Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 68

Chapter 68

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,284 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

jeka ga waye,karka barkowaye mamman,kakira abokan aikinka kowaye bance ko ragar masa ba muddin asirin mu yatonu kaikanka bazan kyaleka ba." Dagudu ya fita daga dakin........daidai karewar video kenan. Malik kansa akasa yana jin kofafin kansa suna toshewa,wace irin macece ita metake nema ta rasa cikin wannan gidan,wace irin hatsabibiya ce ita harta ke iya aikata irin wadanan abubuwan..........tunawa yayi da irin bakar rayuwar da Alfah yayi,da irin yadda ta bata mashi suna,duk mutanen dake ganinsa da kima da mutunci sun daina,ana mashi kallon dan iska wanda yarasa wadda zai nema sai matar ubansa,yadda rayuwarsa tashiga hadari baisan sanda kuka ya kubce mashi ba mai sauti,wanda rabon dayayi wannan kukan tun sadda yarasa gatan iyaye da danginsa,tunda kuma Abdoul-nasser alfah yashigo rayuwarsa duk wani kuka da kunci yayaye mashi,haske da farin ciki ya maye gurbin bakin cikinsa,amman kwatsam rayuwa tazo ta juya masu baya wannan la,anannar mata tajefa mashi abokinsa amininsa dan uwansa wanda yakejin bayada kamarsa ahalin yanxu,idan baiyyi kuka ba mezaiyyi.........lallashinsa dady yake wanda shima yaji kwallar sa tana cika idonsa. "Karka sare dana,duk wani tsanani yanada sauki,kuma kadauka daman kaddararkuce tazo ta hannunta,hakika hajiya mariya babu shaidaniya irinta,kuma ta daukowa kanfa babban bala,i don nayi alkawari kozan karar dakomi nawa sainaga na sadata da gidanzaman ta na har abada." Haka malik yayita kuka dady yana lallashinsa,daker yayi shiru yace yaje gida zai san yadda yayi yanemi ganin Abbi. Haka malik yafito jikinsa amugun mace daker ma yake jan motar,gabaki daya tsoron duniya da rudin shaidan yashigeshi,mutane suna kai kansu halaka saboda son duniya da abun da ke cikinta. Har yaje gida bai iya dawo wa daidai ba,ayadda ya hango dakin Abdoul idonsa biyu,agogo ya kalla shabiyu da minty goma. Kome yake bai bacci ba da alama dai akwai damuwar data hanashi runtsewa,kallon bedroom din da zakiyya take kwana yayi shima akwai haske,itama batai bacci ba,to meke damun su suduka haka. Baida natsuwar dazai fuskanci koguda acikinsu shiyasa ya wuce shima yayi wanka da sallar isha,i yasha ruwan tea ya kwanta yana sakawa yana kwancewa. 💞💞💞💞💞 Fiyah ce zaune gaban baba tayi shirin fita exam don yau suna da peper. Tare ma suke karya wa mama dan wake tai masu sanan aka dama kunun gyada,suna ci suna hira gwanin sha,awa yesmin na gefe itama ida mama kwanon su guda. Ganin yadda fiyah ta sake take ta annashuwa hakan yayiwa baba dadi,yaga damace daya kamata yayi anfani da ita wajen yi mata zamcen yaron nan muhseen. Cikin jan hankali da natsuwa baban yace"uwata wannan jarabawar itace ta karshen gama aji daya ko?" Tana kurbar kunan gyadar tace"eh baba itace,amman sai munje hutu munkoma mun sake wani karatun munyi wata jarabawar sannan mushiga aji biyu" Jinjina kai yayi yace"masha Allah kinga daman burina biyune akanku kullum keda yesmin," Kallonsa tai tace"baba wane irin buri kake dashi akanmu" Murmushi yayi yace"inason inga kun fadada iliminku bayan na secondary,inga kuma daidai gwargwado ban tauyeku ba kuma kun samu ilimin da zai taimakeku agobenku,bayan nan uwata kullum fata nake da burin Allah ya fiddo maku da mazajenku nagari wadanda zasu rikemun ku cikin amana da mutunci kamar dai yadda uncle dinku hake rike da antynku cikin kwanciyar hankali babu maijin kansu" Gabanta yafadi sosai har ta kasa kai dan waken dake hannunta cikin bakinta tace"baba ai banfa gama karatunba,duk fa ko rabi banba akwai aiki gabanmu sosai" Murmushin yayi yace"ai uwata shi aure baya hana karatu,haka karatu baya hana aure aduk sanda kasamu damar yin guda inhar anyarje maka