Chapter 78
Chapter 78
mai shegen laushi,tana jan numfashi da ajiyar xuciya.wani irin yanayi ne yake dawainiya da ita,hakika masoya sun sha azabar soyayya haka take ashe. (Nikau nace aa fiyah,kune dai dakuka saka wani abu arai kowa ya kasa furtaw) Shiru tayi mashi bata ce komi ba. "Ohhhhh may god kimun magana mana,menene ya saka ki yimun asarar hawayena,inhar baki fada ba zance ban yafe ba xubar dasu dakikai ba kan ka ida ba." Still bata yi magana ba murmushi yayi yana shafa kanshi,wani dadi yana kamashi at least dai yasan yana da wani matsayi mai girma cikin ranta,kuma yana da tabbacin shine silar kukanta.ashe dai ni jarumine tunda yadda nakejin ta abun bazai kwatantu ba,kukama rahma ne inhar ya samu yayi. Can yajiyo yar muryarta data dishe don kuka wadda yajita har cikin yan cikinsa don masifar dadin da tai mashi,yana imaging yadda bakinta yake furtawar,dan mitsitsi dashi kadan ya hana bai dariya ba sai ya dake yana saurarenta. "Wlh Allah saiya saka mun.....baka da tausayi ko kadan kasan duk yadda xaka cutar dani,ba tun yanzu kake saka idaniyata fitar da kwalla ba,Allah yana kallonka kuma zai saka mun" Ta kare da shagwaba kamar zata sake yin wani kukan,Abdoul mirginawa yayi yana manne wayar ga kafadarsa yana ajiyar heart. "Menai maki kuma safiyyah?atunanina ban miki komi ba,idan abaya nai maki wannan kinyi mun uxiri kema kinsan cikin condition din danake,kuma har yau kin ki bani damar da zan baki hkr abisa abunda nai acan lokacin,sannan ai bana jin nai maki abunda zakiyi kuka safiyya!nine kikai ma abunda zan dade ina kokawa,meyasa ke baki ganin laifinki sai nawa?" Cikeda shagwaba wadda bata san tanayi ba,jitai kurin tanayi don azahirin gaskiya tana cikin wata kauna da ta kasa control din mind dinta. "To ni menai maka ehy,ka wai nidai nasan ban maka komi ba ko." Murmushi mai hade da dariya yayi yace"naji toni me nai maki zaki tusani gaba da kukan shagwaba,ina mijin naki I think naji baba yace kin tsayar da wanda zaki aura meyasa saini zaki ma kuka" Hararar wayar tai tace"ai bashi yayi mun ba kaine" Shiru yayi yana jinjina rigimarta,shida ta gasa ma maganganu masu zafi baice haka ba sai ita mai raki. "Shikenan naji na dauka ayi mun hkr to" "Uhn uhm ni banyi ba" "To mezanyi ki huce?" Numfashi taja tanajin inama zata ganshi,inama zaizo baba ya barta tafita tana dokin sauraren jin ta bakinsa,tana son jin dagaske abunda takeji akanshi shima haka,idan hakane meya zai hana su mallaki juna..........wata xuciya tace xakiyya!runtse ido tai tanajin zafin sunan da xuciyarta ta anbata mata,har saida ta furta innalillahi. "Menene kuma" Ya fada. Numfashi taja tace "ba komi" "Ko kina son ganina ne inzo" Kamar tace eh amman saita daure tace"baba ya hana" "Baba ya hana kokuma kema kin hana kanki ganina wanene yafi karfi" Tabbas kila yanzu baba ya barshi ya ringa ganinta,tunda babu maganar muhseen amman bata tunanin hakan,don tasan baba yana hangen wani abun na daban. "Aa ba haka bane,kawai dai tunda ya hana mu hkr mana" "Zaki iya hakura dani safiyyah?" Kirjinta saida ya ansa,tabbas bazata iya ba koda ta iya tokau ba cikin dadin rai da kwanciyar hankali ba,cikin kwana hudu ma ta jigata inaga rabuwa ta har abada,bazata iya cewa komi akan haka ba,karta sake kwafsawa irin rannan. "Nima ban Sani ba" "Kin sani baza dai kifada mun ba,acikin kwanakin da mukai bamu hadu ba bamuyi waya ba,wane irin abu kika yanke akan hakan,still kinajin zaki cigaba da kulani ko zaki yadda ni ki kama mijinki" "Ban gane ba?nifa banda miji wanda baban ma yace yabadani din yesmin na barma wa,shima baidace dani ba" "Okay sai waye yadace dake" "Oho" Murmushi