Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 7

Chapter 7

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,296 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

zaka daga kazamin hanunka ka mari y'ata,idan iyayenka da kayiwa sun kyaleka to kuwa banga ubanda ya isa ya hanani kulleka ba wlh,muddin ba hkr kabayar ba." Feea dake bayansa idonta yaraina fata don ganin yadda fuskar Alfah tayi babu rahma ko kadan,kiris yake jira yajuye tirar dake cinsa. "Abba kabari wlh nidai dayayi wa na yafe,na hakura kazo mutai." Zare mata ido yayi yace wa DPO "ku kullesa har sai nina bada damar fiddoshi"aguje malik ya iso wajen yana tare Alfah agigice yace"baza su sake kullesan ba wlh,sannan kushiga taitayinku zaku yi dana sani akan hakan." Alhaji kwangila shima cikin bala,i yace"ubansa kadai zaizo nan na hakura kuma bazai tab'a zuwaba domin kuwa wannan dan iskan yaron ya riga yafita daga cikin zuriar su,kunsan kuwa abunda yayi kunsan irin bala,in dayayi har iyayensa suka korai to bari kuji wannan dakuke gani,matar.............jikake tas tatas Alfah ne tsaye gaban Alhaji kwangila ya wankesa da kyawawan maruka har uku. idonsa yayi wani irin fitinennen jaa,dai-dai sadda wani babban mutun yashigo station din wada tacika da mutane,cikin shakewar murya da ta dishe saboda tsananin bacin rai "wlh kasake furta magana marar dadi akaina saina kasheka,saina fiddo yan hanjinka don ubanka katon banza katon wofi,b'arawon gwamnati baka iya komi ba sai yad'a karya da sharri.........kai *Abdoul-nasser* kul akul nace in ka sake magana saina sasab'a maka awajen nan." Wannan babban mutumen daya shigo yanzu yake fad'ar haka. Ajiye hannunsa yayi da yake nunnuna Alhaji kwangila dashi kamar zai kaimashi naushi,huci yake fiddawa yanajin kamar yadunga dukan bango kozai huce haushinsa......yace"Daddykabarni na koya mai hankali,kabarni na keta mashi rashin mutunci.ni....ni..zai....wulak'anta.......sai wasu zafafan hawaye suka shiga zarya kan kuncinsa. Malik kanshi hawayen yake na tausayin amininsa kuma dan uwansa. Mutumen yace"nadai ce karka sake magana idan ba haka ba zaka ga b'acin raina. tunda ya shigo duk aka k'ame ana sara mai,saboda shine comissioner of police. kallon su yake shima fuskarsa babu walwala ya kalli Alhaji kwangila yace" kagani ko,u see i tall u last time ka guji tun karar shi kar watarana ya baka kunya,Abdoul ba kunya ce ta isheshiba tun wancen karon balle yanzu da yasake firgicewa baijin kunyar yaga maka rigar mutunci,gashi kuma hakan akai bacin malik yaje ya kirani da banson iyakar abunda zai maka ba wlh awajen nan." Zufa yake share wa yana jinjina kai duk ya gigice,feea na gefe na kuka ganin yadda aka wanke ubanta da mafi,wanda yafi nata. fiyah kuwa kamar kazar da aka tsamota daga cikin ruwan zafi,duk ta firgice. Cikin taushin murya Alhaji kwangila yace ma mutumen daya ke magana "nagane hakan Alh maude,zan kiyaye." Alh ya kalli Alfah dake huci kamar tukunyar da aka gama sanwa da ita yace mashi. "Abdoul." Kallonsa yayi ido jawur batare da yace komi ba,yace"wuce kutai gida zanzo in sameku,malik idan yayi wani misbehave tell me." Jinjina kai malik yayi yana cewa"thank u Daddy." Jinjina kai yayi kurin yana cewa Alhaji kwangila "kana iya koma wa ga aikin ka,amman ka kiyaye don wataran abunda yafi haka zai maka,kekuma kiyi hkr kiyiwa Abdoul uziri ba halinsa bane." Feea dake hawaye tace"wlh ni daman nace mashi nayi hkr shine yace sai ya kullesa." Girgiza kai Alh maude yayi yace "uhm shikenan kawai kuna iya tafiya zanje namasa nasiha anjima." Kamar kububuwa Haka Alfah yafito daga station d'in,malik binsan yake cikin sauri don yasan wannan fushin sai yayi kwana uku yana yinsa,inbai samu wanda yajuye haushin sa akai ba. Tuni fiyah ta yanki hanyarta,don tace ma feea bazata bisu ba akwai inda zata bata d burin daya wuce tasan