Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 26

Chapter 26

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,293 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ji yabud'e k'ofar yafiro rataye da jikarsa,dayan hannun kima jaye da trolley sa bai kula sa ba yayi gaba sannan yace"inkana iya kaini airport bismillah inkuma baka iya wa naje na hau taxi." Yana gama fadar haka ya wucesa zuwa waje. Mamaki ya daskarar da malik,ganin sabon canjin Abdoul daya zo dashi yanzu.yajima kafin wani kayataccen murmushi ya kubce masa,yana daka tsalle yace "yesssss,wlh anfara nasara gaskiya ngd sofiyyah,wlh aikinki yana kyau." Ficewa yayi da sauri yaje ya samai amota. Har sukaje filin jirgi malik sai surutu yake masa cike da jin dadi,kuma yauce ranar da Alfah bai dakatar dashi daga surutun da yake masa ba,da dane cikin tawa zaice ko kamun shiru kona bar maka motar. Har jirginsu ya tashi Alfah bai takama malik ba,sai kalma guda daya ce masa da ta sake jefashi cikin farinciki. Cewar da yayi..... _TAKE CARE FOR UR SELF_ koda Alfah ya zauna babu abunda yake sai tunani,kalaman yarinyar suke ta mashi amsa kuwwa cikin kunne, duk sanda yajisu sai yaji wata suka cikin kirjinsa....... _macuci azzalumi mak'etaci baka san komi ba sari zallar cuta da shaye shaye,taya zakaji feeling din tausayi cikin ranka ai bana tantama inkace zakai kisan kai,don kuwa y'an shaye shaye kamarka babu abunda basa yi,wannan la,anannar giyar babu abunda bata sawa.wani ma saboda ita uwarsa yayi wa fyade._ Runtse idonsa yayi yana karairaya glass din dake hannunsa,jiyake kamar ya fashe.......... _wannan la,anannanr giyar babu abunda bata sawa. wani ma saboda ita uwarsa yayi wa fyade._ Ya sakejin kalaman suna sauka acikin kunnensa......duk'ewa yayi yana dafe kunnensa,wata dake bayansa ta lura da halin dayake ciki ta d'an tab'osa kad'an. Afirgice ya d'ago kamar wani tab'ab'b'e ya zuba mata dara daran idonsa,babu arxiki tayi saurin koma wa inda take. Durk'ushewar yasake yi yana jin kamar ya kurma ihu ko zaiji saukin masifar dake addabarsa cikin rai. *kuyi hkr yau ban yi posting kan lokaci ba wlh bamu samu wuta ba shiyasa,kuma kuyi maleji dashi wlh banda time ne.* Mrs bb ce Mom muhseen 09034722970. [9/17, 3:37 PM] Fauziya Madaki: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSER* *(ALFAH)* WRITING BY. MRS BB MOM MUHSEEN. WATTPAD NAME HUMAIRA7531. *DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB AND ALFAH FANS* 🅿️.........20 Malik ya kasa samun natsuwa saboda farincikin da yake ciki,so yake yasamu wani yayi sharing feelings dinsa dashi,fiyah ce ta fado masa ya lumshe ido yana murmushi mai kyau......zama yayi yana cigaba da murmushin,kafin tausayinta ya cika masa xuciya yasan tana can cikin halin ciwo wayarsa ya lalubo gaban aljihun rigarsa yana dailing no dinta,ta jima tana ringing ba adauka ba yabari bayan sallar isha,i ya sake kira. Tashi yayi ya nufi masallaci don baisan rasa jam,I yana son ya sake rok'on Allah daya cigaba da basu sa,a akan Abdoul.don wannan nasarar tayau tayi tsananin sakashi cikin nishad'i inama zaisamu damar yin waya da mami ya bata labarin halin da d'anta mafi soyuwa agareta yakeciki,amman yaji kashedin Abbi bazai so yayi silar barinta wannan gidan ba bayan duk wadannan k'alubalen dasuka faru. 