Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 56

Chapter 56

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,300 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

bita wajen xuwa wajen mota ta anshi no dinsa sukai sallama. Malik shiryawa yayi don samun daddy ayi wacce za,ai don yau insha Allah sai sun saurari abunda kecikin m.card din Daddare ya shirya yace ma Alfah zaije wajen dady yadawo,da ido kurin yabishi don gabaki daya yarasa natsuwarsa,rashin yarinyar na kwana biyu duk ya rikita mashi tunani,matakin da ta dauka akan su baimashi dadi ba,jiyake kamar yatuge wannan shege drip din ya je gidansu,amman yasan bazai iya zuwa ko da kofar get din ba,balle har yashiga ya dauki alkawarin shida maitama har abadan abada. Malik har gida ya iske dady suka gaisa da matarsa mai tsananin kirki,itace ma tai mashi iso ga dadyn har babban falonsa,aka kawo mashi kayan sha da ci amman ba tasu yake ba,soyake akawo karshen komi dake faruwa cikin rayuwar Abdoul,abun ya isa haka yana cikin kewa da mararin ganawa da mahaifansa,amman wannan babban ginshikin yatare komi,ya hana komi tfiya yadda ya kamata. "Malik sannu da zuwa ya hanya" Ya na zaune kasa ya sadda kai yace "lafiya lau dadyy,ya nasameku" "Angode Allah,ya jikin Abdoul din fatan yana samun sauki sosai,naso nazo dazun nasake dubashi sao aka kirani office,amman dasafe zamuzo da yara harda mamansu mudubashi" "Allah ya Kai mu dady,dayake ma goben ake saka ran sallamarsa ai" "Masha Allah Alan ya sa iyakar wahakar kenan,da alama dai akwai magana ko,to inajinka" Muskutawa yai ya ciro wannan m.card din daga cikin aljihun rigarsa,ya nadesa cikin wata takadda ya warwaresa yana cewa"dady wannan shine kedauke da duk wasu abubuwa damuke son sani game da makarkashiyar da aka shirya ma Abdoul,kuma anan ne zamu san suwaye suka hada wannan abun,musan kuma dalilin dayasa sukai hakan idan kayarje man zan sashi ga system din danazo dashi mu saurara." Jin jin jinakai dady yayi yace"naji dadin wannan magana malik,kuma hakika kaida wannan yarinya safiyya Allah ne zai biyaku,domin kunyi abunda za,a yaba maku Allah yayi maku Albarka,amman ina kta safiyyar ba kace tare zaku zo ba" Cikin jimami yayiwa dadyn bayani ataikaice shima ya fahimceta yace "babu damuwa ai tariga ta gama komi sai fatan Allah ya biyata,yabata miji nagari wanda zai kula da ita har karshen rayuwarsu.ni da nai zaton ma kana sonta Abdoulmalik,har nafara murna ta samu miji na kwarai." Murmushi yayi yana sosa kai yace"ai dady da nasotan,kuma naita fatan daburin na zama mijin nata,saidai duba da wasu abubuwa danai naga bani ne nadace da ita ba, ABDOUL-NASSER yafini bukatar samun mata kamarta,domin shine koda yaushe rayuwarsa take cikin hadari,koda yaushe ake neman kassarashi,sainaga safiyya yarinyace mai hankali da natsuwa tanada wasu abubuwan da zaka nemesu ga mata dayawa baka samesu ba,ga ilimin addini tana da wayau da dubara komi zatai saita yi nazarinsa ta lakancesa kafin ta aiwatar,haka zalika tana da juriya sosai ga uwa uba hkrinta shiyasa naga gara na hkr wata kila silar sadaukarwar danai Allah yaban makamanciyarta.shiyasa nai iyakar kokarina wajen ganin nahada su da juna,har saida naga nayi nasara don ina kyautata zaton suduka suna son juna Allah ne bai basu ikon furtawa ba,yanzun haka yana can cikin damuwar rashin ta kwana nan." Jinjina kai dady yayi yace"kayi tunani maikyau malim,kuma insha Allah Allah bazai barka haka ba,hakika zai maka tanadi na musanman.naji dadin jin wannan labarin don haka kasaurari kyautata daga gareni insha Allah." Dariya yayi yace"to godiya nake dady,zamu iya kunna wa duba da lokaci" Dadyn yace "mezai hana bismilla nima na zaku danajin abunda kefaruwa don akwai wani zargi cikin raina" Malik yasaka wannan m.card ga system dinsa yashiga yana uploading dinsa har yahau yashiga cikinsa yana dubawa,recording ne kashi uku guda daya kuma vidion ne. Kuyi hkr jiya nayi alkawari