Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 4

Chapter 4

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,299 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

yi silar zuwanka gidan yari mugu........azafafe yadawo wajen malik na rik'eshi yana cewa"haba Alfah karka biyeta macece zaka iya rauna ta tafa,wani irin juyowa yayi yana kallon malik yace"nasan da cewar macence ai shiyasa zan koya mata hankali yadda zata ji tsoron tunkarar namiji ko bani ba,don ubanki ba gidan yari ba kisaka akaini lahira inkikai hakan zan dawwama ina saka maki albarka jakar banza," Kuka take tana cewa"wlh sai babana yayi sanadin ajalinka,inhar yasan kaine ka mareni zaka gane kurenka mugu........k'afa yasa zai halbeta yaji anrik'e k'afar caraf cikin mamakin wanda yarik'e kafar sa yake kallon wajen........ *fiyah* ce tayi han zarin rik'e kafar tana hawaye duk sun wanke mata fuska,wani irin wurgi tayi da k'afar tana share kwallarta ta mik'e daga durk'ushen da take gaban Rafeea,cikin d'aurewar fuska kamar ba fiyah ba,cikin masifa da y'ar muryar ta kamar ta yan yara tace, "Kar ka sake gangancin dukanta,kai baka da imanine ehy,bakasan kima da darajar mace ba,ana gaya maka cewa macece karka biye mata kaji mata ciwo,shine kake son sake kaimata duka,to kasani wlh muddin mahaifinta yaji bakaiba kaf danginka sai akulle tsinann..........cikin fita hayyaci Alfah ya yunk'uro zai kwasa mata nata marin,tai saurin ja baya Malik da dr suka rik'eshi......cikin zafin xuciya yace"kubarni na lahanta yan isaka.....janshi sukai har cikin taxi d'in daya tsayar d'azun suka shigar dashi daker, sadda xai shiga saida ya juyo idonsa cikin na Fiyah ya nunata da yatsa,yana girgizashi alamun worning. Harara tabanka mashi tana mashi alama da hannu wuce kaidai. Dr yace wa malik"abokina kaban no dinka pls don koda kai baka nemo niba nizan zo har gida induba jikin nashi,don zamanshi babu kulawar likita hadarine ga rayuwarsa." Babu damuwa ya ansa wayar yasa mai sannan yayi mashi asauka lfy. Lallashin Rafeea take tana cewa"kiyi hkr muje gida kinga dare yayi nasan sai nasha fad'a wajen baba da mama,tashi kiyi hkr inkinje gida kisanar da Abbanku nasan dole zai daukar maki mataki,dole ne ma wannan." Tashi tayi tana share kwallarta don har ga Allah mari ya shigeta ba kadanba. Dr ne ya iso wajen yana cewa"kiyi hkr Rafee,atu karki sanar da Alhaji kiyafe mashi bai cikin hayyacinsa hakan tafaru." Cikin masifa tace "shine zai juye haukanta sa akaina wlh saina fad'a ai gabanka yayi man wannan zalincin ko kuma baka dauki mataki ba",ta nufi motarta tana masifa. Tafiya suke zuwa gida fiyah tace"kinsan dr ne Rafeea." Tsaki taja tace"likitan kakane shike zuwa har gida yana dubata duk karshen wata." Jinjina kai tayi tace"amman baza kiyi hkr ba Rafeea kiyafe mai tun da kinji cewar baya cikin hayyacinsa hakan tafaru,don inkin lura hannunsa jini yake fitarwa,kuma sai yanzu na ganeshi shine wanda d'azun na taso makaranta aka bankeshi kan titin central park,na yarda da dr da yace bai cikin hayyacinsa ki yafe mai." Tsaki taja tana kara gudun motar don tuni angama sallar mangaruba, "Ki kyaleni fiyah,wlh saiya gane cewa ya tab'o yar gidan Alh muazzam Canji." Shiru fiyah tayi don daman tasan za,ai hakan Rafeea na da fada aji wajen mahaifinta,don kuwa ita dayace mace wajensa,jida ita yake sosai duk abunda takeso yi mata yake,kuma duk wanda ya tab'ata yashiga uku don bazai kyaleshi ba. Saboda haka mahaifin fiyah baison alakarsu,don dai kurun mahaifiyarta macece mai tsananin kirki da mutunci,shiyasa yake d'an barinta tana shiga gidan kuma take hudda da Rafeea,badan ransa yasoba.don yadda duk estate din suka kafa mashi k'ahon zuk'a akan zamanshi cikinsu,shiyasa yake iyakar yinsa don ganin ya kiyaye abunda zai saka suci mashi mutunci. Har suka isa gida fiyah bata sake cewa komi ba godiya tayi mata da kuma saida safe kowace ta shige