Chapter 21
Chapter 21
El-ladan." Colin tabbatar wa tace"eh Daddy shine tun jiya yana wajensu anyi anyi su sakesa sunk'iya kuma sunk'i fadar abuda yafaru,jiya bamu samu isashshen bacciba." Jinjina kai daddy yakeyi cike da gamsuwa da kuma jimamin abun.........yace"am ya sunan ki diyata,cikin ladabi tafada masa ya ciga ba da cewa "sofiyya wannan lamarin tsohuwar gabace tsakanin mahaifinki da yayana wato Alh muazzam.zan iyacewa tun kafin a haifeku wannan gabar take,kuma har gobe yaya yana kan tsanar babanki saboda wani dalilinsa marar tushe.amman yanzu tunda dai naji haka zanyi kokarin ganin koyau ko gobe babanki ya fito,zanje na bibiyi yaya naji ko babanki ya aikata mashi wani abun,inhar bashida laifi sofiyya insha Allah babanki zai dawo gida cikin k'oshin lafiya." Godiya taringa yimasa harda kwalarta cikin tausayawa yace"kibar kuka,kinjiko ai babanki abun ataimaka masa ne don kuwa mutumen kirkine,nima ai a unguwar taku nake nasanshi yasanni tun shekarun da suka wuce,duk unguwar nan nake gaya maki kowa yasan sa da mutunci ya iya rik'e mutuncinsa,kasancewarsa mutun shidaya talaka marar karfi hakan baisa ya wulakanta kansa ba,baita zuwa kofar gidan wani wai maulaba ko bara.aa bayayi taye yake iyakar karfinsa yake hidimta ma gidansa,wannan dab'iar ce taja masa bak'in jini cikin unguwar,don su ganinsu tunda baida shi dole yazo ya durkusa masu yana masu maula su bashi awulakance yana masu godiya,shikuma yak'i hakan shiyasa kowa yakejin haushinsa baya sonsa amman hakan baisa ya yi abunda suke so ba,nai maki alkawarin malam kabir zaidawo gida kinjiko diyata,ai babanki nawane zanyi iyakar kokarina kuje Abdoulmalik,ka kara bata baki kajiko.anshi wannan ki kaiwa maman ki kice inji Alh mawalle." Kudine ya bata rafar yan dubu guda daya hawaye take sharewa tana girgiza kai tace"aa daddy fad'a zatayi mun yaya jalal kuma zai dakeni." Jinjina kai yayi yace"Allah yayi maki albarka zanzo gidan da kaina karki sanar danita kinzo nan." Har bakin mota ya rakasu saida fiyah tashiga sannan malik ya kewa daddy bayanin kokarin fiyah akan Alfah,kuma za,adace insha Allah shikanshi daddy yaji dadin bayanin yace mashi"to don Allah malik ku rik'e amana karka bari wani abu ya sameta,tunda iyayenta babu wanda yasani,muddin sukaji babanta ko kofar gida bazai barta tasake fita ba,ya gwammace tabar zuwa makarantar,don haka kazama mai kulawa Allah yabada sa,a still har yanzu inkuna bukatar taimakona kuna iya nemana zanyi iyakar yina akanku." Ahaka sukai sallama malik yatada motar suka fita. Nasiha yake mata dabkalami mai dadi da kwantar da hankali,yana sakowa da tsokana da ban dariya har yasamu ta sake yace"gida zan kaiki ko makaranta." Cikin sanyin murya tace"ban gama lectures ba school zaka kaini." Tafiyar so silent har suka isa makarantar,yace"mubar komi sai baba ya samu fitowa fiyah,don munfi samun natsuwa." Tana cikin motar bata kai ga fitowa ba tace"inason information akan zakiya da inda zan sameta,karka damu yaya malik hankalina ya kwanta daba yanin Daddy zamu iya cigaba da kokarin mu kafin lokaci ya kure mana zan shiga aji kamun sending komi ta waya,ngd sosai ka isa gida lfya........harta saka kafarta guda waje yace"bakiji ba." Juyowa tayi ya sakar mata lallausan murmushi mai sanyaya xuciya,gabanta yafad'i tayi saurin ficewa tana rufe k'ofar.ko waigowa bata yi ba har saida taji yabar wajen ajiyar xuciya tayi ta shige aji. Bayan sunfito wajen karfe hudu harda rabi feea ta rugo ta rik'e hijab din fiyah tace"washh Allahna naka maki,kinban wuya yau wlh kinga irin neman da nayi maki makarantar nan,ina kika shiga haka." Ajiyar xuciya fiyah tayi tana cewa"sakeni tundaba sata nai maki ba." Dariya tayi tace"waceni nace kinman sata kawai dai inada magana dake,mushiga mota ko mu gama tattaunawar sanan mutai." Kallonta take