na saba,wlh ban dawo da wuri ba shiyasa kuyi manage dashi plsss *don't share it plss I beg* [9/17, 3:42 PM] Fauziya Madaki: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSER* *(ALFAH)* WRITING BY. MRS BB MOM MUHSEEN. WATTPAD NAME HUMAIRA7531. *DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB AND ALFAH FANS* 🅿️.........41 Sanda yaje har anrubuta sallamar dr yana sake nanata masu kiyaye dokokin dasuka gindaya ma Abdoul din,na daina shan abu mai zafi sosai ko mai sanyi sosai,daga yadda malik yake Abdoul yasan ba yacikin mood mai dadi.kallonsa yayi tayi suna tafiya zuwa gida,hardai ya kasa jurewa yace masa"malik kana lafiya kuwa?" Ba tare da ya kallai ba yace cikin sanyin murya"kaina keciwo shiyasa" Shiru Abdoul yayi amman badan yayarda da abunda yafada mashin ba,baisake tambayarsa ba don yasan ba fada mashin zai ba.lumshe idonsa yayi yana sauraren xuciyarsa dake ta dawo mashi da moments dinsu nabaya shida safiyyah,wani yayi murmushi wani ya jinjina kai yana nadamar wasu kalamansa na baya da yake jifarta dasu,harta hkr batai fushi ba tacigaba da taimakonsa.yayi bincike bai hango yarinya kamarta mai irin wannan hankalin da hkr da tarbiyya ba,ga natsuwa idan zai kwana yana lissafa halayyarta kilan bazai gama ba,don yalura kullum da wasu sabbin halayen zai sameta.ahankali yafurta "mijinki ya More" jiyai kirjinsa yayi masa nauyi saboda abunda ya furta,kenan wani duk zai samu wadannan abubuwan gareta,wata xuciyar take kitsa mashi inka yarda kana sonta maizai hana kafito kabayyana hakan,girgiza kai yayi shikadai malik na ganin yanayinsa baice mashi komi ba,don shima danashi kason tunanin kilaman saiyafi nashi rudani da rikitarwa.har sukaje gida babu mai magana suna yin parking zakiyya tafito aguje tana zare ido.idonta ga Abdoul tana kallonsa,malik yadaure yayi mata murmushi yace"kekadai gidan ko,gashi babu abun ci gidan Allah yasa ko tea kinsha" Kwalla cike da idonta tace"aa bazan iya saka komi acikina ba yaya malik,hankalina duk baya kaina yana wajen ku ina tunanin ko yajikin sa." Abdoul yazo yara b'ata yawuce baice mata cikanki ba,duk suka bisa dakallo. Malik yace"yaji sauki sosai,aikin gani ko." Sadda kaitai kasa yace"karki damu kanki akansa zai warware zaku daidaita,bari nayi waya akawo mana take away kije ki kwantar dahankalin ki karma kisama kanki damuwarsa zai waiwayeki ne" Juyawa sukai suka wuce cikin apartment din babban wanda keda different part's acikinsa. Zube yake kan kujera ya rufe ido still tunani yake. "Daka sassauta ma ranka don gudun abunda zai sameka,kasaurari xuciyarka abunda kaga ta yanke maka akai maikyau sai kayi anfani dashi,amman dogon nazarin bashida anfani amman idan kaji shawarata." Ya wuce dakinsa habarsa da zakiyya daketa hawaye ita kogajiya batayi,tsaye take gefensa takasa mashi magana gani take kamar zai mata tsawa. "Kin tsaya bisa kaina plss move" Silently yayi maganar matsawa tai ta dawo gabansa tana zama tare da tankwashe kafafunta tace"yaya Abdoul yajikin naka" Batare daya kalleta ba idonsa yana kallon rufin falon yace"da sauki" Shiru tai ta cigaba da alwallar kuda kamar taza rushe da kuka tace"yaya Abdoul na gaza samun hanyar dazan fuskance ka da batutuwan dake bakina,bansan dame zan fara ba saboda nasan nidin mai laifice wajen ka,amman yaya Abdoul ka fahimceni duk abunda nai nayisa ne bisa dalilai da yawa kaban dama na warware maka dukullin dake faruwa." Malik ne yafito yanajin abunda take cewa yace"kyaleshi zakiyya bayanzu ba,akwai lokaci yana xuwa tashi kije ki shirya ga abinci nan ankawo.tashi tai tatafi kamar wadda kwai ya fashewa acikinta. 💕💕💕💕💕💕💕💕💕 Jikin baba yayi sauki sosai yana samun kulawar likitocin yadda ya kamata,har ansallami Alh muazzam amman kullin sai yazo ya duba jikin baban,mama dai ba dadin hakan takeji ba amman baba ya hanata nunawa,anty jamila ma sun sake xuwa ita da uncle harda

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});