waye wannan guy d'in,ita sai take ganin kamar yana mata kama da yaran gidan *ALH MU'AZZAM CANJI* amman zuciyarta ta kasa yardar mata da haka,saboda in d'an gidanne mezai fiddoshi daga gidan yazo yana irin wannan rayuwar,girgiza kai tayi tanajin matukar tsananin tausayinsa na cika zuciyarta. Hango malik tayi ya tare masu taxi gudu-gudu sauri-sauri haka take had'awa har ta samu ta tari itama taxi d'in tace mai yabisu baya,binsu yake har k'ofar gidansu tace yayi parking daga nesa, Azafafe ya bude kofar motar yafito, sai soka hannunsa yake cikin kansa yana ya mutsa kyakkyawar sumarsa kamar ta larabawa,isa yayi bakin get din gidan nasu yana jiran malik dazai sallami mai taxi,dora hannunsa yayi ga bango sannan ya aza kanshi sama,daka kallai kasan yana cikin wani irin hali. Hawaye taji sun sulalo mata bata ma sani ba. malik ya iso inda yake yana bude masu karamar kofar shiga,yana mashi magana amman bazata iya juyo abunda yake cemai ba.saida taga shigarsu sannan tace ma mai taxin ya kaita maitama estate. Don lectures din da zata koma tayi anriga angama,kuma daman ita kadai ta rage mata. Har taje gida tana hawaye,ganin sun kusa isa yasa ta goge kwallarta tana daidaita natsuwarta,sallamarsa tayi ta wuto zata shiga gidan, ganin buta tayi bakin shagonsu ta dauka ta wanke fuskarta,yadda baza,ai mata tambayar kukan me tayi ba. "Sofiyya yau ba magana." Maitsaron shagonne yayi mata maganar,watau dalha cousin dinsu ne ta wajen mahaifiyarsu,sadda aka gama had'a shagon ta je har rimi ta daukoshi don daman zaman banza yake acan. Rimi garine cikin katsina Cikin rashi kuzari ta juyo tana yak'e tace"ayya d'alha wlh nagaji ina sauri inshiga gida,sannu da aiki ya kasuwar." Murmushi yayi yace"da godiya,maza hanzarta kar acinye babu ke." Murmushi mai kyau tayi ta shige tabarsa. Sallama tayi yesmin dake kwashe shanya ta ansa mata. "Sannu Adda kin shawo rana." Jinjina kai tayi ba ta bata ansa ba,bin bayanta tayi da kallo cike da nazarinta,da alama Adda na cikin damuwa. Mamace tafito daga cikin daki tace"kamar sallamar fiyah naji ko." Yesmin dake linke zane tace cikin rashin jin dadin ganin yayar tata haka "itace mama,amman kamar bata da lfiya tashige d'aki." "Subhanallahi,bari inje inji." D'akin nasu ta shiga tana kiranta,bata cikin dakin amman jiyo karar ruwa cikin bayinsu yasa tajuya, tabarta ta fito. Haka Allah ya yi sofiyya da daukar damuwar wani ta zama tata,mace ce mai tsananin tausayi abu kadan zai karya mata zuciya,duk da halayenta sunda yawa amman abu mafi bayyana tare da ita shine,san yinta kafin kaga zafin ta zaka jima sannan akwai zurfin ciki sosai,tana da shanye damuwa abu zai jima yana damunta bata bayyana shi ba. Wankan ta fito tana shafa amman yanayin fuskarsa take hangowa,da zafafan kalaman da abban feea yake gaya mai,runtse ido tayi hango yadda idonsa yayi jajawur gwananin ban tsoro........haka ta gama murza man ta saka kaya marasa nauyi tayi sallar azahar da la,asar sannan ta fito tsakar gidan. Mama da yesmin nata hira tazo ta zauna,ta dora kanta bisa cinyar maman tana shagwabe fuska. "Mama yunwa nakeji." Shafa kanta take tace"yesmin dauko wa Addarki d'anwakenta yau mutumen ki akai zakici ko." Daga kai tayi tana sake narkewa daman fiyah badai shagwaba ba,ajiye mata yesmin tayi tana cewa"Adda d'azun ina magana baki tanka niba." Murmushi tayi mata mai sanyi tace"sorry my little,ban cikin natsuwa ne kiyi hkr kinjiko." Tana murmushi tace "bakomi Adda nayafe maki,kinje gidan Antyn." D'an waken take ci cikin rashin kuzari,har yanxu amon muryarsa takeji sadda yake mayar wa da Abban feea magama cikin,kunci da bayyana bakin cikin da yake ciki.kamar bazata tan ka ba tace"banje ba yesmin,ban samu time ba kilan sai gobe." Ko kwatar dan waken bata ciba ta ajiye tace "na k'oshi

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});