Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 43

Chapter 43

Abdoul Nasser Alfa Book 1 Complete Hausa Novel 1,273 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Allah bata so ransa yabaci ba, Kallonta yayi yace"kije mana" Kamar Mai tausayin asa tatashi tafara nufar kofar fita,dariya yake son yayi amman baison tagani. Waigowa tayi kamar zatayi kuka tace"yaya malik karya dakeni,karya zuciya ya mun tsawa." Girgiza mata kai yayi yace"bazai maki haka ba kidai bashi hkr kisamu yadawo ya ci wannan garar don wlh yamun dadi sosai maza jeki" Haka ta bude kofa ta fita aikamar jira yake ta fitan ya dunga kwasar dariya,lallai tarkon nan yayi kamu sosai,insha Allah komi zaizo da sauki. Yana cikin mota ya kwantar da kujerar zaman banza ya kwanta ya rufe fuskarsa da fesin cap di sa. Jikinta wani irin sanyi yayi ahankali ta kwankwasa glass din window din,tunda ta tsaya kamshinta ya iskoshi jiyai xuciyarsa na mashi kai kawo,ahankali ya sauke glass din baiyi magana ba baikuma dago ba,lawallar kuda ta kamayi tarasa abun cewa bakinta rawa yake wana mutun yana ata kwrjini cikin kwana biyunnan. "Sauro yana shigo mun inbakida abun cewa plss zan rufe glass dina" Bakinta yana kerma muryarta kamar zatai kuka tace"pl....s kayi hkr.....karka tafi kadawo don Allah" Wani sanyi dabai san daga inda yake ba yaji yana sirarowa cikin ransa,amman sai yayi shiru yana adduar Allah yasa ta sake bashi hkr karta tafi. Bata san dalilin hawayenta ba muryar na rawa tasake cewa"plssss kaji,im sorry........"maganar ta katse sanda kukanta yake fitowa Wani suka yaji ga kirjinsa jin muryarta na fidda sautin kuka,ahankali ya tashi jiyake kamar anzare mashi duk wata lakka daga jikinsa muryarsa kamar tafito daga cikin frig yace"come in" Ahankali ta zagaya wajen zaman driver ta shiga kanta akasa hawaye na bin fuskarta,tunda yake rayuwarsa bai tabajin kwatan kwacin irin halin dayakeji yanzu ba.koma wa yayi ya kwanta yanajin wani irin yanayi na sake bin gabbansa. Ahankali take sharar kwallah,inza,a yankata bazata iya cewa ga dalili ba. Hanky taga ya miko mata babu musu ta ansa tana kaishi ga fuskarta,wani kamshi ne ta shaka daya saka taji duk wani kunci na xuciyarta yaya yaye,ahankali take share kwallar har ta samu kwallar ta tsaya. Sannan ta mika mashi bai ansa ba yace"nabar maki" Tanajin yadda xuciyarta take bugawa numfashinta kanshi ya canza salon fita, Kamar mai koyon agana tace"kazo muje kayi hkr ko lemun kasha don ku akai" "Danshi dai,ni awa za,ayi abu danni daman ban saka ran samun tarba daga gareki ba saboda baki daukan mutun ba" Juyowa tayi duk da ba ganin fuskarsa take a tace"amman ai nabaka hkr ko" Murmushi yayi yace"baimun ba kije kawai ngd kin baroshi shimadai bacin dnke yazo" Kamar zata rushe da kuka tace"plsss mana kayi hkr to" Malik ne yafito shida uncke suna hira cikin fara,a duk sai taji ta kunyata. Fitowa Alfah yayi itama ta fito tana jin kunyar uncle tasan dole zai dauki wani abun,tunda gasu acikin mota su biyu. "Tunda kunya ta hanaka cin kayan tarban bakon Abokina gashinan na saka an yimaka takeaway dashi,don Allah karkace bazaka ansa ba tasha wuya fa wajen hada maka" Duk uncle ne yake wannan maganar. Kanta akasa malik ya isa inda take cikin kasa da murya yace"qanwata kuka kikai mashi" Tabe fuska tayi kamar zatayi kuka tace"kai yaya malik shine fa........kasa magana tayi tana sadda kai" Dariya malik yayi yace"qanwata gaya mun meyayi maki yasaki kuka" Kasa ansa shi tayi don bata san ma me zata ce mashi ba. Hanyar shigewa tayi zata shige gida uncle yace ah safiyya bakiyi sallama da bakon naki ba,xokuyi sallama aimun gama maganar." Sake musabaha sukai dasu yakoma cikin gida yana cewa maigadi idan ta shigo arufe gidan. Malik tuni ya shige mota yana jiransu kasa motsawa