Chapter 80
Chapter 80
laifina bane mariya ta cuceni Allah ya isa tsakanina da ita ..........ka gaya mun duk abunda kake Abdoul komiye zan yimaka shi inhar bai take sharia ba,zan dawo maka uba fiye da wancen lokacin" Ajiyar xuciya Abdoul yake yana kallon mahaifin nashi yace"Abbi safiyya nakeso,inason kaida dady kuje ga babansu kurukarmun shi ya bani aurenta,inasonta inajinta kamar raina idan ban sameta ni kaina bansan halin da zan shiga ba." "Inhar don wannan ne insha Allah nida dadyn ka zamuyi iyakar kokarinmu muga mun samomaka ita,nima zanyi alfahari da ita matsayin sirikata.zan iya yinkomi don farin cikinka wanda bai take sharia ba,don haka Malam kabir ko cewa yayi na kwanta ya takani zanyi,don kuwa nasan nayi mashi abunda zai bukaci hakan" Daddy ne yace"bama zai ce ba saidai wani abun na daban,to ita zakiyya fa Abdoul,kasan da cewar har gobe kai take so" Sadda kai yayi yace"dady na sani amman tayi hkr bazan iya zabarta akan safiyya ba,zanmata addua Allah yabata wanda yafini".............ko bai bata wanda ya fika ba zaibata wani wanda xai jibanci lamurranta,wanda zai share mata kukanta wanda zai taushi xuciyarta akan rashinka datai,ni zan aureta inhar taba dama " Daga bayansu sukaji wannan maganar,baki dayan su suka juya suna bin kofar shigowa da kallo,malik ne tsaye da zakiyya wadda idonta tuni ya gama lalacewa da kuka,da alamu taji abunda Abdoul ya fada. Daddy ne yace"malik dagaske kake" Riko hannun zakiyya yayi yajawora har cikin falon ya zaunar da ita gaban mami yace"dagaske nake Dady domin zakiyya mutuniyar kirkice,kuma inhar na sameta nasan nayi mata,saidai idan itace tace batayi dani" Zakiyya jikin mami ta fada tana idasa kukanta Abbi yace"malik Allah yayi maka Albarka Allah yabaka abunda kake nema duniya da lahira,hakika kayi mana komi ka zama fitila agaremu Allah ya saka maka da mafifcin Alkairinsa." Yana murmushi yace "Ameen Abbi nagode,maganar zakiyya fa anbani?" Yafada yana sosa kai yana kallonta tana kuka jikin mami, Duk saida suka mashi dariya Abdoul dai mamakin malik din yake,daman yana sonta kokuwa yanzu dayaji cewar ya fasa zaimaye gurbinsa aranta. Mami tace"kubar mun diyata ta huce tukun,kubamu lokaci zakuji daga garemu kuma kai ta nuna Abdoul saika bayarda toshiyar baki,tunda kakimu don gidanki" Sadda kai yayi yana murmushi,kunyar zakiyyar ma yakeji sosai amman ya ya iya da azalzalar da soyayyar fiyah kemashi.zai samu time ya lallasheta yasan zata huce. Abbi ya shafa kanshi yace"yanzu ina zaka son" Cikin wata irin kauna Abbin ya fadi shima ya shagwabe yana kwantawa jikin Abbin yace"office zanje in idaza ayyuka" "Okay yaushe zaka dawo gida to" Kalon malik yayi yana mashi alamar tambaya yaushe zai dawo. Dari ya umma salamatu da dady sukai mashi shima malik din yana tayasu yace"ka tmbayeni yallabai" "Shikenan xuwa dare daka tashi nan nakeson na ganka gida kajiko,kafinma ka dawo ankwaso maku kayanku tass za,a ajiye maku ana.amman abubuwan anfani kurim za,a dauko.kayan cikin gidan da gidan kanshi zanyi kyauta dashi.oky" Jinjina kai Abdoul yayi yace"duk yadda kayi Abbi daidai ne," "Allah yayi maku albarka,kaje karka bata lokaci idan kadawo zamu sake tattaunawa." Kowa kallonsu yake cikin jin dadi don ba tun yanzu wannan kaunar take ba,Allah ne dai ya kaddara sai haka tafaru. Rungume Abbin yayi yana mashi kiss ga kunci yaje ya rungumi dady yana murmushi"nagode dady,thank you very much kayi kokari" Wajen mami yaje itama ya rungumesu tare da ni,ima yana jin kewarsu sosai kallon zakiyya yayi wadda ta kauda kai bata son ganinsa. Itama kissing goshinta yayi yace"thank you for everything kiyi hkr zamuyi magaa daga baya" Tunkudeshi tai malik yana cewa"malam ya haka zaka wani shigema matata