💞💞💞💞💞 Yau suna cikin farin ciki don gaba ki dayansu suna kan tabarma tsakar gida suna hirar da suka jima basuyi na kwana biyi da babu baba. Kowa ka kalla zaka gansa cikin Annashuwa da farinciki,amman fuskar fiyah da saukin walwala,duk motsin da zatai bak'ak'en kalaman Abdoul suke dawo mata cikin kanta,saidai ta fakaici idonsu ta goge kwalla,har baban ya lura yace"halan sofiyyah rigimarce ta motsa,meke damunki naga kwata kwata hankalinki baya nan." Danne kwalarta tayi tace"aa baba ciwukan nne suke man zafi,inakuma son in kwanta." Cikin tausayawa yace"Ayya sannu to,anshi paracitomal kisha ga mamanki zaki samu sauki saikije ki kwanta tunda kinci abinci." Kamar jira take ta tashi ta shiga d'akin mamar ta dauko maganin tasha sannan tayi masu saida safe ta shige d'aki. Koda taga misscall din malik bata bisa ba,don shima haushin sa takeji inbacin shi aida haka bata sameta ba,baida abun sanar da ita yasata tazo wannan marar imanin yakusan kasheta.......hawaye ta share tana jin wata zuciyar tana bata shawara akan ta rabu da wannam wahalar,ina dalili kana niyyar taimakon mutum shikuma baida aiki saina kashe kashe da neman makasarka.,bayi ta wuce tayo Alwallah daker tayi shafa,i da wutri sannan tatashi karatun kur ani tayi kadan,sannan ta ajiye tana jin kewar isalamiya na damunta,don lectures dinsu yanzu duk na yamma ne su suka hanata zuwa. Kwanciyarta kenan malik ya sake kira dogon tsaki taja tana danne wayar da fillow,amman zuciyarta na son dauka don gani take tayi masa wulakanci........bayarda ta iya ta daga filon ta dauko wayar,daidai sanda ya sake kira.dagawa tayi tana kangawa ga kunne hawayenta kuma sunata zuba,cikin shashshekar kuka tace"nidai yaya malik wlh nagaji,nagaji hakanan da wannan masifar,Allah ya sani niba yar iska bace ban san ma me ake nufi da kalmar ba,amman zai ringa aibatani yana cewa inyi yawo tsirara." .......sai kuka ya kubce mata duk yabi ya d'imauce ya ma rasa mezaice mata cikin kermar murya yace"kinga fiyah kiyi hkr don Allah kiyi hkr wlh Abdoul bai kyauta ba,kuma nima saida nai mashi fad'a bazai sake kwatanta maki irin haka ba,amman ki cire batun cewa kin gaji Ai daman inhar kana aikin lada dole zakasha wuya,kiyi hkr ladarki tana wajen Allah amman karkice kingaji karma zuciyarki ta sama ki fasa niyyarki." Tana share kwalla tace cikin raunin murya"yaya malik baka ga fa yadda ya saka kafafuna su kai ba,kilama ban iya sake tafiya"ta sake rushewa da kuka......dafe kai yayi yana murmushi lallai akwai shagwab'a nan wajen,danne dariyarsa yayi yace cikin tausaya wa. "Ayya y'ar kanwar malik,ya zakice haka kinga kidaina insha Allah babu abunda zai samu kafarki,kindai sha magani ko." Cikin kuka k'asa-k'asa tace"uhm" Ajiyar xuciya ya sauke yace"duk kin rud'ani wlh,nakiraki ina murna da d'okin samar dake wani labari kuma sai najiki ahaka." Dandanan ta wartsake tana goge sauran kwallarta tace"gaya man menene." Cire wayar yayi daga kunnensa yayi dariyar san ronsa sannan ya mayar yace"akan mutumenki ne." "Mts!nikadai na ban son ma ni ko sunan sa inji." Dariya yayi yace"sorry mana ansafiyya na,kiyi hkr kiyafe mashi kinjiko watarana da kanshi zaibaki hkr." Zaro ido tayi kamar yana ganinta tace"wannan dan zafin kan lallai! kaima yaya malik ka fad'a don tsokana." Dariya yayi yace"am serious kiyi ta mashi Addua zakisha mamaki,yanzufa yau abunda yayi ya ban mamaki sosai." Yabata lbr abunda yafaru d'azun. Itama tasha mamaki hartake jin ai yanzu ma ta ska k'afa cikin rayuwarsa har sai inda karfinta yakare,saita ga abunda ya turewa buxu nad'insa cikin jin dadi tace "Ashe abunda nake har zai iya canza sa zuwa haka yaya malik." Cikin tabbatar wa yace"sosai ma kuwa yar kanwata,kisake dagewa inyadawo sai kidora daga inda kika tsaya,idan da halima kicanza salo." Dariya tayi tace"kai yaya malik wai incanza salo uhm,zanyi dai bakin kokarina amman katabbatar da bazai sake shak'eni na." Dariya yake sosai yace"bazai kara ba aiyau nai masa fad'a sosai wanda ban tab'a masa ba kuma baiyyi fushiba,don da yayi ba zai mun magama ba." Tace"insha Allah i will try my best." Sunjima yana janta da hira har saidantaji yasmin zata shigo ta latse wayar tayi adduo inta kamar kullum suka kwanta. 💞 *Australia*💞 jirginsu yana sauka mutanen sa suka zo suka d'auke shi zuwa hotel d'in da zai sauka,don saukar dare yayi zuwa safe aroud 9:00 zasu fara abunda ya kawosu. Bin garin yake da

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});