Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 44

Chapter 44

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,288 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

tana ringing bata dauka hankalina yasake tashi,sako da lungu na gidan nashiga kewaye wa Allah baisa naga kofa mai irin mukullin hannuna ba,fitowa nai nayo hanyar fita naji alamun tsayawar mota jinai fitsari zai kubcemin.........wata mota da take ajiye ta lalace na kurda kasanta na kwanta gabana banda faduwa babu abunda yake,zuciyata kamar zata fito waje haka nakeji. Motace aka shigo da ita daga baya naga an fizgo mutun abayan motar idona akan kafafun mace,hankalina yasake tashi don tabbas raina yaban zakiyya ce.yadda take nishi da gurnani daji bakinta suka dade..........rawa kurin jikina yake bakamar jin danai wani yace"da alamun fa wani yashigo mu jefa shegiya can dakin muduba mugani." Dayan yace"nifa wannan yarinyar ban yarda da ita ba duk zargina tare suke" "Aa ban tunanin haka kamota mugani,shegiya zaki yi magana ne inkikaji ukuba,saikin fadi inda kika ajiye memory din nan" Wani daki dake bayana suka bude suka sata suka jawo suka rufe da kwado. Dube duben gidan kawai suke Allah bai basu sa,ar ganina ba,sannan suka fita nabada tsawon lokaci sannan nafito ina rawar sanyi duk da ba sanyin nakeji ba. Leka wa waje nayi naga basunan na koma ina b'ab'are na samu katon dutsi naringa bugun wannan kwad'on yana waigen bayana karsu dawo su saman. Nasha wuya kafin na samu nasarar balle kwadon. Shiganai dasauri itace kau kwamce daker take numfashi,cikin sauri na cire plaster da aka rufe mata baki,ashe bayan ma plaster saida suka cusa mata soso cikin bakin. Tari takamayi tana rike da wuyanta, "Tashi maza zakiyya bamuda lokaci,koda ace munyi asarar memory yazama dai ke bamuyi asararki ba,"daker tatashi muka fito janta nake daker muka fito duk arude nake,karar motar da mukaji abayan mu bayan fitowar mu daga cikin yasa ina juyawa muka hada ido da daya daga cikinsu,zakiyya tace cikin nishi "muruga fiyah yaya mamman ne karmu tsaya,idan suka kamamu bazasu barmu da rai ba." Tunkafin na idasa jin mezatace na fizgeta muka fara falfala gudu,yayinda suka rufa mana baya don insukace su shiga mota zamu bace masu. Gudu muke wanda tunda nake bantaba irin saba,zakiyya tun bata iyawa har ta zage itama damun ga sun kusa cin mana saimu sake himma...........wani gida dake bude muka fada muka labe bayan kyauren kofar,muna lekensu suna dube duben wajen. Jinake fitsari zai kucce man zakiyya durkushewa tayi kasa tana rufe bakinta,don nishi take take sosai karsujimu. Sun jima sosai wannan wurin har muka sadakar da bazasu tai ba sannan suka tafi. A gajiye suka fito suka yanki titi kamar zasu fadi kowa cikin su ya gama galabaita,zubewa sukai bakin titin suna maida numfashi. Xakiyya numfashinta sama sama yake daker tae fizgoshi,riko hannun fiya tayi daker take iya magana tace"fiy....ah.......kikira wani yazo ya taimakemu ina......buk...atar asibiti ga wannan mcard din ta ciroshi cikin breziyarta,ki adanashi....ko..namut..u foyah ki idasa wannan aikin........sumewa tayi nan wajen. Saida fiyah ta saki kara tana girgiza zakiyyar amman bata motsi,agigice take sosai. tafara tarar mota neman taimako amman babu mai tsaywa duba da yadda taimako yanzu yayi wuya,durkushewa tayi gaban zakiyyar tana kuka,kamar anzungureta tatuna da malik ta rarumo wayarta hannunta yana karkarwa ta shiga kiransa. Harta tsinke baidauka ba ta sake kira karo na biyu,nan ma haka jitake kamar zata haukace"kadauki waya yaya malik ina bumatar taimakonka" Runtse ido tai tana sake kira cikin sadakarwa saikuma taji andaga,bata bari yayi magana ba tace cikin kuka"yaya malik don Allah kataimakeni kazo ka taimake mu........kuka yaci karfinta ta kasa cigaba da maganar. Jitai ance"kina iya" Bata cikin natsuwar da zata iya tantance muryar waye amman tasan bata malik bace. Fadar