Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 70

Chapter 70

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,277 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

gaskiya da kadauki shekara da shekaru baka santa ba,kasan masoyanka kasan makiyanka.kasan makasanka dake bibiyar rayuwarka,wai da kai xuwa kai belin wadancen yan iskan dakau kayi nadama ba karama ba." "Wai Abdullahi duk wadanna maganganun na miye,nifa tambaya guda nai maka" "Shiga mota yaya,bari na sallami guards dinka da driver ka alabashshi idan mungama saika tai inda zaka amman yau bazan kyaleka cikin kokwanto ba" Yaje ya sallami driver da sauran security dinsa ya dawo yashiga motar sa suka bar station din. ************ Tunda fiyah tabar gida ko kadan kalaman baba basu bar kanta ba,yadda yayi saurin na,am da muhseen din ne yake bata mamaki,dabadan tasan halin ba baban ba da saitace saboda hidimar da yayi masu ce sanda yana asibiti yasa baiyyi shawara da ita ba yabadata. Haka tai wannan exam babu sukuni,amman tana kyautaya zaton ta rubuta abun kirki. Feea ta isheta da tambaya meke damunta taga yau bata da walwala ko kadan,tafe suke suna tracking don samun taxi feea bata zoda mota ba........."bazan ji dadi ba ina tare dake kuma ki kasa gaya mun damuwarki,bacin ni idan ina ciki kina kokarin ganin kin warware mun ita." "Ba haka bane feea kawai dai inaga bai dace na damu wani da damuwata ba" "Karkice haka koda banda abunda zan maki ai na maki addua ko" Shiru fiyah tai tana nazari,bazata sanar da feea abunda ke faruwa itada Abdoul ba,har gara ta gaya mata baba ya badata ba tare da sanin ta ba. "Feea baba ne ya bada aurena ga kanen uncle yahya,fea bana sonsa ban taba son sa ba ko sau daya,kwatsam yaje ma baba da batun son aurena shikuma ya amunce mashi kaitsaye." Zaro ido feea tai yana cewa"aure waye wannan mai sa,ar.........hararar da fiyah ta sakarwa feea tasa tayi shiru tana dariya. "Sorry gaskiya banji maki dadi ba,irin haka babu dadi su daman irin samarin nan idan sukaga sun kasa samo kanka da kansu kurin sai su kai maganar ga iyayenka,inda sun san wasu baza a ki ansar tayinsu na" "Bayaga haka kuma abunda na lura dashi feea yesmin tana son guy din,din sadda baba yake sanar damu maganar fita tai ta kware tana tari,dana bi bayanta kuka naga tanayi aboye,alamar meye haka feea idan ba sonshi take ba" Jinjina kai feea tai tace"tabbas haka ne ma fiyah,son shin take don haka inaga wannace damarki da zaki kubcewa aurensa tunda har kin tabbatar yesmin tana son sa." "Daman abunda na yanke kenan zanje ma mama da maganar muyita cikin fahimta nasan zata yi wani abu akai" Da haka suka tari taxi suka wuce gida,aranta tana kewar Abdoul gashi wayarta bata nan jikkar ma duka bai bata ba. "Assalamu alaikum" Fiyah tayi sallama cikin gidan lokacin karfe hudu daidai,mama na alwallar sallar laasar ta ansa mata tare da cewa"sannu da dawowa safiyya kinsha yunwa dai yau,tunda baki wani ci abincin kirki ba kuma baki anshi kudin abincin ba" Dakinsu ta nufa tana cewa"bana jin yunwa feea ta siya mana abinda mukaci" Tshige kurin don so take mamar ta fahimci tana cikin damuwa kozata fara tambayarta abunda gake damunta. Anan saita zayyane mata abunda ke ranta,yesmin ta gani tagama salla tana linke sallayar. "Adda sannu" Kallonta tai taga bata cikin yanayin jin dadi,ba haka ta saba ganin yesmin dinta ba,zata iya rantsuwa da bata taba ganin ta cikin irin wannan yanayin ba. "Yawwa sannunki kema yauba islamiyar yamma kenan" Abayar ta ajiye saman kofar dakin tana cewa"aa akwai nice dai bazanje ba yau ban yi hadda ba" Wannan yasake jaddada mata cewar yesmin na da damuwa sosai,don bata fashin islamiya kuma ba,a taba biyota hadda ba.duk sanda ta dawo zatai bitar haddar har saita iya sannan. "Amman