Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 47

Chapter 47

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,286 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

aikin data sha na zaman bakwai.taba kowa naman sa na ajiye nata gaba tanaci saida tayi rbin ledar sannan mama dataga bata da niyya saurara mashi ta anshe tana fada. Wajen karfe sha daya na safe tana dakin mama yesmin taje islamiyya,maman kuma tana kitchen. Ta dora sanwar rana. Karatu take sosai duk da xuciyarta bata gareta hankalinta ya kasu kashi daban badan,ga zakiyya tana son jin halin da take ga Abdoul tana son sanin koya tashi jikin yayi sauki bata sani ba,shikuma wanda xai kiratan ya gaya mata shiru bai kiraba...........tana cikin wanna halin wayarta tayi kara,saurin kallonta tayi yaga sunan sa tai saurin dauka tana kanga wa ga kunne. "Yaya malik ina kwana" "Lafiya lau qanwata ya kika tashi,fatan kinyi bacci daren jiya" Juya ido tayi alamun me yake nufi da tayi bacci jiya lobatai ba, "Na tashi lafiya yaya malik" Kallon Alfah yayi dake kurban tea mai dan gumi don ya gasa cikinsa,kamar baisan da wadda yake waya ba. "Kinjini shiru ban kira kiba,walh sai yanzun ya tashi babu jimawa inbashi ko"? Tana son ansa kodan taji muryarsa,don harga Allah Abunda take son jikenan,amman idan tayi hakan wane irin kallo zai mata,kenan ma fushin nata baije ko ina ba,tunda daga jin baida lafiya duk na rikice. "Kinyi shiru" "Kyalesa yaya malik,kadai gaidashi da jiki Allah ya sawake" "Aa karmuyi haka dake,sannu fa kurin zakiyi mashi" Rutse idonta tayi tanajin kamar tace eh yabashi amman ajinta zai zube, "Ka kyalesa yaya malik,aibadole saina yi magana dashiba daga nan ma idan na mashi Addua zatazo,rabu dashi yanzu ma karatu nake zan ajiye wayar,kila idan na samu time anjima da yamma infito inga jikkin zakiyyar" "Shikenan,amman banji dadi ba da kikace kar abashi,kingashi nan fa har ya miko hannu sa...........karka mun sharri ta dauka dagaske kake ban son wanna game din" Cewar Abdoul dake shan tea din sa. Ras taji abunda yace wani abu ya tsaya mata ga makoshi,watau shi ko ajikinsa bai damu ba.kwalla taji sun silalo mata ta kasa gogewa muryarta na rawa kamar zata fashe da kuka tace"yaya malik sai anjima,kayo mun text din asinitin da aka kaita da no din dakin" Saiyaji ta bashi tausai,hands free ya saka wayar yadda Alfah zaiji muryarta wata kila shima yaji abunda tajin. "Shikenan qanwata zan turo maki,amman kizo nan basai muwuce tare ba" Kwamciya tayi ta dora kanta kan filon mama hakanan kuka yana son kubce mata tace"yaya malik aina ce maka bazan sake xuwa gidan nan ba,kayi hkr bazan iya zuwaba mu hadu dakai Asibitin akwai maganar da zamuyi" "Shikenan saikinzo din" Kashe wayar tayi tana kwantawa ta dunkule waje guda tana kuka kasa kasa,wanan abun ya cuceta wai meke faruwa da xuciyata ne haka,Allah kaga niyyata karka saman Abunda zai wahalar dani bacin taimakone nayi,.......ta jima tana kukanta kafin bacci ya sureta. Tunda suka gama wayar ya silale inda yake ya kwanta,idonsa alumshe sautin muryata yake jin yana amsa kuwwa cikin kunnensa,tabbas kuka take wannane karon na biyu dake iya gane kukanta ta sautin muryarta,yana jin bai khauta ba abunda yayi matan shekaran jiyan,ya zaiyyi ba laifinsa bane zuciyarsa ce ta buga da ganin zakiyya,wadda tsawon shekara shidda ko mai kama da ita bai gani ba,haka xalika baya iya cewa ga lokaci guda daya zauna yayi tunaninta,saboda ya dora ma kanshi wata irin tsanarta da kinta gani yake tunaninta ma inyayi yacuci zuciyarsa,wani iri yakeji wanda bazai iya tantance meyakejin ba,amman shima da yana iyawa to tabbas kukan zaiyyi,don abun yafi karfi sa. Inama Zai iya lallashinta yanzu inama zai iya ansar no dinta yayi kiranta,bazai iya ba mezai ce mata dawace kalmar