Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 58

Chapter 58

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,280 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

baban?" Bata san sanda muryarta take komawa yar karama ba tace"yana samun sauki,may be gobe musamu asallamesa" "Okay" Jin muryarta yake kamar yau yafara jinta,tundaga yatsansa na kafa yajin wani yanayi har cikin kansa,shirun itama tayi tana kwance kamar zata tsaga katifar tashige cikinta. "Ina zakiyya?" Bude idonsa yayi yabin hanyar dakinta da kallo,sai yasamu kansa cewa"gata nan kusa dani" Wani kullutune yazo mata wuya ya tsaya,duk miyan da take hadiyewa yaki wucewa,shiru tayi shikuma yasake anfani da yin shirunta yace"yana mun firane inasamu bacci,taje ta hado mun tea insha idan ta dawo zan baki saiku gaisa" Runtse idonta tai tana damkar zanen gado tare da sauke wani wahalellen nishi,mai tafe da hawaye.saurin rufe bakinta tai don ba wuya kukan na iya tahowa. "Are u on the line" Shiru tayi tana sake rufe bakinta,tana kukanta ahankali can kasa sosai. Natsuwa yayi don fahimtar yanayin ta,ahankali yakejin numfashinta yana sauka da sauri,yanayin kukanta yana shiga kunnensa. Tsikar jikinsa ce tatashi don kukan ta yatada mashi hankali ainun. Kin nuna mata yayi badan hakan baya taba shi ba,aa yana tabashi har cikin ransa amman dole zai bita ahaka badan yaso ba. *"sofiyyerh"* Ahankali cikin voice dinta data sha kuka tace"naam" Runtse ido yayi yana damke hannunsa jiyake kamar tana tafiya da numfashinsa,muryarsa silently so sweet yace"kina kuka ne" Daker tace "uh uh" "To menene?bakison zakiyya na mun firane" Ajiyar xuciya ta sauke tace"ina ruwana da hirar da take maka,meye nawa idan nace kar ta maka fira,kunfi kusa ai karka sake sani cikin batunku pls" Murmushin da bai shirya ba yayi har tana jin sautinsa yace"oky don't worry baza asake ba,hope kinyi exams lafiya" Kin bashi ansa tai tace"zanyi bacci saida safe" Lauya muryar yayi yace"oh sorry to kiyi baccin ki mana,zan so haka ma" Tsaki taja kasa kasa tace"kashe wayarka" "Kekika kirani ashe?" "Ban Sani na malam karka mun gori ai ban roki kakira ni ba balle ka raina mun hankali," Dariya tafara cinsa wadda bazaice ga lokaci. Daya yita ba. "Masifatu kurin,karki sake ki mun rashin kuya wlh har nan kan gadon naki zanzo na baki punishment,wanda nasan zai ladaftar dake." Yafada da wata irin murya hade da salo wanda nan take ya idasa kashe bakin fiyar. Shirunta dayaji yasa yayi murmushi don yasan sakon yaje,dariya yayi ta burgewa yace"matsoraciya,har kin tsorata da wuri tun kafin ma inzo,uhmm kinsan hukuncin naki ashe shiyasa kikai shiru." Ahankali kamar mai koyon magana tace"angaya maka ni Allahn musuruce dallah can saida safe karka sake kirana" "Okay Zane ringa kiranki sau uku arana,yayi maki ko" Tsaki taja tace cikin masifa"dalla cewa nai karka sake kirana" "Oh yayi maki kadan sau ukun,kenan sau biyar zan kira din." Batasan dariya ta kubce mata ba,don yadda yake juya mata magana abun ma saiya bata dariya. Shima taya ta yayi da murmushi mai tsada wanda da agabanta yake saita kusan suma don yadda zai daukar mata hankali. "Angaya maka ina bukatar kiranka?to inkakira ni mezan maka kokuma meza kaimun" Kamar yana rada yace"wai in ringa ladabtar da bakin nan naki mai rashin kunya" Babu shiri tayanke wayar don yama shirin kaita inda bata da mai maidota. Wanna dare dai xukatan mutun uku basu huta ba,zakiyya sabon son Abdoul dinne yayi mata dirar mikiya,jitake kamar yanzu ne tafara sosan bata da wani fata da burin taga sun june har takaisu ga mallakar juna,amman tasan akwai kalubale sosai don Abdoul hankalinsa baya kanta ahalin yanxu,ya zatai ta dawo da soyayuarta sabuwa cikin ransa. *SOFIYYAH* wata xuciyar ta anbata mata tabbas zata iya daidaita su har ma kilan sudawo