Dr yana dogon tsaki,fiyah na gefe tana goge kwallah ganin babu abunda ya same sa........ran rafeea ya b'aci ainun,da abunda Alfah yayi mata kallon shi tayi,cikin fushi tace"dallah malam miye nayi man tsaki,daga d'an kuskure kadan zaka wani yiman kallon wulakanci,kana jaman tsaki ni nace kahau kan titi babu kulawa, ko angaya maka titin dakin gyatumarka ne ehy,"taja dogon tsaki ta juyawa zata bar wajen. Jitai kurun anfizgota kamar kwali omo cikin zafin nama,wani irin jan rik'o yayi mata baiyi wata wata ba ya saka tafinsa tare da iyakacin karfinsa ya kwalhe ta da kyakkywan mari. Ga baki d'aya wajen sun shiga shock,Rafeea jitayi ganinta ya d'auke da jinta.......idonta sun kada sunyi jajawur kamar gauta wata k'ara ta fasa tana dafe da wajen...........aguje fiyah ta karaso wajenta tana rikeda ita,jikinta rawa yake saboda yadda karar marin tafita. tabbas kasan wanda akai mashi ba karamar d'imuwa zai shigaba.cikin tsananin tashin hankali Rafeea ke kuka tana dafe da fuskarta,cikin kaushin murya yace"daga yau zakiyi gigin zagin wani bama niba,don ubanki yar iska da iyayenta basu bata tarbiyya ba." Ya fizge daga hannun dr da malik,yajuya tari taxi zai shiga yajiyota tana cewa"shege d'an iska,azzalumi ban yafeba wlh saina

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});