saikaga kayishi cikin kwanciyar hankali," Gabaki daya ta rude dajin kalaman baba meyake nufi da ita,innalillahi Allah kasa ba wannan shegen muhseen din yazo ma baba da wata magana ba,wlh van sonsa bana sonsa.....idonta yadan caza tace"baba ai babu wanda nake kulawa tunda karatu nake in wani yazo saina gabatar dashi wajenka" Mama kallonta tai ta fahimci wani abu game da diyar tata,idan batai kuskureba tasan maganar da baban ke shirin yi mata,wanda yasa take kakkaucewa. "Ai kwantar da hankalinki uwata,Allah yana sonki don ya kawo maki miji har gida kuma wanda nake maki fatansa da kwadayinsa,badan abun hannunsa ba ko don kudin magabatansa,aa nagartarsa naduba da hankalinsa da natsuwarsa yasa banyi shawara dake ba nai na,am da maganarsa don haka kowane lokaci zaki iya ganinsa yazo wajenki." Bata son fiddo kwallarta gabasan yasa ta sadda kai tana kokowa da kwallar cikin kermar murya tace"waye baba,ni banda wani wanda nakeso kuma ban turo kowa ba wlh" Duk yadda taso karya gane rudewarta saida ya gane yace"kwantar da hankalinki ki natsu uwata,muhseen ne kanen uncle dinku.kema kinsan bashida wata matsala karkiyo tunanin komi,cancanta ce yasa nabashi ke kuma inada yakinin zai kula dake yadda yakamata ahankali zaki fahimceshi kuma har kisoshi." Idan tace zatai magana kukanta bayyana zaiyyi shiru tai tana zare hannunta daga cikin kwanan dan waken,amman kafin ma tatashi yesmin ta rigata ta fice tana tari da alama kware tai. Ahankali kamar wadda kwai ya fashe wa aciki take fita daga dakin,kallon yesmin take durkushe gaban maguji tana kuskure bakinta,idan ba gizo idonta yake ba kwallace ke fita daga idonta,tana gogewa kasa kasa tsura mata ido tai harta wanke fuskarta ta shige dakinsu bata kula fiyah ba. Jinjina kai tayi tana godewa Allah data kawo mata wannan damar,don kuwa bazata iya musawa baba cewa bata son muhseen ba,amman idan ta fahimtar dasu cewar yar uwarta naso hakan zaija hankalinsu su duba maganar. Wajen dalha taje ta anshi kudin taxi tabar unguwar xuciyarta cike da abubuwa. 💞💞💞💞💞 Wayar da akaimashi can caji office yasa ya tashi don bai niyyar fita ko ina ba yau,shiryawa yayi yanayin sa kwata kwata yau ahargitse yake.neman wanda zai juyewa masifar shi yake. Har zaifita idonsa akan jikkar fiya. Dawowa yayi ya dauketa yafifa,ko kallon kitchen baiba inda yake jiyo mktsin mutun yasan zakiyya ce,don har yanzu akuke yake da ita. Driver sa dasuke fita office ne yazo yace"yallabai yau babu office ne" Cikin shan kanshi yace"eh" Juyawa yayi yabarsa don yaga kamar cikin fushi yake. Yadda ya figi motar kasan kiris yake jira,gudu yake don yaje da wuri dpo din yace mashi ga yallabai nan ya sake dawowa neman belin su. Shikuma duk bala,in da za ai da masifar da za,ai bazai bari su kubutaba yau zaifuskanceshi bayan tsawon shekaru,yadda yake nuna mashi shidin ba dansa bane shima zai rufe ido ya nuna baima taba sanin sa ba,idan ma kotu za,axaje akan maganar ashirye yake. Go slow ya tsayar dashi idonsa ya sauka kanta tana cikin taxi,kanta kasa kamar tana duba wani abu. Saurin dauko bag din yayi zaifita saikuma ya fasa,yana son ganinta akebance wannan damace da zaije gidansu anjima. Koma wa yayi yana cigaba da kallonta jiyayi duk wani kuncinsa ya na yayewa,xuciyarsa tana sauka sabanin yadda yakejin wata irin temper tana taso mashi. Kamar kar yatafi yakeji amman babu halin hakan yana gani suka wuce shi shima ya wuce inda zashi. Malik bai tashi da wuri ba sai kusan shadaya wanka yayi yafito yayi break zakiyya ta gaidashi ta shige daki,binta da kallo yayi yana mamakinta to aibashi ya kashe xomun ba. Waya sukai da dady yake tambayarsa Andoul na gida. "Wlh daddy baya nan,yafita tun safe amman bari akirasa aji," "Aa kyalesa nasan inda zaije yana station kan case din safiyyah yana can shida

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});