Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 83

Chapter 83

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,270 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kan kudine da bazai bayar da anty jamila ga uncle yahya ba,tunda shima kudin garesu sosai. Amman bazata iya ja da hukuncin mahaifinta ba,koda hakan na nufin dawwamar bakin cikinta. Yesmin ce ta shigo ta zauna kusa da itana rungumota jikinta tace"plzzz Adda kibar kuka insha Allah baba zai fahimce abunda ke ranki insha Allah zai amunce dashi.tunda abunda ake zarginsa dashi karyane sharrine naji anafada rannan.kiyi hkr kiyita addua idan darabon ku kasance tare baba zai sauko zai hkr yabaki shi.zantaya ki addua kibar kukan Adda nima zaki sani" Rungume juna sukai suna kukan tare,mama na tsaye bakin kofa tana jinsu,badai ta shigo ba tasan za,a rina tasan safiyyah tajima tana sin wani kuma tasan ba tun yanzu suka san juna ba. Juyawa tai ta koma daki don bata ga fuskar yiwa baban su maganar komi yanzu ba. *********** Mamaki yasha yadda aka canza komi na part din ya koma sabo,don yadda yaji bakin ni ima yau akai fenti aka saka sabbin komi na wajen rungumeta yayi yana jin dadin dawowa cikin family dinsa,gefe guda ga sahibarsa ta gama wanke duk wani datti dake xuciyarsa. Shida malik gaba yau falon Abbi akai zaman fira ga mami ga Abbi ga ni,ima sai malik din,zakiyya tana ganinsa tatashi tabar falon baice komi ba don daman yasan za,ai haka amman soon zata sauko idan yayi lallashi. Duk abunda suka faru aketa bita wasu ayi kuka wasu ayi dariya,anan duk sukai dinner basu tashi hirar ba sai shabiyun dare. Anan Abdoul yake tambayar ina su Amina Abbi ya bata rai yace "suna can shashensu yabasu sati biyu su fiddo mazaje duk ya aurar dasu idan ba hakaba wlh ya rantse saakarsu zai bayar. Baice komi ba o aure ne shine ya dace dasu. Mami da ni,ima sukai daki don bacci sukeji akabar malik da Abdoul da Abbi suna tattauna wa game da duk dukiyarsa da umma taso rabashi dasu,har wadanda yariga yasaka mata hannu amman baikai ga bata ba. Nan suka tsara yadda abunuwanshi duk zasu dawo yadda suke basu tashi ba sai biyun dare. Duk maitar shi akan jin muryarta hkr yayi don yasan tayi bacci. Baisan fiyah tana can tana kuka ba,idan ta gaji tayi tagumi tana tunanin yadda zata rabu da Abdoul. Yashiga jininta da bargonta tamkar fitar numfashinta takejin soyayyarsa,lokaci guda kuma baba zai mata haka. Kashe wayarta tai don bazata iya ganin kiransa ta ki daga wa ba. Washegari kamar marar lafiya ta yini don ma exam din sai yamma haka ta yini daki,saiga yaya jalal ya dawo Anty jamila kuma tazo. Ranar yini tai tana surfa ma fiyah bala,i don taki muhseen shima yaya jalal din yana tayata.kuka kau idonta har ya kumbura,bata kara takaici da bakinciki ba saida maganar Abdoul nasser ta fasu duk suka sani ai kamar zatai tsuntsuwa tabar gidan haka taji. Don yaya jalal yace wlh idan yasake ganinta dashi ko aka gaya mashi anganta dashi saiya balla mata kafafu. Mama dai najinsu saida taga abun naneman zama hauka tace duk wanda ya sake mata fada akan haka saota bata mashi rai.miye laifin yaron kawai don anbata sunan sa shine kurin zaku tasanmata,to karta sakejin bakin kowa akan maganar. Wanna ranar fiyah bata san ma meta rubuta ga exam din ba,tasandai ta yi tubutu amman bazata iya cewa daidai tayi ba ko akasin haka,har dare bata kunna wayarta ba Abdoul nacan duk ya rude ya fita natsuwarsa,saiyazo xaiyyi sallama gidan saiya fasa kasa zama office yayi don tashin hankali,maganarta tajiya yake tunawa kardai baban nasu ya dakatar da ita akanshi.inko hakane dole ne yau yaje ya fuskance shi............daga jiya zuwa yau fiyah ta fita natsuwarta bata iya cin wani abun kirki data fara zata ajiye ta shige daki......mama