Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 82

Chapter 82

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,268 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

bai yarda ba fa,bacin ta xurfafa kaunarta akansa hakan zaiyyi matukar tabata,zai girgiza xuciyarta don hakika Abdoul shine farincikin ta shine burin xuciya da ruhinta,tunda ta fara tunanin kasancewa matsayin mata awajen wani namiji dashi take hango rayuwarta,bazata iya daukar kalmar rabuwa daga bakin mahaifinta ba,babu tantama xuciyarta zata iya bugawa don ita kanta tana shakkar wannan ranar..............."safiyyah" Taji muryarsa mai dauke da wasu alburusan shauki suna shigarta ta ko ina,daker ta iya dago kyawawan idanunta ta zubemasa su ga fuskarsa,lumshe mata ido yayi ya bude yana kallonta shima.cike da shauki da kauna daker ma kalaman suka fito. "I need to say something plz" Ajiye idonta tai tana sauke wata sassanyar ajiyar xuciya cikin muryarta silent ta fara magana wadda dan danan yaji ta hade mai tashoshi daker yake control din kansa yana saurarenta. "Yaya Abdoul na gode da kaunarka gareni,domin banyi tsammanin zaka iya sona ba.duba da cewar nidin ba yar kowa bace face yar talaka bawan Allah mai neman rufin asirinsa akoda yaushe,sai kazo kaban mamaki tabbas nayi farin ciki dajin kalamanka wanda da zan iya fiddo xuciyata ka gani da kasha mamaki,Amman inason ka fahimceni yaya Abdoul inajin tsoro inajin tsananin tsoron abunda zai biyo baya,babana kaifi daya ne idan yace aa to mawuyacin abune yadawo yace eh,hakika kanada wani matsayi mafi girma acikin xuciyata,kayi nasarar cinye duk wani fili dake cikinta.kuma nima zan so ace na kasance...........shiru tai saboda kunyar furta kalmar dake bakinta. Matsowa yayi sosai cike da kauna yana rage muryarsa kamar baison wani yaji yace"plzzzz ki fada inason naji,karki boye mun raina yabiya dasonjin me zaki fada plz love" Kallon kasan ido take mashi kafin ya ganta ya daga mata girarsa guda,make kafadarta tayi cikin shagwaba tace"uhm uhm ba yanxu ba" "Sai yaushe" "Sai naje gida idan munyi waya" "Shikenan nasan dai kinsan muhimmancin alkawari don haka basai na tuna maki ba,cigaba da maganarki ina saurarenki" Numfashi taja tace"yaya Abdoul babana daban ne,inajin tsoron idan kaje mashi da maganata yace maka bai yarda ba kayi hkr,wannan kalaman sune suke tsorata ni" Ta tsayar da idonta akanshi. Shima kallon nata yake cikin low voice dinsa yace"meyasa kikekin tsoro" Sadda kai tai cikin jin nauyin abunda zata fada. *"Yaya Nasser banson in rasaka shiyasa"* Cike da jin dadi yace"a u sure love?dagaske don Allah sake fada naji" Dariya ta boye tanayi shima yana tayata kafin ya lauya murya kamar da yaro yace"bacin ma banji kince mun u love me ba" Dariyar ta sake yi tace"ba yau ba sai naji daga bakin baba,kayi hkr ina hango mana abunda zai iya faruwa don haka idan kana iya wa kazo yau kawai kayi mashi maganar." "Dagaske kike inje kuma ince kekika turoni" Daga mashi kai tai cike da jin kunya murmushi yayi yace"yau din tazo mun cikin sa,a hakika ina fatan farincikin danake ciki ayau ya dawwama,ko kinsan bacin wannan dakika sani daman da kwarin guiwata nafito" "Meyafaru to" Ta tambayeshi lumshe ido yayi yana kanne mata ido guda yace"yau muka shirya da Abbina" Xaro idanunta tayi masha Allah tana bube baki cike da mamaki da dariya tace"wow wow Alhamdulillahi dagaske kake amman naji dadi wlh,kamar ma nafika jin dadin meyasa tun daxun baka sanar dani ba" Lakuce mata hanci yayi yace"haka kike kyau idan kina dariya,na gaza ganewa harara da kuka da dariya wanne yafi maki kyau duk wanda kikai sai naga yafimun kyau miye sirrin" Hararar tashi tai tana dauke kai dariya yayi"wow I love it wlh plz karamun daya" Dariya ta saka tana boyewa cikin hijab dinta,tana