Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 22

Chapter 22

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,293 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

"ina sonsa, fiyah soyayyarsace ta ke hanani cin abinci take hanani bacci,ta kuma sani kukan da ba abigeni ba." Kallon mamaki da al,ajabi take mata bakinta har rawa yake. Tace"way...e......waye shi......in..a yake kuma." Sadda kai tayi tace" *ABDOULNASSER ALFAH*" Duka idonta ta fiddo tana kallon rafea kirjinta taji yayi wata irin ansawa,daker numfashinta yake fitowa yana komawa,maganar tayi masifar dukanta bakinta har wani k'afewa yayi saboda iskar data cikashi don abude tabarshi.........kanta taji ya sara xuciyarta tace"duk wannan rudanin na miye,inhar ba kina jin wani abu akansa ba." Cikin abunda baifi minty biyu ba ta koma yadda take,amman still kirjinta bugwa yake tayi kokarin daidaita muryarta takalli rafea data sadda kai tana hawaye,matsowa tayi tana rik'e da hannunta cikin tausayawa tace"rafeea,Abdoul kikeso? Alfah zuciyarki ta kamu da son sa?gaskiya bazan b'oye maki ba banji dadi ba,ko kadan banji dadin maganar ba meyasa zaki bari xuciyarki ta kamu da son wanda aduniya baida abun tsana sama da mace,idan yaganta jiyake uwa ya kasheta.bansan taya zan lallashi xuciyarki ba gaskiya don datayi shawara dani da bakamu da son sa ba.amman yanzu kinyi nisa bakijin kira." D'agowa tayi tana kallon fiyah cikin dishewar murya tace"dake na dogara,dake na laru don ke nakeson ki shigemun wajen wannan aikin,fiyah zaki iya inba keba babu wanda zanje na dorama wannan nauyin." Mik'ewa fiyah tayi cike da b'acin rai tace"oh ni dayake ban son ciwon kaina ba!zanje na samu namiji irin Abdoulnasser nayi maki feating love dinki,karshe duk zuciyarsa dayakeji da ita yajuye bisa na ya illatani yayiwa iyayena sara,koda yake ai su ba masu hannu da shuni bane basu san ciwon y'arsu ba." Ta juya tabarta nan wajen,aguje fea ta isa wajenta tasha gabanta tashare wayenta tace"karkimun mummunan fassara fiyah,niba nufina kenan ba kema kuma kinsan bazan iya maki wannan gorinba,inda dalilin daya sa nace haka." Wani kallo fiyah ta watsa mata tace"dalili,! wane irin daliline zaisa kice inje ga wannan mahaukacin ince masa kina sonsa injawo ra,ayinsa akanki haba rafea kinmun adalci kuwam." Jawota tayi suka zauna tace"abun da yasa nace haka fiyah tsawon lokacin da kika dauka kina hidden abubuwanki,nikuma na ringa binki abaya ina guiding dinki,har gidan dakike zuwa nasani har abokin Alfah da yake d'an kawoki makaramta ina sani,abunda kawai ban sani ba shine mekike zuwa yi gidan? meke tsakaninki da wannan abokin Alfah?din wata zuciyar ta cemun soyayya kuke kuma Abdoul zai sani kuma dagani kuna gaisawar mutunci." Idon fiyah ya rine da masifa fizge hannunta tayi dake cikin na rafeea tace"watau saboda tsabar munafurci bibiyata kikeyi ko rafeea?har xuciyarki take gaya maki wani banzan tunani ko,to inso kike kisan menake zuwa yi zangaya maki tun kafin sakarar zuciyarki ta kuma gaya maki ina bin maza.......yadda fiyah ke daga murya yasa feaa ta rufe mata baki,ita kuma cikin fushi ta fizge tace "barmi na gaya maki abunda nake ciki tunkan kije gidanmu kice ina bin maza,naga makauniyar soyayyarki ta rufe maki ido komi ma zaki iya........banda wata alaka ta soyayya tsakanina da malik abunda ya hadani dashi kuma aikin ladane,tun ranar da wannan abun yafaru da abbanki yasa aka rufe Alfah police washe gari na yanke shawar zuwa muyi magama da malik akan jin mafarin llacewar abokinsa. Fiyah ta juye mata halin da ake ciki na kokarin ganin sun dawo da Alfah cikin hayyacinsa. "Don haka ni babu wata alaka bayan wannan tsakanina da malik,ni babu wani namiji da zan gani inji ina sonsa,kuma taimakon da nayi niyya insha Allah zanyi sai inda karfina ya kare,ina sanar dake cewar haryanxu ban samu zarrar tunkarar