Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 71

Chapter 71

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,272 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

masa komi ba yazo ya dauki hidimar dawainiya da gudan jininmu,alokacin da kai ka yanke alakarka dashi.haka zalika ga zakiyya itama ta taka rawar gani cikin wannan aikin,don haka wadanan mutanen biyu bamu da kamarsu yaya.ina rokonka kiyayyar da kakewa malam kabir el-ladan kajanye ka yafe mashi idan ma ya maka laifi,bacin ma nasan baimaka komi ba,kashige ma yaronka gaba wajen ganin ya samu wannan yarinya guda tsoka daya amiya,ita daya tamkar dubu don Alfah bashida yarinyar data dace dashi bayan ita.Amman saika kaskantar da kanka wajen mahaifinta saika nuna mashi nadamar ka sosai da danasanin abunda yafaru abaya.koda zaka shigar da wannan bukatar. Mariya da mamman wannan kabarni dasu karka dauki mataki karka shigar dasu kotu domin sunan familyn ka zai sake lalacewa,Alh kwangila kuma na kaina zan mikashiga hukuma shida sake aikata irin wanan ko acikin mafarki bazai ba,don haka muje na kaika gida karka nuna mata komi zandai kaika wajen mami kanemi afuwarta duk da bagangan haka ta kasance ba" Ajiyar xuciya yak sauke wa yana jinjina kai yace"Abdullahi bana in sunan familyna ya sake baci,don haka cikin sirri agabatar da su ga hukuma har xuwa ga alkali,bana son ayimusu hukunci mai sauki,mariya inda dahali walahi sonake ayimun gunduwa gunduwa da namanta Abdullahi.murmushi Dady yayi yace "karka damu koba ai hakanba zata dandana kudarta kuma Allah bazai barta haka ba." Anayin sallar magruba yayi wanka ya shirya cikin manyan kaya,yauce ranar dana ga Alfah yasaka manyan kaya don yana jimawa ainun kafin ya sakasu. Shimanshi yayi murmushi ganin yadda suka anshi jikinsa,sai annuri yake fitarwa kamar wani ango. Riga da wandone na farar shadda gizner yar dubu hamsin malik yayi masu dinkin da wata babbar sallar,tunda yaje idi dasu bai sake sakasu ba. Hannun mai links ne rigar iyakar guiwarsa wani fitinennen kamshi yake xubawa,ya taje kanshi malik ne yashigo yana kallonsa cike da tambaya kallon mamaki da al,ajabi yake mashi. "Mutumena ko anyi sabon kamune irin wannan hadewa gaskiya ko wacece na jinjina matsayinta,ni rabon dana ga kayi kyau irin yau bazan iya tuna wa ba gaskiya nawan" Yafada yana dafa kafadarsa cike da zolaya yana mashi dariya,murmushi ya iya mashi yace"karka fassara kwalliyata nayine don inji dadi insha iska kuma,badan wata ba ni bana yin abu don wani yaji dadi" "Uhmmm naji wannan to ga hula in aramaka don nasan ko guda baka da saboda baka son sakawa." Agogo yake daurawa yace"bana so rike kayanka idan inson sawa zanje insiya ne basai na araba" Hayewa yayi gadonsa yana cewa "ina zuwa don Allah" Wani banzan kallo yahi mashi yace"bana zuwa da kowa" Wayarsa ya dauka yana sawa ga aljihun gaban rigar ya dauki key. "Saina dawo" Dariya yayi yana cemashi "ka gaidata sosai" Baiko jiyo ya kallai ba yafito zakiyya na zaune tana kallo ta tusa abinci gabanta tana kallonsa ta kasa ci,kwalla ce ke fita daga idonta tana diga ga hannunta,ko kadan xuciyarta acinkushe take abubuwa sun mata yawa.bata iya bacci ko kadan tunaninsa da begensa sun mata tsaye ga rai,amman idan tatuna da cewar ba ta cikin shirginsa bata sanin sadda kuka yake kunce mata.haka zata raba dare tana kuka har sai kanta yafara ciwo sannan ta hkr tayi alwallah tayi salla ta roki Allah idan sonsa babu alkairi ya rabata dashi,ya kuma rage mata zafin kishim sa da takeji. Kamshinsa ya ankarar da ita yana tsaye kanta saurin saka hannu tai ta share kwallarta bata dago ba ta dauki plet din abincin wanda ko kwatarsa bata ci ba kuma bawani mai yawa bane. Tanufi hanyar kitchen jitai yacabe hannunta da babu komi..........wani abu ya tsarga mata tundaga hannun har