mamakin daman haka yake da barkwanci gaskiya ba karamin alhaki umma ta dauka ba. "Nidai ka kaini gida kaga anfara kiran salla wani wajen" "Idan da zamukai gobe anan love bazan gane ba don kuwa idan ina gabanki ba komine nake tunawa ba,kilaman idan kince mun whats ur name cewa zanyi safiyyah" Wata dariyar ya sake bata haka suka cigaba da fira yana sata dariya har saida tadage yakaita gida sannan yaja motar,yana kallon kiran malik awaya yayi buris don karya bata mashi mode dinsa. Motar muhseen na fita tasu tana shigowa,kallon motar tai tana murmushi da alama dai sun daidaita da yesmin. Kofar gidan ya tsaya yana kallonta cikin kauna kamar xai cinyeta, "Karkasa na kasa tafiya kallon yamun yawa fah" "Don Allah ki gaya mun wani abu mai dadi karki tai kibarni" Hararar so tayi mashi tace"take care of ur self" Shagwabe fuska yayi "yamin kadan nidai" Nidai budeni banson baba ya fito ya ganni cikin motar nan plzzz" "Okay say something plz" Kiss tayi ga hannunta ta hura mashi ta dauke kai tana kunshe dariyarta relax yayi cikin kujerar ya bude mata harta fita yakasa cewa komi,Allah kadai yasan yadda yakeji cikin jikinsa da xuciyarsa........saida tazo kofar shiga ta daga mai hannu by by. Daker yaja motar ya isa bakin get din gidansu,yana tuno moments da dama dasuka wuce yana tuna ranar daya bar gidan,har ya isa yayi parking motarsa. *********** "Safiyyah ya akai yau kikai dare" Inji baba dake alwallar magriba zaije masalaci. Sadda kai tayi don tana tunanin yaji saukar mota,amman bazata iya gane wa ba tace"baba jarabawar sai biyar muka fito sannan mundan tattauna da yan ajinmu kan exam din gobe,sannan na taho" Jinjina kai yayi yace"yayi wuce kije kiyi salla" Yafice masallacinsa. Jiki sanyaye ta wuce daki tana rage kayan jikinta tana adduar Allah yasa baban baiji sadda aka ajeta ba. "Adda sannu da dawowa" Murmushi tayi tace"yawwa yesmin ya gidan" "Gashinan ya exmas din,wai yaushe kuke gamawa" "Wlh exams kam sai godiyar Allah i think sai jibi zamu karkare insha Allah,ina yaya muhseen dinki" Murmushi tayi tana juya baya "daxun yazo bakinan har yaba waya da turaruka" "Uhmmm soyayya dadi Allah yasa alkairi kingode,adai kula sosai yesmin kinsan yadda xamanin yake Allah yabar kauna" Can kasa kasa taji tace"Amen Adda" Dunguremata kai tayi"makira anaso anakaiwa kasuwa" Shigewa toilet tai tabarta tana dariya. Bayan sunci abuncin dare ne baba ya kalli safiyya yace"waye ya saukeki dazun awaje" Kirjinta yabuga dan danan ta rude ta sadda kai tana murzar hannu Allah yasota ta cire xoben dazun. "Dake nake kina jina" Kwallata cika idonta tace"baba Abdoul ne" Basai yatambayi wane abdoul ba don yau iyayensa sunje har wajen aiki sun samai. "Bance maki karya sake xuwa nan ba,ina kuka hadu har daukoki kika biyosa" Jikinta yana rawa tace "anyi wuyar abun hawa yau najima bakin titi saigashi yace inshigo ganin zanyi dare shiyasa nashiga kayi hkr" Bata da zabin daya wuce haka tayi astagfirulla saboda tasan tayi karya kuma babu kyau. "Inhar ba sokike musaka kafar wando daya dake ba karna sakeji karna sake gani,nace maki haka ne don ba sa,an aurenki bane wannan shine magana,don iyayensa sunje har wajen aikina yau sun mun magiya nace aa don haka idan kina son fushina kicigaba da tsayawa dashi." Kwallarta ke xuba ga hannunta saukin ma babu nefa kuma babu haske sosai balle su gani,amman yesmin dake jikinta tana jin yadda jikinta yake rawa sai tausayin Addar tata ya kama ta har itama taji kwallartata tafito. Ahankali tatashi ta shige dakinsu kan kujera ta zauna tana kuka kasa kasa,har kirjinta dagawa yake daman wannan abun takeji shi take tsoro tasan daman baba bazai huce daga abunda Alh muazzam yayi mashi ba,don inba haka ba inhar

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});