Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 14

Chapter 14

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,289 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kare ba,har gajiya nai da kwanciya haka dai har gari ya waye,na fita buge bugen dana Saba,don wanan kudin bai hana ni fita nema ba. Still titin na nufa na hanyar lugbe na had'a omona ina wankin glass Ana bani naira dari...........inata aikina har sadda lokacin tafiyata yayi shagona na koma na unguwar gwagwalada nashirya na hau taxi zuwa maitama estate. Numfashi ya sauke idonsa akan na fiyah datayi shiru ta na saurarensa yace"kinga munsaki layin Maigida Abdoul-naseer mun Kama wani ko,inason na baki ansar tambayarki kafin mukoma ga asalin abunda ya zaunar damu kafin lokaci yayi." Gyara zama tayi fuskarta duk tayi kalar tausayi tace"yah malik kenan duk hasashena akan alakarka da.....Abd...abokinka Ashe ba haka bane inson inji naka labarin rayuwar don har ciki xuciyata ahaka ma ya nuna mun kasha wuyar rayuwa." Ruwa yasa Mata ya mik'a mata yana murmushi Mai kyau da tsari yace"abun kuma yayi mun yawa hajiya sofiyyah,kibari na karashe maki na mutumen mana tunda naji sunansa ma wuyar fada yake maki." Dariya ta d'anyi tasha ruwan kad'an tace"uhm Ina jinka ka cigaba." Cigaba yayi da cewa"sanda muka isa unguwar daker jamian tsaron dake area wajen suka barni na k'ara gidan,don card din daya bani duk address din naciki. Sanda naga wannan daula ta gidan numfashina saida yaja,najinjina irin mahaukatan kudin da aka narkar wajen,maigadi nagaida yana tambayata wanake nema. Kallon card d'in nayi nafada ma shi sunansa yace to nazauna nan bari yaje yasanar dashi aciki. Inanan zaune yaje ya hadawo yace muje nakaika masaukin bak'i,haka nabisa baya Ina sake kalle gidan kamar Wanda yazo daga riga. Haka nazauna tsawon awa guda cikin wani tsalelen falo sai fitar da ni'ima yake ga k'amshi kamar me. Amman fa ankawo mun lemo da kayan cinye cinye. Babu jimawa saiga shi ya shigo fuskar nan kamar gonar auduga,sai Fara,a yake tashi nai Ina mayar mashi da martanin murmushi Zan zauna k'asa,saurin rik'oni yayi yace"haba dai abokina,meye haka tashi don Allah zauna anan kusadani." Haka muka zauna kujera guda ya mik'o mun hannunsa mukai musabaha. Bai jani da nisa ba yace"hakikanin gaskiya abokina na yaba kwarai da hankalinka da natsuwarka da kuma jajircewarka,gaskiya ka burgeni kabani sha,awa domin ba kowane matashine kamar ka zai iya yawon siyarda card ba,sanan ba kowane zai iya yawon wankin glass ba Ana bashi naira dari har yayi godiya ba." Kallonsa nai nace"ka ganni rannan ne yallabai." Kafad'ata ya dafa yana dariya yace"bama rannan ba ABDOUL-MALIK na sha ganinka different places,naganka kana jan taxi don har dauka ta kayi,sanan kayi gadin NI'IMA MEMORIAL SCHOOL kafin akoreka,sannan ka siyar da youghout da purewater.......duk nasani,dalili kuwa shine nasa ana bibiyar Mani Kai." Idona kamar zai fad'o nake kallonsa cike da mamaki daker na iya cewa"yallabai.......not yallabai kakira ni da ALFAH ko ABDOUL-NAS don inajin dadin sunyen fiye da tunani." Shiru nayi Ina jinjina karamci da mutunci irin nashi kallonsa nasa ke yi nace"Amman taya haka,menayi maka mai dadi yasa duk haka tafaru." Donet d'in dake cikin bowl da aka kawo Mani ya dauka ya gutsira yace"ranar da ka d'aukoni motatace ta tsaya nabaro driver DA maigyara bakin hanya nikuma na tsayar dakai ka kawoni gida. Akan hanyar ne naji wani Wanda kuka gaba dashi yana ce maka,malik kadai baka gajiya yau kaine wannan aiki gobe kaine wancen,wlh ni bazan iya wannan wahalar ba duk inbi inkare ga aikin wahala.gara inzauna har sadda aikin office zaizo,Kai ko kunya bakaji wace mace xata soka kana wannan Sana,ar haba shiyasa duk aka gujeka." Ansar daka bashi ita ce tayi masifar yimun dad'i cewar dakai. "Ai babu babban malalaci irin Wanda zaikwanta sai anciyardashi