duk tashiga damuwa kuma har yanzu baban daure fuska yake don yasan zata ce mashi wani abu.............bayan salar isha,i yagama cin tuwon masara da miyar kubewa danya da mamar tayi,har lokacin fuaka abace duk gidan ya zama babu dadi saboda abunda yafaru. Dalha ya shigo bayan ya gaida baban yace"kayi bako awaje yana son ganinka" Kallon dalhan baban yayi yace"waye" "Dan gidan Alh........katseshi yayi yace"cedashi ya shigo" Fiyah na daki tana jin haka dandanan wata masassara tazo ta rufeta,kirjinta yana duka me baba zaice mashi innalillahi nashiga ukuna Sallama yayi yashigo cikin wani yadi marar nauyi yayi kyau sosai,ya gaida mama dake bakin famfo ta asa cikin kulawa. Kafin baba yayi mashi iznin zama ka tabarmar dayake bisa. Yaya jalal ne yashigo yana ganinsa ya hade fuska,Abdoul bai damuba ya mika mashi hannu,Daker ya amsa mashi gaisuwar dayake mashi. [10/11, 7:23 PM] Mom Muhseen: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSEER* *(ALFAH)* WRITTEN BY MRS BB MOM MUHSEEN FOR SALE 300 NAIRA ONLY 09034722970 *kafin muci gaba zanyi wani bayani.akan masu ganin ban kyauta ba dan nasaka Alfah bai auri zakiyya ba,harda cewa ina nuna duk girman laifin mutun ana yafita yes duk girman laifinka idan katuba ga Allah yana yafe mana,haka zalika niban nuna cewar Alfah bai yafewa xakiyya abunda tai ba,tariga ta sanar dashi komi kuma yafahimceta yace ya hkr komi ya wuce,sannan badole sai Alfah ya auri zakiya ne hakan zai nuna ya yafe mata ba.abunda nakeson kugane nifa labarina gaba dayansa akan Abdoulnasser da safiyya natsara shi,duk wanda kukaji sunansa to daga jikin daya daga cikinsu ne,kuma nayi hakane don na nuna cewar ba komine kake nema ka samu ba.duk sonka da abu idan babu alkairi tsakaninku Allah zai iya hanaka,haka duk gujewarka da abu idan rabonka ne dole zai kasance.ita rayuwa haka take xuwa ku kalli yadda abubuwan suke faruwa ko a reality zakiga abunda kikeso bashine yake kasancewa ba,wanda bakinson shine alkairin ka akan kanki ma idan kika duba abubuwa dayawa dakikeso baki samesu ba kuma karshe wanda bakison shine alkairinki.don haka ina mai bawa masu challenging dina hkr akan cewar haka labarina yataho,haka zai cigana da tafiya idan anan anbata maka wani wajen ana faranta maka.haka rayuwar take idan nan kaji dadi ba dole can kaji ba,idan yau katashi da lafiya gobe ba lallai kajika normal ba.don haka kubarni na tafiyar da labarina ayadda yake,haka natsara haka zai tafi plzzzzz idan wata ta kullaceni har tana ganin ta yi asarar kudinta ina bata hkr,nidai don wata kodon wasu bazan fasaba bakuma zan canza idear ta ba ina godiya sosai da challenging wannan yanuna man cewar duk yadda kake faranta ma dan adam duk ranar daka kuskure mashi to hakan nanufin sauran daka faranta mashi zaimanta dasu ya gaya maka magana.ngd ngd sosai da hakan na sake samun experience ahakan,daman arayuwa bakowane zakaima daidai ba nabarku lfiy BISSALAM* 🅿️...........59 "Zauna sosai magana zamuyi dakai." Baba yacewa Abdoul dake yakejin dukan kirjinsa yana karuwa. "Meke tafe kai tukun karna katse maka hanzari" Sadda kai yayi yanajin kamar ya tashi ya ruga amman muhimmancin safiyya arayuwarsa yafi gaban nan,wannace damarsa idan yara sata baisan ya zaiba. Cike da ladabi yafara magana cikin natsuwa "baba nazo ne akan kaban iznin xuwa wajen safiyya,inasonta na yaba da halayenta nagari da hankalinta da natsuwarta don Allah baba karkace aa." Yafada muryarsa tayi rauni tausayinsa ya cika xuciyar mama,jalal kuwa sai wani harararsa yake yaja karamin tsaki yace"kayaba da tarbiyyarta kaikuma fa,taka tayi daidai da tata kaga akwai tazara tsakaninku" Dago jajayen idanunsa yayi ya xuba mashi su yaajin zafin

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});