jiya ba naji kina yi ba,kuma banji inda baki iya ba" Gajiya tai da tambayoyin addar tata ta haye doguwar kujerar dake dakin ta kwanta tana juya mata baya. "Yesmin ba dake nake ba" Cikin kosawa tace"yaya muhseen yazo dazun ya kawo maki wasu kaya suna wajen mama" Dogon tsaki taja tace"ba shi na tambayeki ba ai,ina ruwana da kayan daya kawo tambayarsa nai ina son wasu kaya?ko zindir yaga ina yawo,yama dawo ya anshi abunsa don bana so maye kurin ana turesa yana kawo kasan wlh zaigane wanda yayi ma shishshigi ni banson maita,nace banayi ko dolene" Jiyuwa yasmin tai fuskarta babu fara,a ko walwala kamar zatai kuka tace"Adda kibar zaginsa babu kyau kana aibata wanda yake sonka" Kallonta take tana mamakinta lallai yesmin tayi nisa sosai,don ta sake tunxurata tace"anje anzageshin idan yaji haushi yace yafasa,ina ruwanki ma da zagin sa danake da aibatashin banson shishshigi kinajina,angaya mashi zai siyeni da abun duniya ne wofi dashi kurin." Idonta cike da kwallah cikin sanyin murya tace"Adda tunda bakison sa kibarshi da haka amman kibar aibatashi banajin dadi wlh don Allah" Ta fada tana jiyawa tana goge kwallarta. Mamakinta kashe fiyah yayi tace"yesmin mekike cewa,sake maimaita wa don Allah in tabbatar ma raina." Kukanta ta jiyo kasa kasa tama rasa me zatai saidai murmushi ya kubce mata,Allah sarki yar salihar qanwarta ta shigo layin manya.indai sone abunda yafi kuka ma yi mashi zakiyi. Kaya ta cire ta shige wanka tana jin dadin yadda ta tabbatar da abunda take zargi kan yesmin din. Wanka tai da Alwallah tayi salla sannan tazo tahau shiryawa,riga da siket ne ta saka ta yi simple make up tasaka turare tafito tsakar gida. Mama ke shara ta ansa tana yi mata suna dan taba hira, "Babanku tunda kafa tafara takuwa yafice agidan nan,kinganshi har yanzu bai dawo ba" "Ai haka akeso mama inkinga mutun zaune kamar baba to ba lafiya ba,Allah ya kara mashi lafiya.wai mama yaya jalal lafiya baizo ba" "Yayanku wata yar matsala ce ta faru can wajen aikin,mataimakin principal yayiwa wata yarinya fyade,to matsalarce aketa fama da ita shiyasa yace said satin sama" "Innalillahi fyade vice principal da kanshi,Allah ya kyauta gaba to" Mama tace"ameen iyakarta kenan" Shiru fiyah tai tana nazarin maganar da zata yiwa maman. "Kamar kina da magana dani ko safiyya?" Murmushi tayi tace"mama ai yadda zaki fahimceni nake tunani" "Karki damu ni uwace koma menene zan fahimcenki zan kuma dauki hanyar da zata daidaita matsalar." "Na gode mama,dama akan muhseen ne" ******** "Innalillahi wa inna ilaihir raju,un innalillahi wa inna ilaihir raju,un hazbunallahu wani imal wakil!!! wayyo Allah na wayyo Allah na Abdullahi na cuci kaina,na zalinci kaina na cutar da Abdoul dina.na wulakanta mahaifiyarsa ina zanje da wannan alhakin mariya mariya mariya!!! Saina kasheki saina yi silar rayuwrki wallahi bazan kyaleki ba,,,,,.......kuka ya kubce mashi matananin rikitarwa da gigitarwa kama shi dady yayi ya rungume yana jijjigashi don tausayin dan uwansa ya saka shima kwallar yake,jibi yadda jikinsa yake rawa duba yadda bakinsa yake karkarwa..........."kayi hkr ka natsu karka jefa lafiyarka cikin matsala,ka cigaba da anbatar sunan Allah shine zai kawo maka sauki.kadaina kiran kabani ba laifin ka bane kowa da tashi jarabawar kowa da kalar kaddararsa kadauka cewa kaida Abdoul mariya itace jarabawarku itace kaddarar ku.don haka godiya zakayi ma Allah ka nuna mashi farin cikin ka daya nuna maka gaskiyar da tadauki shekara shidda tana binne,hakika Allah yana sonku tunda har turo maki yarinya mai hankali mai tarbiyya da sanin ya kamata tashiga cikin wanna hadarin domin taimakonku,gefe guda ka malik dan albarka yaron da bamu haifar ba,bamuyi

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});