sufi da son juna,zata nemota itace kurin hope dinta. Abdul kuwa saida yayi dagaske sannan ya samu bacci don kwata kwata xuciyarsa babu komi ciki sai shaukin son kasamcewa da wannan yarinya mai daukar hankali,gabaki daya baisan yadda zai misalta yadda yakeji ba,shidai yasan yana shan wuyar kewarta na kwana biyunnan. Haka yake ga fiya murje murje taitayi agado xuciyarta tana saka mata tana kwance mata,amman kishin zakiyya yaddane duk wani feelings dinta akanshi,hakika yadda takeji ga xuciyarta bazata iya shiga tsakaninsa da zakiyya ba,don ita masaniya gareta akan soyayyarsu.koda xuciyarta tayi kokarin ganin ta kaita inda bata dace da wajen ba,ita zata janye kanta.don bata iya daukar rebel sai goshin asuba bacci ya dauketa. Washe gari da wuri tatai school don eight sukeda exams yau sai shidda zasu dawo gida,don ko break bata tsaya ba feea na xuwa suka wuce yau da mota tafito. Mama tace idan tataso tayo gida kurin don da rana zasu sallamesa suyo gida. Malik saida yaje store yaduba yadda abubuwan suke tafiya sannan yaje company shima yarage wasu ayyukan kafin yakira dady don yaji yaushe yake zaune su idasa sauraren wannan Audio din. "Malik kabari sai dare yanzu haka ma ban garin,amman immediately dana dawo zan kiraka" "To daddy Allah yadawo dakai lafiya,ni sonake ma muzo da Abdoul yaji komi" "Aa karka zodashi yanzu bayada lafiya,tattalinsa ake idan har yaji ayanzu komi zai iya faruwa,kabari ya kara samun lafiya inso samune lokacin sun daidaita da safiyya abun zaifi sauki,duk yadda yahau zata iya sassauto dashi kagane menake nufi ko" Malik yace"hakane kuma dady shikenan Allah ya dawo dakai lafiya" Sukai sallama ya cigaba da aikinsa yana ganawa da costomers daga kasashe daban badan,kullum kamfaninsu kara cigaba yake yanzu haka yaga wasu schedule da Abdoul din ya rubuta cewar zai bude reshen kasuwancinsa can Australia,sannan zai ake fadada store dinsa zai sake hude wani wanda yafishi kayan nagartattau kuma masu kyau.amman baikai ga sanar da malik din ba shine dai yaga takardar cikin drower dinsa na adana muhimman abubuwansa. An sallami baba jikinsa alhamdulillah,yana dan taka kafar amma ba sosai ba,sun bashi yar sandar dazai ringa dogarawa har xuwa sanda zai take dakansa. Muhseen ne yazo daidai sanda zasu tafi gida,mafarin kenan ya daukesu amotarshi suka taho gida,yesmin keta mashi surutu duk da kasancewarta ba mai magama ba sosai amman saita samu kanta da yiwa muhseen din labari,har saida mama ta kwatseta sannan ta bari. Dariya muhseen din yayi yace"mama kibarta inajin dadin hirar,munada irinta gida ai ba takura man tai ba," baba yace ta kyalesu. Dole mama ta samasu ido tsayawa yayi yayi musu siyayya mai sunan siyayya,ledoji uku manya babu wanda ya damu don basusan cewar nasu bane da tun wajen baba yayi fada. Muhseen kau ya kudiri yau bazai tai ba saiyayi ma baba maganar fiyah,don yagaji da dakon kaunarta bacin ita bata shi tae a,hakan dazai mata shine zaisa dole ta kulashi ahankali tasoshi ga baya. Cefane ne leda guda sai dankalin turawa tiya uku sai naman miya na dubu biyar,sai fruits cike da wata leda ayaba ce kankana ce gwandace da abarba harda apple. Saida sukaga yana shigo dasu yesmin nataya shi sannan suka san ashe su yasiya mawa nan fa aba yayita fada yana cewa ya dauke yakai can gidansu meyaa zaiyyi dawainiya dasu har haka. Mama dai shiru tayi don ranta yabata wani abu,amman babu kyau zargi tabari maganar tafasu sannan. Anan muhseen yadade har akai sallar la,asar bayan yadawone yashiga zaima baba sallama yadurkusa yana sosa kai yace"baba zan tai ubangiji ya sa kaffarane Allah kuma ya kiyaue gaba" Sosai baban yaji dadi yaringa saka mashi albarka tare da mashi addua mai kyau,kasa tashi yayi bakinsa kuma sai yayi nauyi,

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});