tayi daga inda take saidai shine ya isa inda take,ta juya baya ya tsaya daga bayanta. Tsayuwarsa yasa taji kamar ta koma kankara saboda wata irin mutuwar jiki tasame ta. "Goodnight amman karki manta banyi hkr ba,zan tai da cewar nazo kin wulakanta ni saboda..........juyowa tayi kadan yahana ata fda kirjina ba tayi saurin dan ja baya, "Don Allah..........lumshe idonsa yayi yana girgiza kai wanda kadan yahana numfashinta bai kare ba. "Goodnight" Haka yabarta kamar anshuka ta har motar tabar kofar gidan sannan ta samu karfin guiwar daga kafarta tashige. Wannan dare xukatan mutane biyu basu huta ba. Mrs bb Mom muhseen. [9/17, 3:38 PM] Fauziya Madaki: 💞💞💞💞💞💞💞 *ABDOUL-NASSER* *(ALFAH)* WRITING BY. MRS BB MOM MUHSEEN. WATTPAD NAME HUMAIRA7531. *DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB AND ALFAH FANS* 🅿️.........31 Washe gari da wuri suka gama soyen raguna uku,zuwa karfe biyu na rana sun gama dan ma Suna da dan yawa kuma kasko uku sukai,duk yadda fiya take kwari kwari saida Inna balaraba da Anty jamila sukai mata magana ko bata da lfiya,saboda yadda duk ta zama sukuku,bacin sun santa da kazar kazar da yawan magana wani bin. Tun safe take tsammanin wayar zakiyya amman shiru kuma ta kirata bata samu ba,duk saitaji gabanta yana faduwa Allah yasa ba wani abunne zai faruba,haka taita tsammanin kiranta har karfe uku na rana. Daker ma taci abincin rana kadan kadan ta duba wayarta taga ko zata ga misscall amman shiru. Saida akai sallar la,asar ta sallame kenan taji karar wayar zunbur tayi ta jawota Kosallama batakai dayi ba taji muryar zakiyya tana magana cikin tsananin tashin hankali, "Fiyah........kina ina fito yanzu fito don Allah ki saman hanyar shoprite.......babu lokaci kifito don Allah akwai babbar matsala" Jikinta ya dauki karkarwa tace"ganinan zakiyya kiyi kokarin boyewa biyoki akai ne" Muryarta da alamun kuka take tace"eh biyoni sukai gasu nan bayana ina cikin mota na samu waje na lab'e kiyi sauri bari na turo maki inda zaki saman." Kashewa tayi tatashi zunbur ta canza abayarta ta suri wayar tafito falon. Anty na kitchen ta sameta tace"Anty don Allah zan fita bazan jimaba,result dinmu na islamiya zan ansa feea tace yau ake rabawa kuma basu bada na wani,don zasu tantance wadanda zasuyi musabaqa" Kallonta take kamar zata karyata ta amman kuma bata hujja, "Shikenan,amman safiyya don girman Allah kiyi kokari kidawo da wuri,banson kiyo dare nafison kina kusadani" "Insha Allah bazan ba" Fita tayi cikin hanzari saita dawo ta duba jikkarta tadauki kudin taxi ta sake ficewa cike da fargaba. Duba kwatancen tayi tasanar da mai taxi din ya karya kwana ya nufi wajen,suna shiga wani lungu ta hangi mota tsayw wajen,tunaninta ta zakiyyarce don bata sanar da ita kalar motar da take ciki ba. Sauka tayi ta sallami mai taxin ta nufi motar,kwankwasa glass din tayi aka sauke shi idonta akan wani bakin mutun fuskarshi babu kyan gani,shikadai ne cikin motar ja baya tayi tana rawar murya tace"kayi hkr nai zaton yayana ne yace mun yana kusa da nan" Kallonta yake yana zaro ido yace"bar nan kafin ina farka cikinki" Babushiri na yanki hanya amman jikina yaban akwai wani abu,labewa nai wani sakon gida ina leken motar wani katon mutun yafito daga wani gida hannunsa da wata jikka ta mata,yana fitowa daga gidan na hangi faduwar mukulli baisan ya fadi bama shi,shiga motar yayi ya jima sannan sukaja suka bar wajen. Saida na tabbatar sunyi nisa sosai na dawo da sauri na dauki key din,nashiga kofar da zata sadani da gidan don kofar babu marfi. Mukullin nasakana shiga bude gidan jikina ko ina rawa yake,daker ya bude na shiga gidan da gani andade babu kowa cikinsa. Kiran wayar zakiyar nayi

Table of Contents

Chapters

101 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});