Chapter 86
Chapter 86
ciwonsa na cikin ciki ya warke tas cikin kwana ashirin da dayan da aketa mashi treatment,xuciyarma kuma alhamdulillah bugunta ya daidaita don har yana farkawa yaci dan wani abu yasha magani,amman baya tankawa kowa maganarsa bata wuce eh,aa,yawwa ko idan zai gaida mami dasu Abbi zaice ina kwana atambayesa ya jikin zaice da sauki shikenan. Malik ne kurin yake dan mashi hira yana tankawa shima idan yagaji yayi mashi banza. Wani sabon miskilancine ya tsiro dashi aduk sanda yake sauraren maganar ta jiyake xuciyarsa tana kuna,har wata sa,in jikin ya rikice sai anmashi allurar bacci..........saida mami ta tusashi gaba da kuka tana ya sassautawa kanshi yaji tausayin kanshi da nasu,komi zaifaru yariga yafaru idan anhanashi safiyya bayana nufin karshen rayuwarsa ne yazo ba,akwai mata da dama Allah zai cire maka ita inhar ita din babu alkairin tare da ita,fada take mashi sosai har tasamu ya xubda kwalla ranar yini yayi baice komi ba,bayan kwana biyu kafin asallamesu dady da Abbi suka tai Nigeria saboda wani aiki daya taso anbar malik da su mami da ni,ima da zakiyya dai bayan sati biyu idan an basu sallama zasu dawo tare alokacin ne kuma Abdoul ya fara saukowa yana sakin jiki da yan uwansa zasuyi fira harda dariya shidai iyakarsa murmushi,ahakan ma sunajin dadi son da ai bama aiyin firar dashi. Yau shi kadaine su mami basu kai ga zuwa ba don gidan Abbi dake nan kasar suke zaune malik ne yake kwana dashi,idan safiya tai yaje gida yayi wanka yayo break. Xakiyya ce ta shigo da kwandon kalacinsa fuskarta da fara,a ganinsa zaune yana kallon tv dake cikin dakin nashi. Murmushin shima yayi mata ta ajiye kwandon bisa wani table tana dauko brush din sa ta matsa mashi maclean tace"yaya ina kwana" Muryarsa ta canza sosai tayi sanyi dakaji zaka san cewar yasha jinya. "Lafiya lau kiyya,yau manta wa dani kukai har shadaya saura babu wanda yazo" Murmushi tayi tace"wlh makara mukai yau,nice ma wai nai saurin fitowa sabida break dinka kayi hkr" "Yazanyi daku"ya mika hannu ta bashi brush din yafara kokarin saukowa hannunta ta bashi ya kaa saan ya sauko yana cewa"thank you" Murmushi tai tana bude mashi kofar bayin yashiga ta shiga tattara dakin tana gyara mashi gadin,duk dadai tun safe masu gyaran dakunan marasa lafiya suke shigowa su share. Freshner ta fesa dakin ya kama kamshi komi yayi lafiya lau sannan ta zuba mashi break din ta ajiye kafin ya fito. Kallon dakin yayi yajin jina kai kullum ita ke gayara mashi dakin yayita kamshi alamar jinjina yayi mata yace"kina kokari gaskiya da alama gidanku bazai kasance a datti ba ina taya abokina murna" Hararar wasa tai mashi tana juyar dakai tana murmushi. "Nidai bana so wlh" Zaro ido yayi yana zama kasa inda ta shimfida mashi darduma yace"abokin naune bakiso kome?" Itama zaro idontai tana rufe baki "nabani ni wlh ban ce ba karka jamun" Dariyar da yajima baiba yau yayi yana kallonta ita kuma ta boye fuskarta tana juya baya. Aransa yaji dadi da hakan ta faru,tabbas yasan duk wadda tasamu malik matsayin miji ta gama morewa,don shima gwanine wajen jawo hankalin mace akanshi,ya tabbata kokarinsa ne tasa har zakiyya take saurarensa kuma da alama tayi na,am da malik din. Shine ya shi go da fara,a yana kallon Abdoul din "alhamdulillah jiki yayi kyau wlh daman nagaji da zaman kasarnan haka gara katashi komunje muji inda tamu maganar ta kwana ko yakikace"yafada yana kallon zakiyya jitake kamar zata nitse awajen tsananin kunyarsu takeji mikewa tai zata fice Ya tare kofar yana leken fuskarta Abdoul murmushi yake masu yana break dinsa. "Ina zaki daga nayi magana shikenan tunda kunya