sannan kake maganar wahala,duk namijin dayasan ciwon kanshi dole yayi wahala wajen Neman nakanshi,sannan aikin office daka ke magana,inhar ba hanya gareka ba bakasan wani ba babu ta yadda za,ai kasameshi kuma ni na gode ma ALlah daya bani rai lafiya da nake iya Neman na kaina har na iya yiwa wani alheri. Basai naje nayita maula ana cimun fuska azagan azagi iyayena sannan aban awulakance,ahaka ahaka Allah zai bud'aman don yace tashi in taimakeka." Wannan maganar itace tasa naji kayi masifar burgeni kuma naji sha,awar taimakon ka saida nasa akaringa bimun Kai aka tabbatar mun da Cewar kai din jajirtaccene kuma jarumi Mai yin iyakar kokarinsa don ganin ya rufa ma kanka asiri.wannan yasa nace Zan taimakeka zaka zamo abokina aminina kuma d'an uwana,don haka daga yau kadawo d'anan gidan kuma kai zanba wa amanar company nina da store Dina,don nauyin dake kaina yayi mun yawa,Amman tamabayata anan malik itace inane asalinka kuma ina iyayenka,sannan miye matakin karatun ka?.............. 😊sorry wlh banda caji Ku hadu gobe. Comment and share Mrs bb ce Mom muhseen. [9/17, 3:36 PM] Fauziya Madaki: πŸ’žπŸ’žπŸ’žπŸ’žπŸ’žπŸ’žπŸ’ž *ABDOUL-NASSER* *(ALFAH)* WRITING BY. MRS BB MOM MUHSEEN. WATTPAD NAME HUMAIRA7531. *DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB AND ALFAH FANS* πŸ…ΏοΈ.........12 "Nisa wa nai nace mashi iyayena sun rasu,tun ina dan shekara goma a duniya,mu y'an Asalin katsina ne anan iyayena suka yi aure har suka haifeni ni kadaine d'ansu watarana b'arayi suka shigo mana suka kashesu,suka sama gidan wuta Allah kadai ya rayani bacin bakar wuyar danasha asibiti.saida nayi wata uku kwance,wata diyar yayar babana ta yi jinyara,itace ta cigaba da rik'eni har Allah yasa na mallaki hankalin kaina.ninake dauwainiya da kaina in biya kudin karatuna,babu irin sana,ar da ban ba ahaka har na samu nasarar shiga jamiar yar aduwa university.anan nayi karatuna na business administration,Alhamdulilah nasamu result mai kyau ina yin graduation mijinta yace inzo muje abuja inda yake kasuwancin sa,ahanyarmu ta zowa aka kirasa matarsa da d'ansu mota ta banke su sunrasu. Juya wa mukai muka koma akai zaman makoki naji wannan mutuwa kamar kamarme nadade ban dawo daidai ba,karshe shi bai dawo abuja ba sainine na biyo hanya nazo na kama hayar shago inda yan kudina naja jari nacigaba da yan buge buge na.kaji asalina kaji karatuna yanzu haka banfi shekara biyu dana gama service ba.inanan ina tara kudi zan koma masters." Jinjina kai kawai Alfah yake yana kallona kafin yace"gaskiya kai namijin gaskene malik ka burgeni Allah yajikan iyayenka yakuma gafarta masu da ita ma marik'oyar taka,abunda za,ai tashi zakai muje part dina kaga d'akinmu don gado daya zamu ringa kwana,zan gabatar dakai wajen mami da Abbi idan ya dawo don tuntuni nayi mashi maganar itama mami harta zak'u da son ganinka inyaso anjima ida kahuta saimuje kakwaso kayanka zuwa safe saimu fita muje kaga komi yadda yake,fatan zaka daukeni kamar d'an uwanka na jini don ni tun randa na fara ganinka ka kwanta man Arai naji ina sha,awar taimakonka don allah malik kazama mai rikon amana karka bari wani yabiyo ta wajenka ya cutar dani,zan iya yafe komi amman banda cin amana banda munafurci Don Allah ka kula,Allah yabamu sa,a ya karemu daga makiya." Tundaga ranar nazama d'an gida mami mahaifiyarsa jitake dani kamar dai Alfah haka ni'ima yaya sama yaya k'asa,haka wajen Abbi ma na samu karb'uwa sosai don min saba kamar yadda yakeyi da Alfah haka nima yakeyi dani,saidai bangaren umma ko kusa hakan yayi wuya,itadasu zuwairat kamar su cinna man wuta zakiyya budurwar Alfah kawai muke gaisawa sosai ta dalilin kaunar da takewa Alfah,soyayya suka buga kamar zasu cinye juna,basa iya yini zungur basu ga juna ba ko basuni muryar juna ba,duk irin yadda Alfah yake

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});