Alfah da wata magana ba sai rannan shima kuma Allah kadai ya ceceni kiris ya rage bai karyani ba,saboda ganina dayayi gidansa.to inga inje ince masa wai wannan da kukai rigima bisa titi tace tana sonka ai wlh ranar ba bakina zai fasa ba idanuna tas zai tsoyayar dasu don ba imani ne dashi ba,shida mahaukaci banbancin kadanne. Idan kinji zaki iya tunkararsa wlh zan maki rakiya har k'ofar gidan,shima kuma dana kaiki zanyi kwana.inkindawo da kafarki kintsira.don naga baida abun sha,awa sai karya kafafun jama,a kome sukai mashi oho" Jin abunda fiyah kesanar da ita yasa gabaki daya taji jikinta yayi la,asar to wannan wace irin xuciyace Allah yayi masa,bai daukar komi easy Fiyah tace"zanje inshiga aji ga malam can yazo,tajuya tabar feea nan zaune tana tunani. 💞💞💞💞💞💞💞💞 Yau Abdoul zai yi tafiya zuwa Australia,zasu yi ani meeting daabokn kawancinsa na kwana biyar,sanan zaibiya ya bada oder kayanshi akawo ashi har nan abuja. Kayan sa malik yake had'a mashi shikuma yana kan computer,yaudai fuskar akwai sassaucin rahma ba kamar lokutan baya ba......shiyasa malik ya ma fiyah text inta taso ta biyo ta gidan yana son ganinta. Tun ranar da tayi masa gorin shan giya bai sake ganin yasha ba,saidai in ya fita don yazu dakin sa bedroom dinsa yake ajiyewa cikin frig dinsa. Babu riga jikinsa duk halittar da Allah yayi mashi ta bayyana,daka kallai kasan mutunne mai motsa jikinsa always. Yana da baiwar galgasa irin kwantacciyar nan maibin jiki,kirjinsa ma haka da kafafunsa amman ta kirjin saika rantse salon yake mata(🤭lol),har wani shalk'i take tana walk'iya. Haka gashinsa na kansa dana fuskarsa,yanada saje wanda yake had'e da gemunsa,kasancewar irin gashin nan na fulani garai kamar na larabawa,sai yasake hasaka fuskar sa idan yagyarasa kyau yake sosai. Baidamu da manyan kaya ba koda can daya na gida sai idan wani daurin aure zaije kozai raka Abbi wajen manyanmutane,sanan yasaka amman shi yafison kanana don kayansa mostly inyaje waje yake shigowa dasu,ko in malik zaije yabashi sakon da combus kala kala haka yake sawa kuma suna hawan kayan sa suna masifar yi masa kyau, Malik ya gama hada mashi akwati guda said yar traveling bag dinsa da ake rataya wa ga hannu guda. Kallonsa yayi cikin tsokananyace "yallabai na gama saura wankan." Cikin mamaki da al,ajabi yaga ya d'ago yana mashi wani irin smile wanda tunda suka baro gida malik bai samu wannan damar ba ga Alfah..........cikin jin dadi ya iso garesa yace"don Allah sake maimaita wa wlh kabaji yadda naji wani sanyi cikin raina ba,Abdoul inda kasan yadda murmushi yake haskaka fuskarka da baza ka so ka daina ba." Rufe systems din yayi yana nufar bayi baice masa komi basaida yakai kofar shiga yajuyo yace"fuskarce banso tayi haske,don baida wani anfani akanta muddin haske ya bayyana akanta mata zasuyi kokarin kawo kansu gareni nikuma bana sonsu,nafi kaunar mutuwata akansu." Yana gama fadar haka ya shige yabar malik da rik'e hab'a,tabbas da ace Alfah yana k'wata fuskarsa da murmushi da fara,a y'anmatan da zasu biyosa basuda iyaka,amma hakan ba hujja bace. Fita yayi zuwa main falonsu yana jiran isowar fiyah yana son su had'u da Alfah kafin ya wuce. Karfe uku yau suka tashi ko alamar jiran feea batai ba don tana cike da jin haushinta,tama rasa wanda zatace tana so sai wannan gantalellen mahaukacin,mts aka taringa jera tsaki ta fito daga makarantar,kirane yashigo mata mama ta gani saurin dauka tayi tace"Assalamu alaikum mama lafiya ko." Cikin farin ciki taji mamar tayi magana cewa"daman ince maki babanku ya dawo babu jimawa." Itama cikin farinciki tace"dagaske mama?wayyo mungode Allah mungode ma Alha ganinan zandawo insha Allah." Kashewa tayi sai lokacin taga sakon malik na biyu ayau din nan. _fatan lectures sunyi dadi,inba damuwa kisaman gida yanzu pls._ Tarar

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});