inda suke tayi cikin dimaucewa da gigita,saidai shican ya kashe wayar. Kuka ta tisa zakiyya gaba tanayi idan zakiyya ta muti ya zatayi da rayuwarta. Babu jimawa taga mota tsaye inda suke saidai wanda yafito daga motar ne yasa hankalinta dawo jikinta,bakinta ne taji yafurta. *yah Abdoulnasser* kallon zakiyya tayi dake kwance kamar gawa sannan ta dago ta kallai,shikanshi wadda ke kwance kasan kusada fiyah ganin ta ya gigitashi,idonsa dan danan yayi jajawur yasha mur matuka bai sake dago kai ya kalli fiyar ba yayi kwana zaibar wajen batare da yunkurin yin wani abuba. Aguje tatashi ta bishi tana hawaye ganin dagaske koma wa zaiyyi. idan yatai yabarsu anan komi zai iya faruwa dasu wata kila zakiyya tana iya rasa ranta. Jiyai kurin ta rike hannunsa cikin rawar murya tace"karkayi haka plsss narokeka karka tai karka tai kabrmu a,inhar katai zamu iya rasa ranta bata camcanci haka ba kome katuna akanta baidace kabarmu ahaka ba......narokeka plsss yah Abdoul plssss.........ingijeni yayi na fadi agefe cikin fushi da na jima banganshi cikin sa ba yace"ina ruwana da mutuwarta ko rayuwarta,baishafan ba data mutu kotai rai karkisake zuwa inda nake balle kimun mganar wanna abar." Ya wuce kamar kububuwa yabar ni awajen.....zaman dirshen nayi ina kuka nashiga ukuna ni safiyya yau naga bala,i dagaske Alfah tafiya yayi wace irin xuciyace dashi haka,ya zanyi da zakiyya ni kau yau.nafi karfin minty talatin wajen babu wanda ya kulani kowa yazo wucewar sa yake.........kamar wasa saiga motarsa tasake dawowa wajen,inda muke lokacin naci kuka nakoshi har muryata bata fita,koda naga kiran anty kasa dauka nai namata sakon cewa naje gida amman zan dawo yanzu. Ko kallonsa banba banza nai dashi yana zuwa ya sungumeta yaje yasata baya yarufe,yayi tsaye baimun magama ba alamun intaho mutai,yadda ya bata mun rai bana jin ko kallonsa zan sake yi ahalin yanzu,tashi nai daga durkushin danake na kakkabe jikona na share fuskata na nufi tiri kurin,inajin xuciyata na zafi kamar garwashi. Madam bata lokaci kafin taxi ta tsaya nashiga nabarsa nan shida zakiyyar nasan dole zaikula da ita ko dawowar dayayi nasan xuciyarsa ce taji bazata iya barinta ta rasa rayuwarta ba bayan yana da damar kaita asibiti,can kukarata kaida ita wani abu yazo mun wuya ya tomare kuka nakeson inyi inba haka ba azai wuce ba,kukan naitayi wanda har cikin raina nakejinsa har mai taxin yana ban hkr ,ban ma sauraresa ba saida nayi na koshi sannan ya mikomun ruwa na wanke fuskata dashi bayan nafito daga taxin.na sallamai na shiga gida. Anty na ganina tace"kina lafiya fiyah?kuka kikai me akai maki" Wani kukan ya haomun nace"Anty yanzu don Allah sun kyauta mun kenan,inazowa na biyu amman suka ban na biyar wannan karon,har hakan yaja baza asani cikin musabaqa ba,wlh Allah ya isana" Dariya Antyn tayi tace"lallai safiyya har yau dai da sauranki,to waye yace maki kullum ake kwana bisa gado" ganin haka karyata ta ansu yasa nashige daki naci gaba da kukana. Don't share it plssss and plss [9/17, 3:39 PM] Fauziya Madaki: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSER* *(ALFAH)* WRITING BY. MRS BB MOM MUHSEEN. WATTPAD NAME HUMAIRA7531. *DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB AND ALFAH FANS* 🅿️.........32 Tunda na shiga daki kuka naitayi ni bazan ce ga abunda nake ma kuka ba,kawai dai nabarwa raina cewar yadda ya banzatar dani awajen bacin yaga irin halin da muke ciki,shine dayaga cewar masoyiyarsa zata zata rasa rayuwarta yadawo............saida naji kaina yafara ciwo sannan na hakura,m.card din da zakiyya tabani na ciro daga cikin aljuhun doguwar rigata na kura mashi ido,zanso jin abunda yake ciki amman ba yanzu ba sai tare da yaya malik,cikin jikkata naje nayi mashi kyakkywar ajiya sanan ta nufi bayi,don jikinta duk tsami yake mata. Gyare jikinta tayi tsaf sai kamshi take fitowa

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});