Chapter 66
Chapter 66
Allah don inagani bazan bari wani ya cutuba,koda hakan yana nufin nizan cutun. Akarshe ina rokon Alfarma wajenka inhar kadaukeni da daraja arayuwarka yaya Abdoul kamance da komi,kayafe komi aranka ka hakura da duk wasu kudiri daka dauka akan abunda yafaru da rayuwarka ka auri zakiyya,sannan ka yafewa mahaifinka don shima abunne yafi karfinsa,zakaji anan gaba zakace nafada maka.yaua Abdoul Allah ma muna masa laifi mummuna kuma mutuba munemesa afuwa ya kuma yafe mana,saimune tsakanin mu kuskure zai gifta ace bazamu iya yafewa junan mu ba,idan ba,a yafiya taya ubangiji kai zaiyafe maka. Nidai inhar inada kima inda muhimmanci arayuwarka inhar inada alfarma wajenka.........muryarta ta karye sosai rawa take domin abunda take furta wa yana cutar da ita cikin ranta,amman dole hakan zatai don zakiyya tafita bukatar Abdoul tunda har tana kirarin wani yamutu saboda kishinsa. Jiyowa yayi gabaki dayansa yana zuba mata rinannun idonsa,yayinda idanunsu suka nitsa cikin najuna,wasu abubuwa masu girma suna shigar kowane acikinsu..........kwallarta datake boyewa bata san sadda suke anbaliya ba,har lokacin tana kallonsa don gani take shine kallo na karshe da zatai mashi. Girgiza mata kai yake bakinsa yayi nauyi matuka,muryarta sosai take rawa tace. "Yaya Abdoul inhar kana son faranta mun ka.....aur......ka auri zakiy.....zakiyya" Kuka ya ci karfinta tasaka hijab dinta tana rera abunta,wanda jinsa yake har cikin karshen ransa kamar ya jawota ya matse yana lallashinta,riko hannunta yayi sosai yanajin yadda kirjinsa yake halbawa..........yace"safiyyah" Kasa ansawa tai tana son amshe hannunta "kasakan zan shiga gida kar aga na dade" "Zan sakeki amman why are you crying,kefa kika fada da bakinki cewar baki dace dani ba,itace tafi dacewa dani,har kina rokona akan in aureta,to kuma kuka namiye kike" Tarage sautin kuka tace"babu komi" "Akwai komi,meye cikin xuciyarki inaji ajikina kamar kin kwari kanki,kamar kin cutar da xuciyarki amman bazan iya gane haka ba sainaji daga gareki" "Aa babu komi sai anjima" Rike hannun yayi sosai yana sanyaya muryarsa yana rage mata sauti,cikin wata murya da tasaka ta lumewa cikin kujerar yace " *did u love Abdoul-naser*" Jitai har numfashinta yana niyyar barinta,maganar ta daketa sosai da sosai kawar dakai tayi tana aro jarumta tasaka ma ranta ahankali tace" sorry i don't lov.......love u" Lumshe idonsa yayi baice komi ba,ya dan kai hannun bakinsa ahankali kamar zai mashi kiss suka hada ido yasaki hannun yace"sai anjima" Fita tai yaja motar yabar wajen. Kafafunta kamar ba nata ba haka takejinsu kamar mai koyon tafiya ta nufi cikin gidan. [9/21, 3:59 PM] Mom Muhseen: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSEER* *(ALFAH)* WRITTEN BY MRS BB MOM MUHSEEN FOR SALE 300 NAIRA ONLY 09034722970 🅿️..........48 "Yajikin naki uwata" Cewar baba kenan bayan shigowar fiya ta zame saman cinyar mama ta kwanta,tana jin kamar taita risgar kuka ko zataji saukin abunda yake damun xuciyarta da gangar jikinta. Idonta arufe tace"na samu sauki sosai baba,ya naka jikin kaima" Yace"yanzu muhseen yace zai koma ya taho daku ashe kuma kun taho" "Uhm" kurin tace don bata son ma ko maganarsa aimata. Mama tace"kasan yaron nan nagidan Alh muazzam ne ya taimaketa,akan idonsa aka saceta Allah yarufa asiri yabisu tare da yan sanda" "Wane yarone na gidan Alh muazzam?" "Malam har kamanta yaron nan Abdoul nasser" Canxa fuska yayi yace"madalla ya kyauta sosai,ana son irin haka" Daga haka sai mama tayi shiru don taga baison maganar. Tunda koma gida ya shige dakinsa bai ake fitowa ba,yarasa abunda yake mashi dadi magananunta kurin suka mashi yawo cikin kai,meyasa takeson cutar da xuciyarta saboda wata wadda bata san darajar mutun ba,bata san karamci da mutunci ba.har