Chapter 79
Chapter 79
gareshi,amman kuma tana jin bakuncin kalmar tun kafin tajita akunnuwanta. "Eh" "Okay good night and sleep well ban yarje maki tunanina ba har sai bacci ya daukeki" Shagwabewa tai. "Yaya Abdoul taya zan iya hana xuciyata tunani" Lumshe ido yayi muryarsa tai sanyi yace"shikenan kiyi ammab kadan kinjiko kiyi addua sosai da asuba saikiyi tilawar karatun saiya fi zama" "Okay by" Ta kashe wayar tana mulmulawa can karshe gadon tanajin duk wata damuwarta ta yaye,yanzu tsakaninta da babane kurin case dinta shin zai anshi abdoul ko zaice baimashi ba.wannan shine fargabanta sannan ya matsayin zakiyya yake ahalin yanxu wajen Abdoul,zata so ace tasan wane hukunci ya yanke tsakaninsu. ************ Karfe bakwai yabar gida ko malik ma bai gaya ma inda zashi ba,duk da yaga sai wani sha mashi mur yake baisan dalili ba. Office ya tsaya ya fara rage ma kanshi wasu abubuwan don idan ya tafi wasu bazai yisu yau ba. Ahaka har karfe goma ta buga ya tashi ya fito yabar sakon duk wanda yazo ace baya nan,ya kirasa awaya. Maitama yayi kwana da motarsa ya nufa maganganun zakiyya suna sake dawo mashi dalla dalla,yana jin zafi da kunan abun duk yadda yake son daukar hukunci da hannunsa yasan hanashi za,ai amman tabbas idan yaga umma babu abunda xai hana bai kwalwa mafa maruka guda biyu da zasu fiddata daga cikin hayyacinta. Sukuwa su zuwairat da Haulat da Ameena wata tsanarsu yakeji,jiyake inama zai ciresu daga jikinsu ace su ba yayan Abi bane,aman yasan kome sukai kome suka xama dole za,a kirasu da yaran Abbin. Ya na shigawo yaga baban fiyah zai fita yayi saurin tsayawa yafito yana durkusawa kadan yace"baba ina kwana" Baban bai nuna komi ba ya ansa cikin fara,a yace"anzo wajen Alh ko" "Yace aa dama dadyne yake nemana ba wajensa zanje ba" "Shidinma ya dace ka mance dakomi Nasser kaje kuyafi juna,komi yana da dalili haka kuma kaddarar mutum bai isa ya kauce mata ba,aduk sadda kaji ranka da xuciyarka suna raya maka wani abu marar kyau kayi saurin korar shaidan ka kuma yi auziyya kana hazbunallahu wani imal wakil,Allah ya daidaita lamauran kaje Allah ya maka Albarka" Cikeda jin dadi Abdoul yce"na gode baba insha Allah zanyi yadda kace nagode sosai Allah ya kara girma" Ya fiddo kudi aljihu baisan konawa bane yace"baba ka hau taxi don girman Allah karkace bazaka ansa ba,wlh badan komi nai ba alherine nayi maka badan baka dasu ba" Murmushi yayi baban yace"don nayi maka nasiha nasser saika biya ni,kaga bani hanya ina sauri" "Don girman Allah baba nima dankane inda hakkin baka abu ka ansa,don Allah baba ka ansa" "Shikenan nagode Allah yayi Albarka" Ahaka suka rabu ya wuce gidan dady yana satar kallon gidansu fiyah,har ya kasa hkr ya kirata lokacin ma tanata shirin fita don shadaya suke shiga. "Gani kofar gida nazo nakaiki makarantar" Xaro ido tai har yesmin na kallonta. "Innalillahi kayiwa girman lillahi katai babu ruwana wlh idan baba ya ganka" Dariya yayi yana bala,in son yaga ta tsorara kyautake. "Mataoraciya to ai har baban ma mun gaisa dashi yanzu" "Jana kake yanxun haka ma kana kan gado" Wata dariyar yayi yace"I'm serious ki leko inanan unguwar dady nazo wajensa yana nemana" Ajiyar xuciya taja tace"bakaji wlh har naji gabana ya fadi,ina shiryawa sai anjima" Ta latse wayar don idan ta biye mashi ba lallai ta gama kan lokaci ba. Abdoul gaban dady ga kuma Abbi shima ga mami ga matar dady Umma salamatu............... Kuyi hkr don Allah nasan kuna hkr dani,ku kara kan wanda kuke ina ganin comment dinku kowa da nashi ra,ayin saidai zan baku hkr bisa ga wani abu guda.akoda yaushe marubuciya duk sanda xata dora alkalaminta don isar da wasu sakonni ga mutane,on ready ta riga ta tsara ga yadda lamuran da zasu faru,komi