kikeji na daina zoki zauna abunki,inkikatai ina zan iya zaman gadin wannan miskilin mutumen" Dawowa tai ta zauna suka cigaba da hirar su gwanin sha,awa. Har sadda su mami suka karaso. ************** *nigeria* Biki ya kankama don komi anriga da angama yiwa amaren,tundaga kan wani gyara da tsumi iyayen nasu sunyi bakin kokarinsu wajen yin hakan,idan kagansu zaka dauka cikin inji aka sasu aka wanke tass........damuwar da fiyah ke ciki itace ta shafi yesmin,duk yadda take murnar zata kasance da burin ranta idan ta tuna da cewar Addarta bata sanma mijin ba,saidai yakan kirata awaya shima bata taba dauka ba.kuma baya fushi zai sake kira saidai yesmin din ta dauka matsayin fiyar suyi firar ta kashe,tunda ance baya kasar sai karshen shekara yake xuwa amman yanzu da an daura auren zatabi jirgi ta sameshi can. Kwance take tana ta kallon no dinsa duk wasu moments dinsu dashi wanda tundaga kan haduwarsu ta farko da karshen haduwarsu saita fashe da kuka,kukan da tunda akafara hidimar bikin batai ba,don xuciyarta ta dunkule ta dake wanda takejin bata jin akwai abunda zai sake sata kuka ashe fadane kurin tai,haka taita kukan har yesmin ta shigo. "Haba Addata kiyiwa girman Allah kiyi hkr baki isa ki canza kaddararki ba,abunda Allah ya hukunta dole zaki ansheshi hannu bibbiyu,tabbas akwai ciwo akwai tashin hankali amman bamusan dalikin dayasa haka ta faru ba,kidauka Allah sonki yake dahar ya maki musaya da wani kila shine mafi alkairinki........."rungumeta tai tana cewa"yesmin nasani nasan dahaka amman taya zan cire shi daga cikin raina,yesmin yya Abdoul yayi reshe acikin xuciyata har ya fitar da tsiro,duk iyakar kokarina abun ya faskareni,yazanyi haka zanje gidan wani ina fama da wani cikin raina,ina jintsoron Allah ya kamani da wannan laifin" Kukan suke tare mama na baking kofa tanajinsu bata san sadda hawaye suka silalo mata ba,hakika Safiyya na cikin halin damuwa,kuma bata da yadda zatai da damuwar tata zata dai roka mata Allah yasa mata hkr da dangana. Yesmin har anje anmata jerenta unguwarsu Anty jamila,fiyah kuma kudin kayan dakinta baba ya danka mata ga hannunta yace tunda baza,a iya daukar kaya har kasar waje ba yaga bari yabata kudin tayi sana,a idan har mijin yabari acan ma saita karasa karatunta. Rungume baban tai tana kuka yana lallashinta tare daa mata albarka,nasiha yayi masu sosai don yasan ba lallai ya samu amar yi masu ba na da kwaa uku da yarage daurin aure. Dole fihay ta saka danaa dataga dai dagaske auren nan yinsa za,ai taroki allah yasa hakan shine alkairinsu ita dashi,shima allah ya bashi lafiya yakuma samashi juriya da dangana. Ta saduda kodan nasihar da baba yayi mata da kuma wacce yan hwanta suke mata,mama kam kullun ne saita bata baki tana bata labarin irin wadanda akaima aure irin nata da irin nasarar dasuka samu. Baba da Abbin Abdoul sun sasanta don har gaisawa suke yake mashi allah yasa alkairi,ai baisan biki za,ai gidan ba tunda shima baya zaune nan dai har ybashi gudun mawa mai yawa gaske haka dady ma. Tun dawowarsu Abbi yasa aka shiga hidimar gyaran gidanshi ba kama hannun yaro,don rana guda zai aurar da yara uku Amina da zuwairat da haulat.khadija yabarta said ni,ima ta samu miji sai ahadasu. Komi da komi aka canza ma gidan idan ka shigo unguwar bazaka gane shine ba. Sati biyu kacal aka dauka ana gyaran don komi yayi lafiya lau bazata yakeson yiwa su mami idan suka dawo duk da babu ranar dawowar bikin ma duk baifi saura wata guda ba. *Rana bata karya aidai uwar diya taji kunya* ππππina tay Abdoul kishi tsakani a Allah mom banji di
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101