Chapter 82
Chapter 82
bai yarda ba fa,bacin ta xurfafa kaunarta akansa hakan zaiyyi matukar tabata,zai girgiza xuciyarta don hakika Abdoul shine farincikin ta shine burin xuciya da ruhinta,tunda ta fara tunanin kasancewa matsayin mata awajen wani namiji dashi take hango rayuwarta,bazata iya daukar kalmar rabuwa daga bakin mahaifinta ba,babu tantama xuciyarta zata iya bugawa don ita kanta tana shakkar wannan ranar..............."safiyyah" Taji muryarsa mai dauke da wasu alburusan shauki suna shigarta ta ko ina,daker ta iya dago kyawawan idanunta ta zubemasa su ga fuskarsa,lumshe mata ido yayi ya bude yana kallonta shima.cike da shauki da kauna daker ma kalaman suka fito. "I need to say something plz" Ajiye idonta tai tana sauke wata sassanyar ajiyar xuciya cikin muryarta silent ta fara magana wadda dan danan yaji ta hade mai tashoshi daker yake control din kansa yana saurarenta. "Yaya Abdoul na gode da kaunarka gareni,domin banyi tsammanin zaka iya sona ba.duba da cewar nidin ba yar kowa bace face yar talaka bawan Allah mai neman rufin asirinsa akoda yaushe,sai kazo kaban mamaki tabbas nayi farin ciki dajin kalamanka wanda da zan iya fiddo xuciyata ka gani da kasha mamaki,Amman inason ka fahimceni yaya Abdoul inajin tsoro inajin tsananin tsoron abunda zai biyo baya,babana kaifi daya ne idan yace aa to mawuyacin abune yadawo yace eh,hakika kanada wani matsayi mafi girma acikin xuciyata,kayi nasarar cinye duk wani fili dake cikinta.kuma nima zan so ace na kasance...........shiru tai saboda kunyar furta kalmar dake bakinta. Matsowa yayi sosai cike da kauna yana rage muryarsa kamar baison wani yaji yace"plzzzz ki fada inason naji,karki boye mun raina yabiya dasonjin me zaki fada plz love" Kallon kasan ido take mashi kafin ya ganta ya daga mata girarsa guda,make kafadarta tayi cikin shagwaba tace"uhm uhm ba yanxu ba" "Sai yaushe" "Sai naje gida idan munyi waya" "Shikenan nasan dai kinsan muhimmancin alkawari don haka basai na tuna maki ba,cigaba da maganarki ina saurarenki" Numfashi taja tace"yaya Abdoul babana daban ne,inajin tsoron idan kaje mashi da maganata yace maka bai yarda ba kayi hkr,wannan kalaman sune suke tsorata ni" Ta tsayar da idonta akanshi. Shima kallon nata yake cikin low voice dinsa yace"meyasa kikekin tsoro" Sadda kai tai cikin jin nauyin abunda zata fada. *"Yaya Nasser banson in rasaka shiyasa"* Cike da jin dadi yace"a u sure love?dagaske don Allah sake fada naji" Dariya ta boye tanayi shima yana tayata kafin ya lauya murya kamar da yaro yace"bacin ma banji kince mun u love me ba" Dariyar ta sake yi tace"ba yau ba sai naji daga bakin baba,kayi hkr ina hango mana abunda zai iya faruwa don haka idan kana iya wa kazo yau kawai kayi mashi maganar." "Dagaske kike inje kuma ince kekika turoni" Daga mashi kai tai cike da jin kunya murmushi yayi yace"yau din tazo mun cikin sa,a hakika ina fatan farincikin danake ciki ayau ya dawwama,ko kinsan bacin wannan dakika sani daman da kwarin guiwata nafito" "Meyafaru to" Ta tambayeshi lumshe ido yayi yana kanne mata ido guda yace"yau muka shirya da Abbina" Xaro idanunta tayi masha Allah tana bube baki cike da mamaki da dariya tace"wow wow Alhamdulillahi dagaske kake amman naji dadi wlh,kamar ma nafika jin dadin meyasa tun daxun baka sanar dani ba" Lakuce mata hanci yayi yace"haka kike kyau idan kina dariya,na gaza ganewa harara da kuka da dariya wanne yafi maki kyau duk wanda kikai sai naga yafimun kyau miye sirrin" Hararar tashi tai tana dauke kai dariya yayi"wow I love it wlh plz karamun daya" Dariya ta saka tana boyewa cikin hijab dinta,tana mamakin daman haka yake da barkwanci gaskiya ba karamin alhaki umma ta dauka