Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 78

Chapter 78

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,300 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

mai shegen laushi,tana jan numfashi da ajiyar xuciya.wani irin yanayi ne yake dawainiya da ita,hakika masoya sun sha azabar soyayya haka take ashe. (Nikau nace aa fiyah,kune dai dakuka saka wani abu arai kowa ya kasa furtaw) Shiru tayi mashi bata ce komi ba. "Ohhhhh may god kimun magana mana,menene ya saka ki yimun asarar hawayena,inhar baki fada ba zance ban yafe ba xubar dasu dakikai ba kan ka ida ba." Still bata yi magana ba murmushi yayi yana shafa kanshi,wani dadi yana kamashi at least dai yasan yana da wani matsayi mai girma cikin ranta,kuma yana da tabbacin shine silar kukanta.ashe dai ni jarumine tunda yadda nakejin ta abun bazai kwatantu ba,kukama rahma ne inhar ya samu yayi. Can yajiyo yar muryarta data dishe don kuka wadda yajita har cikin yan cikinsa don masifar dadin da tai mashi,yana imaging yadda bakinta yake furtawar,dan mitsitsi dashi kadan ya hana bai dariya ba sai ya dake yana saurarenta. "Wlh Allah saiya saka mun.....baka da tausayi ko kadan kasan duk yadda xaka cutar dani,ba tun yanzu kake saka idaniyata fitar da kwalla ba,Allah yana kallonka kuma zai saka mun" Ta kare da shagwaba kamar zata sake yin wani kukan,Abdoul mirginawa yayi yana manne wayar ga kafadarsa yana ajiyar heart. "Menai maki kuma safiyyah?atunanina ban miki komi ba,idan abaya nai maki wannan kinyi mun uxiri kema kinsan cikin condition din danake,kuma har yau kin ki bani damar da zan baki hkr abisa abunda nai acan lokacin,sannan ai bana jin nai maki abunda zakiyi kuka safiyya!nine kikai ma abunda zan dade ina kokawa,meyasa ke baki ganin laifinki sai nawa?" Cikeda shagwaba wadda bata san tanayi ba,jitai kurin tanayi don azahirin gaskiya tana cikin wata kauna da ta kasa control din mind dinta. "To ni menai maka ehy,ka wai nidai nasan ban maka komi ba ko." Murmushi mai hade da dariya yayi yace"naji toni me nai maki zaki tusani gaba da kukan shagwaba,ina mijin naki I think naji baba yace kin tsayar da wanda zaki aura meyasa saini zaki ma kuka" Hararar wayar tai tace"ai bashi yayi mun ba kaine" Shiru yayi yana jinjina rigimarta,shida ta gasa ma maganganu masu zafi baice haka ba sai ita mai raki. "Shikenan naji na dauka ayi mun hkr to" "Uhn uhm ni banyi ba" "To mezanyi ki huce?" Numfashi taja tanajin inama zata ganshi,inama zaizo baba ya barta tafita tana dokin sauraren jin ta bakinsa,tana son jin dagaske abunda takeji akanshi shima haka,idan hakane meya zai hana su mallaki juna..........wata xuciya tace xakiyya!runtse ido tai tanajin zafin sunan da xuciyarta ta anbata mata,har saida ta furta innalillahi. "Menene kuma" Ya fada. Numfashi taja tace "ba komi" "Ko kina son ganina ne inzo" Kamar tace eh amman saita daure tace"baba ya hana" "Baba ya hana kokuma kema kin hana kanki ganina wanene yafi karfi" Tabbas kila yanzu baba ya barshi ya ringa ganinta,tunda babu maganar muhseen amman bata tunanin hakan,don tasan baba yana hangen wani abun na daban. "Aa ba haka bane,kawai dai tunda ya hana mu hkr mana" "Zaki iya hakura dani safiyyah?" Kirjinta saida ya ansa,tabbas bazata iya ba koda ta iya tokau ba cikin dadin rai da kwanciyar hankali ba,cikin kwana hudu ma ta jigata inaga rabuwa ta har abada,bazata iya cewa komi akan haka ba,karta sake kwafsawa irin rannan. "Nima ban Sani ba" "Kin sani baza dai kifada mun ba,acikin kwanakin da mukai bamu hadu ba bamuyi waya ba,wane irin abu kika yanke akan hakan,still kinajin zaki cigaba da kulani ko zaki yadda ni ki kama mijinki" "Ban gane ba?nifa banda miji wanda baban ma yace yabadani