gidansu. "Assalamu alaikum...........ina kika tsaya sofiyya badai kijin maganata ko,bance inkinga wannan yarinyar zata shiriritar dakeba ki kamo hanya kidawo gida,banson wannan alakar taki da ita ko kad'an kinsani,amman ina hakuri ne saboda mutuncin uwarta,amman inbacin haka bazan bari kina shigewa wadannan mutanen a da basu san mutuncin mu ba." Duk Malam kabir El-ladan ne yake wannan fadan watau mahaifi ga sofiyya. Sadda kai tayi tana idasa shigowa cikin gidan,durk'usawa tayi gabanshi cikin ladabi da biyayya tace"baba kayi hkr wlh akullum ina kokarin kiyaye duk abunda kake gaya man,matsala aka samu shiyasa amman dawuri muka taho." Ta zayyane mashi duk abunda yafaru tacigaba da cewa"wlh baba dagaske Rafeea take zata iya fa da ma Abban su kuma har prison yana iya kaishi." Baban yace "Allah ya kyauta,ni shiyasa banson kina shiga motarta yanzu dada tsotsai wani abu yafaru fa,ki kiyaye ba koda yaushe zaki ringa shiga motar ta ba kinjiko mamana." D'aga kai tayi tace"insha Allah baba zan kiyaye kayi hkr." "Shikenan,nayi tashi kije kiyi sallah Allah yayi maki albarka." Tashi tayi tana ansawa da Ameen maman tace intayi sallar tazo ga abincinta nan ta d'auka,shigewa tayi d'akinsu tana magana da yesmin dake ta faman gugar uniform. "Yaushe kika dawo yesmin." Tace"Adda nah nima ban jima ba uncle yahya ya ka woni bajima wa,anty tace gobe inkin taso kibiya tana da magana dake." Kayan ta ke cirewa tare da cewa"uhm ni wlh Anty zata matsaman kan wani kanen mijinta,ki kyaleta kawai yesmin ni 6allemun wannan abar." Tana juya mata baya ta 6alle mata bra d'inta. ************* Tunda suka dawo gidan malik baiyyi gigin sake mashi magana ba,don yasan yanzu zai sake burkicewa babu mai taimakonsa kuma,don unguwarsu ba sosai mutane ke shiga sabgar da batasu ba. Malik ya dawo daga masallaci sallar isha,i ya samai falo shima ya gama tashi sallar agida yana d'auke praymate d'in. Girgiza kai yayi kawai don baisan yadda zai yasa Alfah cigaba da yin sallah cikin jam,i ba,ko masallacin bai zuwa duk sallar dazai tofa cikin daki zaiyyita.fuskarnan kamar kullum tur6une babu walwala babu rahma kanta. Zama yayi yana kallonsa kafin yace mashi. "Me zakaci abokina" Kallon banza ya wurga mai kurun yana cigaba da opreting system d'insa,xuwa can ya ajiye ya tashi yaje gaban frig ya bude win d'insa ya dauko ya cire hancin,ya bulbula ga cup ya koma mazauninsa yana kurb'a yana aikinsa,....kallon bakin ciki da takaici kawai malik kemashi,don baima san yazaiyyi da Alfah ba,idan akwai abunda yatsana cikin halayyarsa sabbi to bai wuce wannan shan win d'in da yake ba. Kasa hakuri yayi yace mashi"Wai Alfah mai yasa kakeson kashe kanka,meyasa kai rayuwa baka daukar komi da sauki,duk abunda Allah ya kaddara maka baka hkr karok'esa sassauci,ina anfanin wannan halayyar daka k'irk'iro ma kanka...........cikin masifa dazafin zuciya ya jefar da cup din glass din dake hannunsa ya fashe kasa,yana huci. Yanuna malik da hannu yace"kafita harkata malik,kadaina takurani da kalamanka,komi nake komi zanyi is not ur business." Hawaye suka cika idon malik yace"komi zakace kuma kome zakayi man Alfah wlh saina gaya maka gaskiya,koda kuwa kasheni zakai wlh saina fad'a,don kuwa ina kaunarka inason rayuwarka idan kai bakason ta,ka taimakeni ka kulaman da ita,idan narasaka Alfah yakake son inyi,banfa da kowa saikai.Allahne gatana kaine gatana.plsss karage shan win d'inan koda baka bari dukaba dr ya sanar dani yadda tayi maka illah." Kwallarsa suka silalo kan fuskara yaciga ba da cewa"Allah yasan da abunda yafaru baka da laifi,amman ya6oye gaskiyarsa saboda yana son jarabtarka yaga iyakar imanin ka,duk wannan ba daidai bane,kuma kaima kasani kake take sanin.....cikin sanyin murya ya katse malik da cewa"enough!and i'm sorry to hut u." Tashi yayi yashige bedroom d'insa da system

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});