cike da tuhuma kafin tace"wlh nagaji gida nakeson naje mezai hana mubari idan munje gida saiki tambayi mominki kizo gidanmu." Jinjina kai tayi tace "shikenan muje to yau bazan bari kihau tax ba." Murmushi fiyah tayi tana wucewa gaba kawai hakanan taji tun batasan me feea zata gaya mata ba taji kirjinta yan bugawa,har sukaje gida daker take maida ma feea ansar labarin datake bata. Mrs bb ce. Mom muhseen. [9/17, 3:37 PM] Fauziya Madaki: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSER* *(ALFAH)* WRITING BY. MRS BB MOM MUHSEEN. WATTPAD NAME HUMAIRA7531. *DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB AND ALFAH FANS* 🅿️.........18. Parking tayi wajen da suka saba ajiye motar suka fito kowace rataye da jikarta,fuskar fiyah tayi fresh bata saka komi ba yau bayan cream din da take shafa wa,saboda duk bata cikin sukuni. Class din babu kowa na su fiyah sai wani namiji daketa karatu shikadai,sallama tayi mashi tace"ina y'an ajinne." Yace"ashe tunjiya malamin yakira classrame yafada masa bazai xo ba ya samar da mu,to mafarin kenan duk wasu basu shigo ba sai anjima." Jinjina kai tayi tafita feea ta hango tana nufo department dinsu,ajiya tana ta d'okin jin abunda feea zata gaya mata,amman ayau saita samu kanta da rashin son jin koma miye takeson sanar da ita,don kawai taji aranta abun azai mata wani dadi ba. "Kuma babu kowa ajinko?inajin sun canza time din lecture din muje can muzauna." Cewar rafeatu fiyah bata mata musu ba ta jera da ita suka nufi wani block suka zauna,shiru shiru babu mai cewa komi fea tace "niban tambayeki ba,daman kinyi waya baki gaya man ba." Murmushi fiyah tayi ta mik'a mata wayar cikin sanyin murya tace"kinganta uncle yahya ne ya siyamun bata wuce 2 week ba fah." Jinjina kai feea tayi tace"tayi kyau wlh,Kingode." Daga haka suka sake daukar wani shirun,fiyah nata nazartar ta ta lura akwai magana bakinta,amman tana shayin fada kokuma don bata san ansar da za,abata bane.kawar da shirun fiyah tayi da cewa"ina maganar da mukai dake zaki sanar dani." Ajiyar xuciya feea tayi tana kallon fiyah dandanan fuskarta ta canza,ta koma kalar tausayi cikin rauni tace. "Fiyah,banda wata qawa data wuce mun ke wadda zamuyi magana mu kashe murufe tare,kece kadai zan ita sanar da damuwata kiban shawara kuma kitai makeni batare da wani yaji ba." Kirjin fiyah yabuga tace"inajinki Allah yasa lafiya.?" Girgiza kai tayi idonta ya cicciko da ruwa take cewa" *SOFIYYAH*,Ina cikin damuwa wlh na farko dai abunda yafi tada man hankali shine Abbana zaiyi aure kuma yarinyar da zai aura class mate d'ina ce,wallahi munyi primary da secondary duk tare,kuma d same class.sannan wlh bata da kunya ta raina kowa idan Abba yayi haka munshiga uku,momi zuciyarta bugawa zatai duk tsawon shekarun nan baitashi auren ba sai yanxu kuma yarinya karama diyar cikinsa,saar diyarsa wlh tunda aka fara maganar momi bata da kwanciyar hankali kullin tana cikin damuwa hat jininta yahau.tace ita ba auren take mawa ba wlh ya aure koma wacece amman banda sa,ar yarta yaje ya nemo babba wadda zata iya zaman kishi da ita ba diyar cikinta ba.amman Abba yaruntse ido yace bazai fasa ba duk ubanda yaji bazai iya zama da shiba yafita.in takaice maki jiya nakoma gida momi ta tafi zaria gidansu." Hawaye suka zubo mata tana sharewa cikin kuka ta cigaba da cewa, "Bayan wannan sai abunda ya hana xuciyata samun natsuwa,bana bacci mai dadi banda wani aiki sai tunani,zuciyata banda azalzalara da take babu abunda takeyi,har ciwo take mun wlh safiyyah bana iya cin abinci saboda halin da nake ciki." Cikin tausayawa take kallonta har idonta ya cika tab da kwallah tace mata"menene kuma bayan matsalar su Abba. Share kwallar tayi ta d'ago tana kallon fiyah cikin karyewar murya tace
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101