agabana,dalla wuce" Tashi yayi guiwarsa tai sanyi yana masu saiya dawo. *********** Yesmin ce keta kokarin hada sanwar dare sun hira da mama tana aikinta. Shinkafa da miya zatai mamar ke yanka mata salad ita kuma tana soya miya don har ta kwashe shinkafar,dalhane yayi sallama. "Aaha dalha ka dawo kenan" Cewar mama "eh na dawi ko shagon ma ban budeba saiga muhsen yatsaya,yace in turo mashi yesmin." Rudewar datai jin ance muhseen yana kiranta yasa ta yadda ludayin juya miyar tana zare ido,nashiga ukuna dawane idon zan kallai.daman kullum xullumin haduwarsu take. "Yesmin miye haka?" Muryarta tana rawa tace"ba komi mama faduwa yayi" Murmushi dalha yayi yace"ya za,ace mashi mama" Itama murmushin tai tace"kace tana xuwa yanxu" Ya fita don sanar dashi Mamar tashiga kitchen din ta ganta durkushe ta buga tagumi. "Tashi like ki gyara jikinki ki fita yana jiranki" Idonta yayi kwal kwal zatai kuka. "Mama nidai don Allah" "Banson shirme cinyeki zai ne kokuwa bakonki ne yau kuma,tashi karki bata mun rai." Haka ta fito ta wuce daki kaya ta canza duk da basu jima jikinta ba,amma akwai kaurin girki. Hijab tasaka kalar kayan data saka,ta fesa turare ta kalli kanta ga mirrow murmushi tai tana jin kunyar haduwar su,bata san dawane idon zata kallai ba. Muryar mama tajiyo tana cewa"halan sai yayi tsiru a kofar gidan sannan zaki fita." Dariya tai jin abunda mamar tace saida ta ga komi lafiya lau sannan ta fita. Mama na mata dariya kunya kamar ta nitsar da yesmin. Yana cikin motar amman kofar gefensa abude take yasha gayunsa don daman muhseen badai iya gayu ba. Hangota yayi yadda take ta sunkuyar da kai,murmushi yayi lallai yana da aiki waccen kunyar kwarar sa zatai,yana son ta saki jiki yadda zasu saba shima har yafara jin kaunar tata. Bude kofar wajen mai zaman banza yayi yana cewa"bismillah princess" Kasa ansawa tai yabar kofar bude tadan zauna adosane. Cikin natsuwa tace"yaya muhseen ina wuni" Kallonta yake sai kauda kai take. "Bazan ansa ba gaskiya tunda ma ko kallona baza xa ai ba yafada cikin muryar shagwaba kamar yaro. Kasa kasa tai dariya kafin tace"kayi hkr yaya muhseen kunya nakeji" "Yau kuma akejin kunyar tawa,to menayi har akejin kunyata" Kasa ansawa tai tana wasa da yatsunta. "Shikenan tunda bazaki fada ba,ya kike to yasu mama da baba" Ahankali cikin natsuwa take anashi,har lokacin ta kasa kallonsa. "Yesmin" Yakirata cikin lumana don yana son ta bashi hankalinta. "Na,am" "Kallona nakeson kiyi" Ahankali ta kalleshi ta sunkuyar dakai murmushi yayi yace"nasan kinsan komi daya faruko?" Daga kai tayi"ba daga kai ba kimun magana nafison inajin muryarki" Ahankali tace"eh yaya muhseen nasani" "Yawwa fatan zaki ansheni hannu biyu kuma zaki bani dama na baje kolin tawa baiwar ta soyayya,bazan so kin dari dari dani ba, ban kuma ce kibar jin kunya ta ba aa kunya abune mai kyau ga diya mace,amman ki daukar kamar yaya jalal ki saki jiki kina mun fira kamar sanda muke abaya,zanso ace munyi rayuwa mai kyau da fahimtar juna.har mukai ga inda muke fata oky" "Insha Allah Zan kokarta" "Yawwa kokefa princess yau ranar gabatar da kai ce ba dogon surutu don haka anshi wannan" Ya miko mata wata keda fashion harda dai kwalin waya aciki. "Banson jin aa anshi kurin tunda dai na kusan zama miji ko ba haka ba" Murmushi tai ta ansa cikin ladabi. "Nagode yaya muhseen Allah ya kara budi" Yaji dadin adduarta yace"thank you so much princess,kije gida magaruba ta gabato kisata caji anjima zamufara zance" Dariya tai tana fitowa tace"ka gaida hajiya da jawaheer" "Aikuwa kamar kinfada akunen su" Sallama sukai ta shiga gida tana sauke ajiyar xuciya. *********** Fiya basu fito exam ba
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101