din yesmin na barma wa,shima baidace dani ba" "Okay sai waye yadace dake" "Oho" Murmushi yayi yace"ni mekika daukan" "Yaya Abdoul inada exam gobe banma yi karatun kirkiba zan kwanta saida safe" Da yaushe kike fitowa. "Around 4:30 mun fito wani abune?" "Aa daman don na daukoki" "Bana so fa,baba zai ganmu" "To menene badai kin barwa yesmin wancen guy din ba,nikuma ba saina na shigo ba" "Kashigo kuma?kayi me" Dariya yayi yace"ince ma baban ni abani inyi manage" "Kuttt dani din?nizakai manage dani,to banso nikuma aiba neman kai yake dani ba baban,akwai maza cike da gari zan samu wanda nake so" "Ni bakisona kenan" "Kamar yadda kaima ba sona kake ba,zaka auran don ka maidani kurin borar ka,kuma ma kanada zakiyya me zakai da local irina" Shi wlh sai yanzu ma ya tuna da wata zakiyya,gaskiya yana cikin case ina zaya da mata har biyu.baida wannan tsarin yana son only one wife da zata haifa mashi yaransa masu tarbiyya,ina zai iya tara mata biyu. "Ina ruwanki da zakiyya ne wai,ko kishinta kike" Tsaki taja cike da jin haushi tace"Menene kishi?Allah ya kyauta to kishi basai ana son mutun ba" "Ya tabbata ba kisona ngd safiyya,ba komi tunda zakiyya na sona kuma ashirye take data aureni kinga no need na bata ma kaina lokaci,shikenan saida safen." Dandanan tabi ta rikice "yaya Abdoul........shiru yayi ya kyaleta kuma bai kashe wayar ba. "Kaji wai fushi kayi,yaya Abdoul magana fa nake maka,kayi shiru." Muryarta harta fara rawa sarkin kuka kurin. Ya furta "Badai kin barwa zakiyya ni ba,baki sona saboda baki iya auren kalata,dan giya mai neman mata ko?haka kike kallona har yau shiyasa kike cemun bazaki iya auren irina ba. Baiyi mamaki dayaji muryarta dakuka ba tana cewa"ni wallahi ba haka ba,nibana maka wanan kallon wlh na manta ma kataba shan wata giya,miye haka wai sai ta sake rushewa da kukan. Dadi ya kamshi yace"it's oky,yi shiru na bari ba haka kike kallona ba to meyasa rannan kika gaya mun haka" Cikin kuka tace"to ai ba laifina bane,kaine kakesani abunda banyi niyya ba" "shikenan ya isa yanzu zan iya sake dawowa karo na biyu na nemi iznin baba ya bani ke" "Baba fa zaiyi mun fada" "Bazan Bari yayi maki fada ba,kinji an safiyya na" Lumshe ido tai tanajin wani irin farin ciki,amman har yanxu bataji abunda take son ji daga gare shi ba,shiyasa tace"uhn bacin ba sona kake ba taya xai baka yarsa kaje kayita dukanta" Xaro ido yayi kamar tana ganinsa yace"rufaman asiri na dakeki,wlh bazan iya kai hannuna da sunan duka ajikin ki ba kiyarda dani,dacan ma kuskurene amman zan gyara oky" Shiru tayi tana sauraren numfashinsa. "Safiyyah" Can kasan makoshi yankirata,saida duk wata kofar gashi ta jikinta tatashi,daker ta ansa. "Na,am" "Safiyyah" Lumshe ido ta sakeyi tace "na,am inata fa ansawa." Ajiyar xuciya yaja sosai ya sake sauke muryar kasa. yace" *Did you marrie me?*" Dammmm taji kirjinta ya buga gabanta ya cigaba da faduwa,wannan kalmace mai nauyi bazata iya ansa mashi ba bacin bata san matsayinta acikin ransa ba,baya ga haka ga zakiyya bazata iya zaman kishi da ita ba,duk da tsabar kaunarsa da take ji ta gama kewaye mata ko ina. Numfashi take ja ahankali tama rasa me zatace mashi. "Safiyyah are. you hair me" Daker tace"uhm inaji" "Bakice komi ba" "Yaya Abdoul ba fa ka sona,ina kataba ganin anyi aure babu so tsakanin ma,aurata" Numfashi yaja yanajin wani sabon yanayi akanta,wata irin kaunarta yakeji tana bin ko ina na jikinsa. "Wannan ne kurin damuwarki?" Can kasa tace"uhm" "Goben kijirayeni cikin school dinku,plss kiyi zamanki bakin department zanzo harnan nima alokacin sainaji result dina,hakan ya maki" Jikinta yayi sanyi sosai tabbas tana sonji daga

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});