da kuke gani ahaka yataho,kuyi hkr idan kunga sabanin ra,ayinku haka labarin ya ke. [10/9, 5:48 PM] Mom Muhseen: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSEER* *(ALFAH)* WRITTEN BY MRS BB MOM MUHSEEN FOR SALE 300 NAIRA ONLY 09034722970 🅿️..........56 Tunda ya gama sauraren duk wadannan evidence din da zakiyya tayi sanarar dauka idonsa kamar anzuba attarugu aciki,jijiyar kansa ta fito sosai kallo daya zakai mashi kasan cewa xuciyar ta motsa. Mikewa yayi atsananin fusace zai fita dady yayi saurin rikosa yace. "Ina zaka?" Yana huci duk jikinsa rawa yake soyake kurin ya ganshi gaban umma da yaranta yayi masu dukan da zasu kasa sanin wace duniya suke. "Zanje gidan ne" Jawosa yayi ya zaunar kusa dashi yace"duk hukuncin da zaka dauka baikai wanda ubangiji ya daukar maka akanta ba,domin mariya yanzu haka tana gidan mahaukata na nan garin,hauka tuburan take wanda ko kayan jikinta bata barinsu saita fatattatakasu,tsirara take zama kaga kuwa kai bazaka iya yimata haka ba.yanzu haka ma ana shirin kaita gidan mahaukatan dake legos don tana niyar fin karfinsu anan.don haka ka godema Allah daya bayyana komi,sanan ka godema safiyya da yarinyar nan zakiyya.sun sadaukar da komin su dominka,wannan ya zama izna gareka da duk mai hankali.sannan ga mahaifinka nan kaje ka nemi yafiyarsa kuyafi juna komi ya wuce Allah ya kyauta gaba." Kuka Abdoul keyi kamar yaro karami kasa motsawa yayi saidai Abbin da kanshi yazo ya rungumeshi yana kukan shima,wata irin kewar juna ce da tsananin kaunar juna ta kamasu.........bayan tsawon shekaru sai yau Allah yayi zasu sake ganawa,sai yau Allah ya bayyana sirrin daya boye sunsha kuka sosai suna rungume dajuna ni,ima da mami ma hawayen suke. Daddy da umma salamatu banda hkr da nasiha babu abunda suke masu,hakika idan kagansu saika tausaya masu don kowa yayi kewar dan uwansa Abbi jiyake kamar ya bude kirjinsa ya saka Abdoul dinsa aciki. Kira yake"kayafe mun yarona yafemun kaddararmuce tazo ahaka,babu wani tsumi ko dubara dole hakan zata faru,nayi kewarka har bansan adadi ba,nayi kukan rashinka har idona ya kafe da hawaye.............idan kanajin kalaman Abbi kai kanka saika zubar da kwallah,Abdoul yana shashshekar kuka yace"Abbi nima ka yafemun,xuciyata awancen lokacin ta gaza yardarmun cewar kana kaunata,xuciyata ta gayaman dama neman hanyar rabuwa dani kake,tunda har alakafa mun mummunan sharri irin wannan ka yarda tabbas kadaina sona,na yi iya yadda zanyi na koyama kaina tsanarka don ko sunanka bana son malik ya anbata mun,nayi rayuwa irinta dabbobi nayi abubuwa da basu dace dani ba,naso mutuwa lokuta dadama.nida kaina nake neman ta ninake kai kaina inda za,a bankeni.idan nai makaina rauni bana yarda naje asibiti don su dubani,malik yasha wuyata nayi masa abunda idan da wani dan uwana ne bazai iya zaman da malik yayi dani ba,Abbi nayi rayuwa cike da wahala kullum cikin kunci da bakar xuciya nake.xuwan safiyya rayuwata shine ya fara canzani,tasha wuyata ba yar karama ba idan na kamata kamar kato haka zan daketa,bana jin ko digon tausayinta.saboda lokacin babu wadda na tsana alokacin irin mace,bana kaunar ganinta idan har ta kusanto inda nake jinake tsaf zan kasheta..........nasha giya har babu adadi,kayan maye babu kalar wadanda ban sha ba,kafin malik da safiyya suyi nasara akaina.Abbi yanzu haka ina da illar da giya taimun,tayimun illar da bana tunanin zan warke,tamun tabo acikina wanda bazan iya shan ruwan zafi ba,haka bazan iya shan na sanyi ba.inko har nasha to gani can raina ahannun Allah.........rufe mashi baki Abbi yayi yana kwalla "Ya isa haka ya isa Abdoul hakika na zama uba marar anfani,amman kayi hkr ba
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101