ta buda baki yace mashi ya auri zakiyya,tsaki yaja yana dukan bedside drower dinsa da hannunsa ko zafi bayaji. Nizata kalla tace bata sona,to daman waye yace yana son nata ita nan har zata ja ma mutane rai.idan tana ganin hakan daidaine shikenan bai shirya ansar zakiyya ba amman tunda ta nuna itace tadace da rayuwarsa fine. Wani zafi yakeji aransa to inba ta sonsa kukan ubanme yake mashi amota,mtsss yaja dogon tsaki kamar zai fito da halshensa don haushi. Knocking ake mashi yasake jan taki cikin tsawa yace"waye nan,banson takura" Yasan itace don malik baya nan. "Yaya kabude kofar nan pls muyi mgn" "Bana son maganar nikuma,pls out" Marairaice murya tai tace"yaya don Allah mana" Cike a haushi ya tashi yabude kofar kamar zai kifa mata mari yake kallonta. Tsaye yayi bai bata damar wuce wa ba yace"fadi inaji" Langabar da kai tayi cikin sigar da zata jawo hankalinsa tace"yaya magruba ta taho babu kyau bacin yamma" Wani jakin kallo yake mata yace"sai akace maki bacci nake ko,pls go i need to rest" Matsowa tayi sosai kusada shi kamar zata rungumeshi,wani takaici ya cikashi miye haka zakiyya keyi,ko dacan bata mashi wannan iskancin balle yanzu da baya jinta aransa. "Yaya Zan debe maka kewa nasan kana cikin damuwa." Wani kullutun haushi yazo mashi wuya,yadda take wani kusantoshi abun yake kona mashi rai. Fixgo hannunta yayi damugun karfi yayo wajeda ita bai ajeta ko ina ba sai waiting falo,yayi wurgi da ita saman kujera yace cikin fushi. "Stay away from me,inbacin iskanci nizaki ringa turowa kirji,angaya maki dan iska ne ni.kokuwa danake sonki sha,awarki nake,zakiyya!zakiyya!!zakiyya!!! Kinji uku ko kita idona wane irin haline kika aro kika yafama rayuwarki.shekarun baya ban sonki da wannan abun ba,ban sonki da sonkanki ba.ban sonki da wofintar da darajarki ba.ban sonki da rashin kunya ba,why yanxu kike yi just bcos of her Imagine!kinji kunya yarinya kankanuwa tafiki sanin meyadace da rayuwarta,tasan darajar kanta gata da kawaici da hkr da kauda kai.saike dakika kusan haihuwarta kike aikata abubuwan da basu dace dake ba.to last worning kitsaya iya matsayinki kafin na yanke mummunan hukunci akanki." Yajuya afusace yabar wajen. Kuka ta rushe dashi tana data sanin daukar shawarar da xuciyarta tabata,ita kanta yatoshe kaunar Abdoul ta rikitata hanyar dazata shawo kansa take nema,gashinan tasake bata rawar ta da tsalle. Malik bai dawo gida ba yana tashi daga wajen aiki ya wuce gidan dady sunyi waya akan su hadu gidansa,su gama sauraren wadanna recording din. Baima biyo ta gida ba don karya sake bata lokacin yau yake son duk dare sai sungama sauraren komi,kafin asan wadda ake ciki. Falon dady ya shiga da sallama tv ce keta surutu yasamu waje ya zauna yana turawa Alfah text din cewa karyaga bai dawo ba suna tare da ddy. Dadyn ne yafito suka gaisa suna dan tattauna abunda ya gabata sannan ya miko system din yace ya kunna. Shiga yayi inda suke ya lalubo gudan audion da basuji ba,ya kunna. Muryar ummu ce ta sake fitowa ras kamar lokacin take maganar. "Zakiyya muddin kika bata mun shiri Allah ya isa ban yafe ba,ke ba Allah ya isa kadai ba zan maki ba tsine maki zan kishiga duniya,inhar nice uwarki duk abunda na tsara maki shizaki yi saba mani kamar kin zabi tsinuwata ne,duk lalacewa ta dai uwarki ce ni dole kuma kiyi abunda nace" Shashshekar kuka zakiyya keyi tana cewa"umma kiban umurnin komi amman ban wannan,bazan iya yiwa Yaya Abdoul karya ba muddin wani abu yasamai ta silata Allah saiya saka mai,nikuma bazan yafe ma kaina ba.umma kiyi hkr ki ji tsoron Allah karki aikata abunda kike shirin yi" Ji kake tas tas tas,an wanke zakiyya da kyawawan maruka har uku cikin bala,i umma kecewa. "Harna haifi dan zai mun gardama,kedin wacece don
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101