Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 62

Chapter 62

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,294 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kuke?" Yesmin kwalla suka cika idonta tace"yaya dalha ina Addata" Sadda kai yayi yanajin banu dadi yace"wlh naje har makarantar,na duba nayi tambaya ansar dayace ko biyu wasu dasuka santa sukace ai tatafi gida,wasu suce su basu santa bama,bana nan naje duk inda nake tunani bansameta ba wayarta har yanzu kashe take" Durkushewa yesmin tai tana kuka sosai mama da baba suna sallallami,dalha yace "ga bako nan yana son magana daku wata kila yasan wani bayani akan rashin dawowarta" Yaje zaure ya shigo da malik yana sallama daker suke iya danne ransu suka ansa mashi saboda halin dasuke ciki. Babane yace "matso nan yaro zauna ga tabarma,karka tugunna" Baiyyi musuba ya zauna gefen baban yana gaidasu "lafiya ba lau ba yaro,Allah yasa lafiya daga wajenka" Malik cikin natsuwa yace"am baba daman zuwa nai nasanar daku safiyya tana asibiti,yan garkuwa da mutane suka saceta to Allah yasa gaban wani dan uwana sukai hakan shine yabisu ya kuma sanar da yan sanda hakin da ake ciki,da taimakon Allah dana Dan uwana shida yan sandan akai nasarar samunta ankuma kama mutanen,amman dai yanzu safiyya na asibiti ana duba lafiyarta amman jikin ba tsananta wa yayi ba,shine na samu bayanin gidansu nace bari nazo n sanar daku don kar hakalinku ya rau gida biyu" Mama hawaye suka.kece mata tana cewa"lahaula wala quwwata ialla billa ni y'arsu,Allah kadubemu saita duke tana hawaye" Malik yace"kiyi hkr mama ai abun yazo da sauki da yanzu bamu san inda take ba,ku kwantar da hankalinku tana cikin kulawar likitoci insha Allah tana lafiya" Baba yace "mungode ma Allah wadannan jarabawowi dayake mana ya kuma bamu ikon cinyewa,kaima yaro mun gode maka Allah yayi maka albarka kaida dan uwanka,tunda ni bazan iya zuwa ba kuje dasu don Allah suganta ko sun samu natsuwa,sai abar yesmin wajenta inhar sun riketa zuwa wani lokaci" "To aba baby damuwa su shirya muje kaima kanena afito sai muje" Yace ma dalha. *********** Fiya ce kwance kan gadon asibiti an saka mata oxygen,Abdoul ne gefemta hannunsa cikin nata idonsa ker akanta,kamar ance mashi zata ruga yana tuno abunda likitocin suka gaya mashi dazun bayan fitowarsu. "Yallabai mun samu daidaiton numfshinta,sannan sanadin Allurar da sukai mata tagusar da hankali hakan ya jawo zata kwana biyu bata farka ba daga baccin da take ba,idan kuma jininta mai karfine alluran da muka saka cikin drip din suna iya daidaita mata hankalin ta kilan ta farka xuwa gobe,karka damu yallabai aita auna arxiki don wasu ma daga nan sun haukace wasu ma mutuwa suke,she is very lucky Allah yabata lafiya,saita warke za,ai bill din kudin." Ajiyar xuciya yaja yana kallon hannunta da yatsunta dasuke mashi masifar kyau,zoben hannunta ya tsurawa ido kamar ya kai hannun ga bakina ya sunbata,amman yanajin tsoron kar xuciyarsa ta zurma dayawa karshe yazo yashiga tension,jin alamar za,a shigo yasa yatashi da sauri yana koma wa gefe yana zama saman plastic chair's................ Don't share it s i Beg Abdoulnasser its for sale if u need it contact me on 09034722970. [9/18, 8:46 AM] Mom Muhseen: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSEER* *(ALFAH)* WRITTEN BY MRS BB MOM MUHSEEN FOR SALE 300 NAIRA ONLY 09034722970 🅿️..........45 Idonsa bisa kofar shigowa malik ne farko sai dalha da yesmin,mamace last duk suka shigo mikewa Abdoul yayi yana sassauta fuskar sa cikin yanayin tarbar baki yace"sannunku mama,ha waje ki zauna"ya bata kujerar da yatashi akai. Zama tai yana sake cewa "ina wuni mama" yana sunkuyar dakai cikin sakin fuska tace"lafiya lau ya muka sameku,ashe kuma haka abun ya kasance to mun gode yaro Allah yayi albarka,Allah