Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 30

Chapter 30

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,268 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ta anbaci zakiya wani irin dum taji tana sake ware duk idonta akan feea kafin taja hannunta tace"feea kin tabbata ita zai aura." Jinjina kai tayi "wlh kau fiyah kinga ma invitetion nan." Ta zaro ta nuna mata gashinan zakoya muazzam and Alh jamilu badaru (kwangila) Cikin tsananin mamaki ta kalli feean tace"insha Allah baza ai auren nan ba,karki damu zan taimakeki ki kwantar da hankalinki" Zakiyya!zakiyya!! Abunda take nana tawa kenan tana da tarin tambayoyi sosai amman zakiyar kawai ce zata ansa mata su,kallon ajinsu tayi babu malami ta kalli feea sannan tace"kije class ga shi can inajin ma last test zakuyi,zamuyi magana kicire komi aranki." Haka suka rabu fiyah ta shiga class dinsu ta samu waje ta zauna tunani ta shiga yi. "Zakiyya na son auren ko aa,in har bata so wane dalili ne yasa zata aureshi wanda ya haifeta sau uku ko hudu.kai bama yarda zai zakiyya ta so auren sa,lokaci guda bai isa ta manta da nasser ba har tayi wani auren..........haka akai wannan lecture daker taba da constretion dinta ga abunda ake masu tana yi tana jotting,ganin abunuwan suna da amfani sosai kuma tasan shi tsaf zai iya makosu cikin questions din exams. Tayi mashi tambayoyi sosai tana yi tana rubuta duk abunda yake sake mata bayani.......sai sha daya suka fito waje ta samu ta zauna koda taga sakon malik share wa tayi.don ba shine gabanta ba bata ma duba shi ba, No din zakiyya da tayi save tun jiya ta shiga lalubowa ta kasa kunne taji kozata shiga,cikin sa,a ta shiga tana ta ringing saida ta kusan katsewa sannan ta dauka . "Hello,wake magana" Ajiyar xuciya ta sauke tace"Sunana safiyyah,don Allah ina magana ne da zakiyya muazzam." Cikin tabbatar wa tace"yes I'm zakiyya,who is safiyya mekikeso." Fiyah tace"no tukunna dai yanzu dai magana nake son nayi dake amman ba awaya ba,ki saman time sai nazo na kiyi mana wajen da xamu hadu,maganar is very important awajen ki.bayan haka pos dinki da kika yar a bakin bank tana wajena." Cikin dokantuwa tace"plss ina Central park kizo mu hadu yanzu don Allah saboda banda isasshen time ina hidimar bikine." Fiyah tace"no yanzu ina makaranta kuma kona tashi banda time akwai ayyuka da zanje nayi kisamu lokaci kedai,inkin yanke time kikirani sai anjima." Ta yanke wayar tana jin insha Allah komi zaizo da sauki,don naga alamar bata da zafin kai irin na yaran masu kudi. Sakon malik ta shiga dubawa tana jin kirjinta yana bugawa,bata son ganin kalaman nan nashi wlh tada mata hankali suke. Ilai kuwa sune _Kyakkyawa acikin kyakkyawai fatan kin tashi lfy,jiya kin gudu kin barni da jimami Allah yasa dai kalaman malik basu hanaki bacci ba_ Runtse ido tayi tana fita daga cikin text app din. Tana tsogumin wannan sabon salon na shi,wata qawarta ta iso tana cewa "Fiyah ana nemanki wani guy ne gashi can bakin department." Zaro ido tayi tana binta abaya aikuwa malik ne hararar sa tayi shikuma yana mata dariya, "Amman meyasa bak kirani ba zaka zo har nan baka san yanzu mutun ake kiwo ba ba dabba ba.idan wani yaje ya kai labari ga baba ko yaya jalal fah." Kama kunnesa yayi duka biyun zai durk'usa tai maza tatare shi har suna karo danjuna. "Meye haka yaya malik,don Allah ka daina muje idan magana ka keso dani amman ba nan cikin mutane ba wani dan sa idon yana can yana gulmata fiyah tsaye da namiji." Dariya yake yana shigewa gaba tana bin bayansa wai gowa yayi yace "wai tsoron aganmu tare kike?" Bata kalleshi ba tace "yaya malik