zaifara. Saiya tuna ranar da yake gidan yayarta fushin da yayi biyonsa da tai tana kwalla don ta bashi hkr,kenan ita bata camcanta dayayi mata hakan ba,dafe kansa yayi tare da saitin xuciyarsa don ciwo suke mashi. Malik ne yafito yayi shirin zuwa company tunda yau shibazai iya fita ba,kallonsa yayi yaga yadda yake shafa kirjinsa da kanshi ya iso inda yake ya zauna yace"daka taimaka ma xuciyarka kabar tunanin tunda bata so,inkuma inbaka no dinta kakirata niba wahala bane wajena,inkai kana ganin hakan kamar da wuya,gata nan na saka maka ka kirata ko karka kirata ya rage naka.daka cire ma kanka wannan nauyin ka fuskanci reality da yafiye maka sauki Abdoul,amman nasan indan nafurta abun da yake damunka zaka karyani kuma zaka dauki zafi,don haka nidai karufa man asiri kacire damuwa,zanje company daga can zan biya store.likita zai dubaka anjima amman kafin nan zanje naga jikin zakiyya." Uffan bai cemashi ba idonsa a kulle bai bude ba,har malik din yafita kallon wayarsa yayi yaga digit din numbers din daya kera mashi,daukar wayar yayi yana kallonsu na dan lokaci kafin yasa hannu ya goge su tas. Ya maida ya ajiye. Kuyi hkr babu yawa wlh masassara nake. Daker idan zanyi sanyin idaniya plsss kumun uziri. It's for sale if u need it meet me 09934722970 Don't share it plsss I beg [9/17, 3:41 PM] Fauziya Madaki: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSER* *(ALFAH)* *ABDOUL-NASSER NA KUDINE,INKIKA KARANTA BAKI BIYA BA KEDA LILLAHI,GA MAI BUKATA ZAI IYA TUNTUBAR WANNAN NO DIN 09034722970. WRITING BY. MRS BB MOM MUHSEEN. WATTPAD NAME HUMAIRA7531. *DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB AND ALFAH FANS* 🅿️.........34 Bata tashi daga baccin ba sai bayan azahar,tatashi tayi wanka ta dawo tayi sallar azahar tana bitar haddarta ta dade bata biya ba,yesmin ta shigo masu da abinci falon mama sun kallon wani film merlin,mama itama hada ita ake kallon. Suna ci suna hira hankalinsu akan film din yayinda fiyah hankalinta nacan wajen tunanin karyar da zatayi ta fita anjima. Mama tace"safiyya duk don na hanaki naman nan kike fushi" Shagwabe fuska tayi "mama bafa haka bane,kawai dai tunanin exam nake wlh banyi wani karatun kirkiba,gashi ko time table bana da ita" "Addana garin ya haka,to ya za,ai kisan lokacin da zaku fara,kinma tunamun jiya Anty rafeea tazo nemanki" Mama tace"kitambayeta kila ita bazata rasa ba" Murna ta kamata ganin ta samu hanyar da take so. "Aa itama inajin ita tazo nema wajena,amman bari inkira Amatullah nasan ta siya." Tana jawo wayarta kamr gaske. Dandanan tayi wayar karya ta ajiye"mama tace ta siya zanje in ansa sainayi photocopy" Mama tace"haka din za,ai maida hankali kigama kokinje kidawo kar babanku ya tadda bakinan" Kamar zatai kuka tace"mama yanzun fa rana tayi kibari ayi sallar la,asar basai inje ba bafa nisa keda akwai ba unguwar tasu." "Shikenan Allah ya kaimu anjiman bandai so kikai magaruba awaje shiyasa." "Insha Allah mamana bazan Kai ba" Haka suka cigaba da hirarsu suna kallansu har suka gama cin abincin. Mama tana mitar baba baidawo gida yaci abinci ba,fiyah nadariya tace"Kai mama Kika Sani ko aiki ya mashi yawa yau." Ana kiran sallar la,asar tatashi tayi salla tana gama wa tacanza kaya xuwa doguwar riga pink ta wani material da sukai ankodinsa su uku Anty da yesmin sai ita. Yar karamar jikkarta tadauka ta saka wannan m.card din ciki,sannan ta fesa turare tafito tana cewa mama "mama zan tafi saina dawo" "Baki tafiya da yesmin" Bata fuska tai"Kai mama kamar dai wata wace zata bace" "Aisaiki ta tafiyar tunda kinfison kiyi tafiya kedaya kamar mayya" Ficewa tayi tana saurin nufar get din estate din. Cikin Sa,a ta samu taxi bata tsaya ko inaba sai asibitin,ta biyashi

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});