yayi yace"ni mekika daukan" "Yaya Abdoul inada exam gobe banma yi karatun kirkiba zan kwanta saida safe" Da yaushe kike fitowa. "Around 4:30 mun fito wani abune?" "Aa daman don na daukoki" "Bana so fa,baba zai ganmu" "To menene badai kin barwa yesmin wancen guy din ba,nikuma ba saina na shigo ba" "Kashigo kuma?kayi me" Dariya yayi yace"ince ma baban ni abani inyi manage" "Kuttt dani din?nizakai manage dani,to banso nikuma aiba neman kai yake dani ba baban,akwai maza cike da gari zan samu wanda nake so" "Ni bakisona kenan" "Kamar yadda kaima ba sona kake ba,zaka auran don ka maidani kurin borar ka,kuma ma kanada zakiyya me zakai da local irina" Shi wlh sai yanzu ma ya tuna da wata zakiyya,gaskiya yana cikin case ina zaya da mata har biyu.baida wannan tsarin yana son only one wife da zata haifa mashi yaransa masu tarbiyya,ina zai iya tara mata biyu. "Ina ruwanki da zakiyya ne wai,ko kishinta kike" Tsaki taja cike da jin haushi tace"Menene kishi?Allah ya kyauta to kishi basai ana son mutun ba" "Ya tabbata ba kisona ngd safiyya,ba komi tunda zakiyya na sona kuma ashirye take data aureni kinga no need na bata ma kaina lokaci,shikenan saida safen." Dandanan tabi ta rikice "yaya Abdoul........shiru yayi ya kyaleta kuma bai kashe wayar ba. "Kaji wai fushi kayi,yaya Abdoul magana fa nake maka,kayi shiru." Muryarta harta fara rawa sarkin kuka kurin. Ya furta "Badai kin barwa zakiyya ni ba,baki sona saboda baki iya auren kalata,dan giya mai neman mata ko?haka kike kallona har yau shiyasa kike cemun bazaki iya auren irina ba. Baiyi mamaki dayaji muryarta dakuka ba tana cewa"ni wallahi ba haka ba,nibana maka wanan kallon wlh na manta ma kataba shan wata giya,miye haka wai sai ta sake rushewa da kukan. Dadi ya kamshi yace"it's oky,yi shiru na bari ba haka kike kallona ba to meyasa rannan kika gaya mun haka" Cikin kuka tace"to ai ba laifina bane,kaine kakesani abunda banyi niyya ba" "shikenan ya isa yanzu zan iya sake dawowa karo na biyu na nemi iznin baba ya bani ke" "Baba fa zaiyi mun fada" "Bazan Bari yayi maki fada ba,kinji an safiyya na" Lumshe ido tai tanajin wani irin farin ciki,amman har yanxu bataji abunda take son ji daga gare shi ba,shiyasa tace"uhn bacin ba sona kake ba taya xai baka yarsa kaje kayita dukanta" Xaro ido yayi kamar tana ganinsa yace"rufaman asiri na dakeki,wlh bazan iya kai hannuna da sunan duka ajikin ki ba kiyarda dani,dacan ma kuskurene amman zan gyara oky" Shiru tayi tana sauraren numfashinsa. "Safiyyah" Can kasan makoshi yankirata,saida duk wata kofar gashi ta jikinta tatashi,daker ta ansa. "Na,am" "Safiyyah" Lumshe ido ta sakeyi tace "na,am inata fa ansawa." Ajiyar xuciya yaja sosai ya sake sauke muryar kasa. yace" *Did you marrie me?*" Dammmm taji kirjinta ya buga gabanta ya cigaba da faduwa,wannan kalmace mai nauyi bazata iya ansa mashi ba bacin bata san matsayinta acikin ransa ba,baya ga haka ga zakiyya bazata iya zaman kishi da ita ba,duk da tsabar kaunarsa da take ji ta gama kewaye mata ko ina. Numfashi take ja ahankali tama rasa me zatace mashi. "Safiyyah are. you hair me" Daker tace"uhm inaji" "Bakice komi ba" "Yaya Abdoul ba fa ka sona,ina kataba ganin anyi aure babu so tsakanin ma,aurata" Numfashi yaja yanajin wani sabon yanayi akanta,wata irin kaunarta yakeji tana bin ko ina na jikinsa. "Wannan ne kurin damuwarki?" Can kasa tace"uhm" "Goben kijirayeni cikin school dinku,plss kiyi zamanki bakin department zanzo harnan nima alokacin sainaji result dina,hakan ya maki" Jikinta yayi sanyi sosai tabbas tana sonji daga
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101