Chapter 98
Chapter 98
na saka kafin na ce"kawai ina tunanin da wasu kalamai ya dace na gode wa Allah ne, bisa kyautar da ya yi mini da kuma ni'iman da ya lulluɓe rayuwata da ita". "Ban gane ba". "Yaya Alhassan ni da kai mun san cewa ban dace da kai ba, amma duk da hakan ka aure ni ka killace ni a cikin gidanka ka ba ni dukkan kulawan da ya dace. A zamanmu da kai kullum cikin neman sabon hanyan da za kyautata mini kake yi......". Ban ƙarisa ba ya ɗaura ɗan yatsansa a saman leɓena. "Shit! Ba na son na ji wannan kalmar ta ƙara fito wa daga cikin bakinki. Bari na faɗa miki abin da ban taɓa faɗa miki ba, ni fa daman tun da ran Abba ina sonki a cikin zuciyata kawai na rasa ta yadda zan faɗa miki ne, ban san kuma yadda za ki fahimci maganar ba sa boda lokaci da yarinta a tattare da ke". Hannunsa da yake saman leɓena na ture"wai daman tun lokacin kake so na?". Ya ɗage mini giransa"ƙwara kuwa kawai ban faɗa miki ba, amma na san da na faɗa miki da yanzu mun haifi ƴaƴan ya kai dozin biyu". Babu shiri na kai masa duka a kafaɗarsa ya yi saurin zame wa. "Dozin biyu sai ka ce ka sama akuya". Dariya ya ƙyalƙyale da shi sai da ya tsagaita kana ya ce"to me ye a ciki? Ai duk za mu iya kula da su. In kuma ba za ki iya haifa min ƴaƴa ba sai na je na auro wacce za ta iya". Harara na galla masa wanda ya ke yawan cewa a duk lokacin da na yi masa sai ya tsorita. Zan yi magana ya katse ni"kin ga mayar da wuƙan wasa nake yi miki, Amatu ke ce wacce nake so kuma ba zan taɓa iya haɗa soyayyarki da na wata mace ba, ina fatan ki kasance matata har a cikin gidan aljanna". Ya ƙare zancen ya na jawo ni jikinsa ya rungume a ƙirjinsa, luf na kwantar da kaina tare da lumshe idanuna. Ya kawo bakinsa daidai kunnena kamar mai raɗa ya ce"Ina sonki matar Alhassan". "Ina sonka mijin Amatullah". A hankali ya ke shafa kaina kafin na ji ya ɗauke ni cak ya wuce da ni cikin ɗaki, na yi luf abina. Alhamdulillah! Alhamdulillah! Alhamdulillah! A yau Allah ya ba ni ikon kammala wannan littafin mai suna DAFIN HARSHE . Ina roƙon Allah ya yafe mini kuskuren da na yi a cikinsa abubuwan alkhairin da na yi a ciki kuma Allah ya haɗa mu akan ladan. Ina godiya ga masoyana da suka yi jimirin bibibiyar littafin tun daga farko har ƙarshe ba tare da gajiya wa ba, ina godiya Allah ya bar ƙauna. Ga masu buƙatan littafaina, tambaya, ba da shawara ko wani gyara ƙofa a buɗe take, za a iya tuntuɓa ta ta wannan lambar kamar haka 07038908713. Sai na ji ku.......
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98