Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 77

Chapter 77

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,293 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

aka yaya muhseen ne to kuma naga maganar ta wuce still bakibar damu ba,kodai na gaya ma mama" "Karkifara kuskuren gaya mata don bata wa zamuyi" Cikin damuwa tace"amman Adda ni kina kokarin fitar dani cikin tawa damuwar taya kikeson zan jure ganin ki ahaka,kigaya mun ko shawara saina baki" "Yesmin idan lokacin sanin yayi zan gaya maki amman kicigaba da man Addua Allah ya zabamun abunda yake alkairi ga rayuwata." "To Adda insha Allah,amman kema ki dage kiyi tayi sannan ki rage saka damuwa bakiga yadda kika rame ba" "Zan rage yesmin karki damu" Tafita don kiran da mama ke mata,kalon wayarta take kamar xata ganshi aciki,wata xuciyar ce ta raya mata kila bazai rasa wannan sabon layin nata ba,don shine yayi mata register kila yayi saving no din.wannan yasata jin wani sanyi har cikin ranta,ta rarumo wayar da sauri amman saita rasa wace no din zata kira,idan tayi nazari xata iya tuno no din daya kirata atsohuwar wayarta amman daker idan daidai zata rubuta,haka ta fara sakawa sa bismillah tana adduar Allah yasa itace. Hannunta har karkarwa yake idonta cike da kwalla,bata san girman soyayyarsa acikin ranta ba amman koma ya take tana masifar azabtar da xuciya da gangar jiki. Kamar wasa taji tana ringing,wata zazzafar ajiyat xuciya taja harda lumshe ido. Yana dakin dayake aikin sa wani dakine na musamman da yake zama yana rage ayukansa akan computer,yana rubuce rubucensa fa takaddu.suna tare da malik ma alokacin yana nashi aikin shima,yace"yallabai wayarka fa tana neman agaji" Girgiza kai yayi yana saka biro ga bakinsa idonsa ga computer yace"bana jin zan iya waya aikina nake" "Idan someone special ne fah" Murmushi yayi yana kallon kofar shigowa don ya saka zakiyya ta hado mashi naman,da madarar daya shigo dasu ta kawoma malik nashi taje ta dauko na Abdoul din.daidai shigowarta yace"gata nan ai kaga kuwa duk wanda zai kira na musanman bayanta yake" Mamaki ya kashe malik baidaice komi amman yasan tabbas akwai abunda ya faru tsakaninsa da safiyya,kuma zaiso yaji koma miye. Jawo table tayi tana dora komi asama fuskarta kadaran kadahan,yana dan murmushi yace"bakiji ba hajiyata" Jiyowa tai tana kallonsa yadaga girarsa yace"eh ban gama dake ba pls sit here" Yana jawo dayar kujerar dake gefensa ya nuna mata,kallon malik tayi asace yayi kamar bai gansu ba,tadan jima kafin ta zauna.malik hakanan yaji abun bai mashi ba,ransa baimai dadi ba amman zaisan mezai. Tashi yayi da tashi system din yana ficewa. Rubda ciki tayi tana kuka mai sosa rai,hakika so masifa ne idan bakai dace da wanda kake son ba,tabbas kalar tata soyayyar idan banda wahala da ciwon xuciya babu abunda take haifarwa............amman tana so tasan dalilin yin fushinsa don kurin tace tana bata sonsa,bata ra,ayin auren kalarsa.duk da kalamanta sunyi tsauri tayine don ta gano ko yanajin makamancin halin da takejin kanta akanshi,ashe kwaba tayi bata sani ba.........hakika dole xai fushi saboda kalamanta amman ai yayi mata uxiri,tana mace ba kimarta bace furta tana son sa,hakan bai dace da ita ba. "Bayan duk abunda yafaru zakiyya na dauki zafi dake sosai,kuma har yau ban daina ganin laifinki ba.may be idan naji hujjarki zuciyata zata iya sassautowa,amman aduk sanda zan kalleki wannan bakar ranar nake tunowa" Hawayenta ta share tana kallonsa kamar xara hadiyesa don tsananin kauna. "Yaya Abdoul ka fahimceni wlh Allah ne shedata banda zabi banda wata mafita daya wuce bin bayan umma da sunan amuncewa,saboda wannan hanyarce kurin zan iya taimaka maka.ta cigaba da bashi labarin duk abunda tai har kawo kan abunda yafaru da ita da zamansu da fiyah komi ta sanar dashi ataiaice,wani malolon tausayinsu ne su biyun wata kaunar yarinyar ta sake