ya saka maka da alkairinsa sannunku" "Babu komi mama duk abunda kaima wani kamar kayiwa kanka ne,kaima akwai lokacin da zaizo kana bukatar taimako Allah shi zai turo mai taimakonka,shine kawai insha Allah likitan yace xuwa gobe ko jibi zata farka,saboda sun mata allurar maye idan jinin ta yana da karfi zata iya tashi nan da 18hours,ku kwantar da hankalinku babu wata matsala insha Allah" Yesmin kwalla take sharewa ta isa ga fiyah tana rike hannunta "Addata sannu kinjiko,Allah zai baki lafiya baba ma yana maki sannu bai iya zuwa da yazo ai" Abdoul tausayi ta bashi don da alama akwai kauna mai yawa tsakaninsu,ga kuma kamar da suke sosai dakaga fiyah kaga qanwarta..........mama tace"dalha sai mu wuce ita yesmin saita zauna kusada ita ko." Malik yace"mama inhar ba dai yarda damune bakiyi ba ai babu bukatar haka,tai tafiyar ta gida gobe saita dawo insha Allah,karkiji komi munan ai" Ajiyar xuciya tai tana satar kallon Abdoul,tabbas tagane yaron don tun baikai haka ba yake mutunta ta,inhar zata fito yaganta zai duka har qasa yace"ina wuni"idan unguwa zata zaice adawo lafiya,kirkinsa ba kadan bane,don yasha biya mata kudin taxi idan ta dawo daga wani waje suka hadu. Kwatsam taji wannan mummunan labari yafaru dashi,ta dade abun bai bar kanta ba kuma har gobe ta kasa yarda wannan natsatstsen yaron kamili shine zai haka,akwai wata dai akasa. Mikewa tai tace"aa yarona ai karka damu wlh nayarda daku sosai,wanda yyi maka wannan ai yafi gaban kace baka yarda dashi ba,naga kar atakuraku ne shiyasa amman tunda kace tatai shikenan Allah dai yayi maku albarka." Fitowa sukai suduka malik zai mayar dasu Abdoul zaimasu rakiya,har mama ta bude kofa kenan ta kalli Abdoul ta danyi murmushi tace"Abdoul-nasser ko?" Shima ya saki fuska yana shafa kanshi yace"eh mama baki manta ni ba ashe" "Taya Zan mance da kai ai duk wanda ya mance alkairi to abin cikesa gaskiya,kaidai Allah ya warware maka damuwarka.ya kuma kareka daga sharrin masu sharri,Allah yayiwa rayuwa Albarka.karo na babu iyaka kasake taimakona ta hanyar ceton guda jinina" "Haba kibar godiyar haka,ai safiyya kamar n,imah take wajena kibar damuwa" Shiga sukai malik yaja suka bar asibitin,tunani mama take barkatai meyasa ta hana safiyya abunda tai niyya kwanakin baya na taimakon wannan yaron,tunda har ta nuna alamun tana son taimakonsa tabbas kilan tana da wasu dubaru,da haka ta faru zataji dadi don wanda ya maka kaima kayi kokarin yi mashi,haka dai taita tunani har suka zo gida. Abdoul ya kwana asibitin don cewa yayi babu wata nurse dazai barma safiyya,idan ta farka cikin dare kuma nurse din tatai gantalinta fa,wazai kula da ita.malik dai dariya yayi yace to yallabai mukwana lafiya ni nayi nan,ya wuce yatai gida babu maganar xuwa wajen dady don dare yayi sosai,kuma yace in yadawo zaikirasa amman bai nemai ba. Washe gari malik ya gama shirin xuwa office ya wuce dakin zakiyya yayi mata nocking kamar bazata bude ba saigashi ta bude tai tsaye tana kallonsa babu ko gaisuwa saida yace"zakiyya ba gaisuwa kuma" Kauda kai tai gefe tana cewa can kasa kasa "ina kwana"murmushi yayi yace"kinga banine na kar xomon ba ko rayata ma ban ansa ba,kibari idan yadawo saikijuye haushinsa amman not me.yanzu kije kishiga kitchen kihada break za akaiwa fiyah,duk da bana tunanin ta farka." Wani kallo take mashi mai cike da haushi tace"yaya malik,ni zan mata girki?lallai ta mutu bata ci ba wlh" Kallon ta yake cike da mamaki "zakiyya" Kallonsa tai sosai tace"yes abunda kaji yaya malik,wlh bana iya ciyar da reble dina kamar dai banda hankali" Ransa yafara baci yasake cewa"i said go and cook her something" Juya baya tai tana kunkuni "ni gaskiya yaya malik, bazan iya ba haba don Allah mijina fa takeso shine zan mata girki"

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});