ba. "Nidai ka kaini gida kaga anfara kiran salla wani wajen" "Idan da zamukai gobe anan love bazan gane ba don kuwa idan ina gabanki ba komine nake tunawa ba,kilaman idan kince mun whats ur name cewa zanyi safiyyah" Wata dariyar ya sake bata haka suka cigaba da fira yana sata dariya har saida tadage yakaita gida sannan yaja motar,yana kallon kiran malik awaya yayi buris don karya bata mashi mode dinsa. Motar muhseen na fita tasu tana shigowa,kallon motar tai tana murmushi da alama dai sun daidaita da yesmin. Kofar gidan ya tsaya yana kallonta cikin kauna kamar xai cinyeta, "Karkasa na kasa tafiya kallon yamun yawa fah" "Don Allah ki gaya mun wani abu mai dadi karki tai kibarni" Hararar so tayi mashi tace"take care of ur self" Shagwabe fuska yayi "yamin kadan nidai" Nidai budeni banson baba ya fito ya ganni cikin motar nan plzzz" "Okay say something plz" Kiss tayi ga hannunta ta hura mashi ta dauke kai tana kunshe dariyarta relax yayi cikin kujerar ya bude mata harta fita yakasa cewa komi,Allah kadai yasan yadda yakeji cikin jikinsa da xuciyarsa........saida tazo kofar shiga ta daga mai hannu by by. Daker yaja motar ya isa bakin get din gidansu,yana tuno moments da dama dasuka wuce yana tuna ranar daya bar gidan,har ya isa yayi parking motarsa. *********** "Safiyyah ya akai yau kikai dare" Inji baba dake alwallar magriba zaije masalaci. Sadda kai tayi don tana tunanin yaji saukar mota,amman bazata iya gane wa ba tace"baba jarabawar sai biyar muka fito sannan mundan tattauna da yan ajinmu kan exam din gobe,sannan na taho" Jinjina kai yayi yace"yayi wuce kije kiyi salla" Yafice masallacinsa. Jiki sanyaye ta wuce daki tana rage kayan jikinta tana adduar Allah yasa baban baiji sadda aka ajeta ba. "Adda sannu da dawowa" Murmushi tayi tace"yawwa yesmin ya gidan" "Gashinan ya exmas din,wai yaushe kuke gamawa" "Wlh exams kam sai godiyar Allah i think sai jibi zamu karkare insha Allah,ina yaya muhseen dinki" Murmushi tayi tana juya baya "daxun yazo bakinan har yaba waya da turaruka" "Uhmmm soyayya dadi Allah yasa alkairi kingode,adai kula sosai yesmin kinsan yadda xamanin yake Allah yabar kauna" Can kasa kasa taji tace"Amen Adda" Dunguremata kai tayi"makira anaso anakaiwa kasuwa" Shigewa toilet tai tabarta tana dariya. Bayan sunci abuncin dare ne baba ya kalli safiyya yace"waye ya saukeki dazun awaje" Kirjinta yabuga dan danan ta rude ta sadda kai tana murzar hannu Allah yasota ta cire xoben dazun. "Dake nake kina jina" Kwallata cika idonta tace"baba Abdoul ne" Basai yatambayi wane abdoul ba don yau iyayensa sunje har wajen aiki sun samai. "Bance maki karya sake xuwa nan ba,ina kuka hadu har daukoki kika biyosa" Jikinta yana rawa tace "anyi wuyar abun hawa yau najima bakin titi saigashi yace inshigo ganin zanyi dare shiyasa nashiga kayi hkr" Bata da zabin daya wuce haka tayi astagfirulla saboda tasan tayi karya kuma babu kyau. "Inhar ba sokike musaka kafar wando daya dake ba karna sakeji karna sake gani,nace maki haka ne don ba sa,an aurenki bane wannan shine magana,don iyayensa sunje har wajen aikina yau sun mun magiya nace aa don haka idan kina son fushina kicigaba da tsayawa dashi." Kwallarta ke xuba ga hannunta saukin ma babu nefa kuma babu haske sosai balle su gani,amman yesmin dake jikinta tana jin yadda jikinta yake rawa sai tausayin Addar tata ya kama ta har itama taji kwallartata tafito. Ahankali tatashi ta shige dakinsu kan kujera ta zauna tana kuka kasa kasa,har kirjinta dagawa yake daman wannan abun takeji shi take tsoro tasan daman baba bazai huce daga abunda Alh muazzam yayi mashi ba,don inba haka ba inhar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101