kenan don baka san yan sa ido ba,to yanzu wani nacan yana cewa ashe dai safiyya el-ladan ashe daman musulmar karya ce kuganta can tare da saurayi bayan bata tsaya wa da kowa duk makarantar nan." Me malik zai banda dariya kallonta kurin yake yace"Ashe dai qanwata ba wasa har tsoron tun kararki ma ake,to miye idan anganni dake ba sai kice yayanki bane." Jinjina kai tayi tana rik'e haba tace"uhm yaya malik kenan wlh wata ko wani nacan suna mana kallon masoya raba kanka da mutane." Daidai isowarsu bakin motarsa ya juyo yana rungume da hannun sa ga kirji ya zuba mata mayatattun idanun sa. Shiru tayi tana neman hanyar buya daga idonsa dake mata wannan kallon da bata so,yasha gabanta yana murmushi mai sauti leko fuskar yayi yana son su hada ido dariya yayi ganin ta runtse idonta. Motar ya bude mata yana cewa"bismillah gimbiya safiyyah." Wannan suna ya shigeta har saida ta kallai cike da mamaki,shi kuma ya kanne mata ido guda tai saurin shigewa motar tana jan numfashi. Dariya yayi yazaga yashiga suka bar makarantar. Don ma kar yayi anfani da yin shirun ya sake yi mata abunda bata so yasa tace. "To da bangama lectures ba fa" Hankalin sa naga tukin uace"ai dayake ma nayi sa,ar kun gama." Rausayar dakai tayi tace"ina zamu yanzu to." Kwana yayi yana cewa"siyen flower,wace kala ce tafi yi maki kyau cikin flower." "Yanzu wannan flower da tsiya sai ansiyeta, don Allah nidai kabarta kasan halinsa yanzu haka muna isa karshe kila ma dani da ita zaiyi watsin ala tsine damu cikin mutame." Dariya yayi yace "karki damu Allah bazai maki ba." "Hum to idan yayi manin fah" "Saki rama kaina" Dariya tayi "da haka kace sai kiyi hkr,inbanda abunka ina ni ina iya bugunka ai saidai kabarni da ciwon hanu." Hirar su suke har suka isa wani waje da flowers din kawai ake siyarwa zalla,gasunan gwanin sha,awa sai wadda ka keso........tunda suka tsaya ta hango wata pitch color and dark pink color,dance danan taji ta burgeta inda take kalla yabi da ido yayi murmushi yafita yabarta. Inama ace mutumen kirkine zata ba kuma in ta bashi ya ansa cikin jin dadi da annashuwa,wanda tasan har abadan bazai yada ba saidai idan yabarta inda zata bushe,da tace ya dauko wadda ta gani don tayi bala,in burgeta Amman bazata so taba wanda baisan mutuncin mutame ba,banda yunkurin kisa bai iya komai ba saifa zafin ran banza. (Nikau nace uhmmm gaba dai gaba dai ansafiyyan malik😊) Dawowa yayi da ita rik'e ga hannu,an sakota cikin wata fation leda mai zanen flowers din. Banda kamshi babu abunda take duk ta cika motar da kamshi,mamaki da al,ajabi ya rufeta ganin wadda dai taketa santi itace ta siyo baki bude take kallonta Kasa cewa komi tayi murmushi yayi yace "baki ce tayi kyauba." Kauda kai tayi gefe"yaya malik ba kyau ake nema ba ai,fatan da ake abashi ya ansa cikin girmamawa shine kawai bawai kyau ba." Kunshe dariyar sa yayi yaja suka bar wajen. Tunda suka tunkari airport din kirjinta ke amsa wa,tunda take tunda tafara wannan aikin wahalar bata tabajin faduwar gaba irin ta yau ba,duk sai taji ta diririce tun ma kafin suyi ido hudu dashi...........kallon sa tayi cikin raurau da ido don har gobe bata mance wahalar da ya bata tace"yaya malik nidai bazan iya fita ba kaje kai dai wlh ni tsoro nake ji wlh." Ajiyar xuciya yaja yace"relax safiyya,karki saka tsoro nace maki bazai maki komi ba ai yadauki fada na" Ajiyar xuciya ta sauke tana sake jin gabanta yana faduwa. Fitowa sukai daidai sana akafara sanarwar saukar jirhin.duk atsorace take kamar ace kes ta ruga da gudu.........ahankali mutanen suka

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});