dabaibaye xuciyarsa,yasan tabbas kaurace matan dayai tana cikin wani hali,amman shima yana cikin halin da yadace amashi uxiri. "Shikenan kibar kukan komi ya wuce,koma miye nasan gobe zanji abakin dady,nagode maki kiyya kuma kiyi hkr abisa rashin fahimta danai maki,duk wanda ya ga abunda yafaru zaiyyi ma fiye sa abunda nai kiyya,don haka ina maki albishir Abdoul din dakika sani baya he will return okay" Yafada cikin tsokana ta sadda kai tana murmushi,ahakali yake janta da fira suna cin naman suna shan fresh milk din,zakiyya jitake kamar tanayawo agajimare,yau itace da abdoul dinta haka lallai komi yayi farko zaiyyi karshe,amman fargabanta guda har yau yana kan bakarsa ta bangaren fiyah ko aa,tanajin zafi da kunan kishin fiyah yana taso mata,tana zargin Abdoul bazai iya rabuwa da itaba. "Kije ki kwanta dare yayi munyi mgn da safe" Badan tasoba haka tatashi tana waigensa,murmushi yake binta dashi har tafice. Dafe kanshi yayi dake masifar sarawa............abubuwa suna dawo mashi tsanar umma da yaranta tana ninkuwa cikin ransa,inama zai iya daukar doka ga hannunsa,ya rantse da saiya kashe duk mai saka hannu cikin tashin hankalin daya shiga,amman ina bazai iya ba yasan ko yayi yunkurin hakan baza,abarsa ba amman zaiso yaje yaji matakin dasuka dauka muddin bai mashi ba dole xai dauki nashi dakanshi. Ajiye ayyukan yayi yana daukar wayarsa daya samu missed call uku kalon no din yake yana karanta su,yayi saving no din amman baisaka suna ba,bangare duga na xuciyarsa yana jansa ga wani waje,amman yanaga hakan ba mai yuwuwa bane. Fitowa yayi yana wuce bedroom dinsa,shirin kwanciya yayi amman xuciyarsa ta azalzalesa akan kiran no din kodan ya tabbatar ma kanshi da cewar itace ko ba itabace,saida yayi relax agado ya kure Ac sannan yayi dailing number yanaji tana ring amman babu ansa. Kasa hkr yayi ya sake kiran. Lokacin fiyah tasha kukanta ta godema Allah tana cin alwashin muddin bai biyota ba ta yafeshi har gaban abada,koda hakan na nufin sonsa zai kassarata,tana jin wayar na vibration saida ta gama ta duba taga shine,bata bisa ba saida ya sake kira.hannunta yana rawa ta dauka wasu hawayen tausayin kanta suna silalowa,sai kurin ta sa kuka........ Kuyi hkr da wannan ina cikin jimamine wlh nagode da adduoi ku [10/5, 7:03 PM] Mom Muhseen: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSEER* *(ALFAH)* WRITTEN BY MRS BB MOM MUHSEEN FOR SALE 300 NAIRA ONLY 09034722970 🅿️...........55 Wani abune yakeji tundaga kafarsa har cikin kanshi,ya wuce xuwa xuciyarsa kafin ya watsu cikin gangar jikinsa.runtse idanuwan sa yayi yana jin zafin kukan da kunan sa cikin ransa...........yana daukar duk wani alhakin kukata akanshi,hakika bata cancanci irin wannan ba,don kuwa halaccinta yafi yayi mata abunda xai sakata kuka,kukan ma irin wannan mai ratattake xuciyar mai sauraro.ahankali ta koma yin kukan kasa kasa,lumshe ido yayi yanajin inama inama,inama ace gashi gata take rera mashi wanan kukan wanda lallashin sa ya dace ace ajikinsa zai lallasheta,yana yi yana shafa kanta yana hura mata isaka afuskarta da kunnenta,tabbas ba shiru ba har bacci ma zatai.amman inaaa bazai sameta ba koda yasamu sai idan tana matsayin mallakinsa ne zai iya hakan,huci ya furzar cikin wata kasalallar murya yafara magana,wadda saboda salon maganar da yadda yake furta kalaman dole tasa kukanta yasake yin kasa,don wasu abubuwane masu kama da kibiya suke sukarta babu kakkautawa. "Serfiyyah plzzz stop crying,I'm sorry I'm very sorry.I don't mean to hurt you plzzzzz I beg." Ahankali take shashshekar kukan tana ajiyat xuciya don wadannan kalaman sunyi matukar tasiri acikin xuciyarta,sun wanke kaso hamsin na damuwarta. "It's okay an safiyyah na sorry goge kwallarki ki gaya mun waye ya taba mun ke yanzu aga fushina." Shiru tayi tana yin lamo akan katifarsu

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});