tsakar kanta,runtae ido tai tana son sadakarwa amman xuciyarta na gargadinta da cewar tausayinki yaji bawai sonki ne yakejiba karki bada kanki zakiyya kibari inhr yna sonki a kanhi zai nemoki. "Meke damunki." Uffan batace mashi ba ta kwace hannunta tashige kitchen tana kuka kasa kasa. Ajiyar xuciya yayi yanajin babu dadi yadda yaganta cikin damuwa,komi kenan zai samu lokaci ya tambayeta. Fita yayi yashiga motar yabar gidan wani irin yaayi yake jin kanshi aciki,dokin ganin ta yake fiye da tunanin mai tunani amman baisan dame zaine mata ba,yasan dai jikkarta da sabuwar wayar daya siya mata sune suka karfafa mashi guiwar xuwa,amman baida wasu kalamai na musanman dazai fada mata yaja hankalinta suyi fira,amman kila idan idonsa yasauka akanta yaji kalaman sun sauka suma. Murmushi yayi wa kanshi inama ya dauko malik da zai samu saukin abun cewa shiya shi da magana bata kare mashi. Ko inda gidansu yake bai kalla ba yasamu waje yayi parking yafito,shagon dalha ya kalla yaga yana ciki wajensa yaje suka gaisa yace"don Allah abokina kashiga ciki kayi mun sallama da safiyyah mana" Murmushi yayi yace"to yallabai yanxu kuwa" Ya Vito yashiga gidan da sallama lokacin baba ya dawo duk suna tsakar gidan banda yesmin dake can daki,duk yinin yau taki fitowa saboda taji maganar da fiyah take gaya ma Mama. "Baba ana sallama da fiyah" Wani irin duka kirjinta yayi mama ta kalleta shima baban kallonta yake cikin alamar tambaya yace mata"waye" Sorry for let update fat an kuna lfy ina gaida kowa da kowa.✍🏻 [9/25, 5:29 PM] Mom Muhseen: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSEER* *(ALFAH)* WRITTEN BY MRS BB MOM MUHSEEN FOR SALE 300 NAIRA ONLY 09034722970 🅿️...........51 Fiyah kamar mai hadiyar kunama sai zare ido take gabanta yana faduwa.saida ya sake maimaita tambayarsa idonsa akanta yace"bada uwata nake magana ba?nace waye ne" Kyafkyafta ido take tace"baba......ban....ban san ko waye ba wlh" Jiyowa yayi ga dalha yace muje inga kowaye. Tashi yayi suka nufi wajen yana zaune saman bencin dake bakin shagob dalha yana sauraren radio din da dalha ya kunna,yana ganin baba yayi saurin tashi yana jin wata irin kunya da giltness yana kamashi,sadda kai yayi yana shafa sumar sa cikin ladabi yace"ina wuni baba" Baban kallonsa yake a natse yana ayyana yadda ya koma,don yasha ganinsa ahanya baya ma cikin hankalinsa yasha ganinsa zaune bakin titi ko kaganshi akwance cikin yanayi marar dadi,amman yanxu sai yaga natsuwa da kamala ta kamashi.ga wata yar kiba dayayi kuma cikin shiga ta mutunci ta hausawa. Daker baban yace"lafiya lau wa kake nema" Shiru yayi yana mulmula maganar tome zaice,yazo zance ko yaya zaice tunawa yayi da jikkar fiyah da wayarta yace kanshi kasa "daman jikkarta ce data fadi tun rannan da wayarta ne nataho mata dasu,sannan na dubata a jiki" Jinjina kai baban yayi yace"yayi katabbata sukadai suka kawo ka?" Inama zai iya furta abunda yake karkashin ransa ga baban,inama zai iya cewa baba kaban ita kaban iznin nemanta........amman ina maganar tafi karfinsa yana jin nauyinsa fiye da tunani. "Eh shikenan" "To yayi zata zo ta ansa amman daga yau karka sake xuwa don Allah,domin idan wanda naba aurenta yazo yaganku zaiji babu dadi" Wani abune yatsaya mashi ga wuya,dandanan yaji kanshi ya sara mode dinsa najin dadi dayazo dashi yana guduwa yana barinsa,daker ya hadiye wani miyau kanshi still yana soke akasa yace"insha Allah" "Allah yayi Albarka mungode da dawainiya" Kasa ansa adduar yayi yaji dadinta amman dacin dake bacinsa da ciwon dake ransa ya hana shi ansawa. Juyawa baban yayi yashige gida. Bayan fitar baba mama ta kalli fiyah tace"kigaya man gaskiyar abunda yaje tsakanin ki da yaron nan safiyya,karki kwari kanki" Kanta akasa taji duk ta

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});