Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 73

Chapter 73

Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel – Full Story 1,207 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ƙarfi na ja fesar ina rarraba idanuna ko zan hango Anty Zulaihatu amma ban gan ta a cikin filin tsakar gidan, da hakan ya ba ni tabbacin in ba ta cikin zaure to tabbas ta fita. "Innalillahi wa inna ilahirin raji'un!". Na furta can ƙasan maƙoshina tare da runtse idanuna sa boda sautin da tarin da Umma take yi har yanzu babu ƙauƙautawa tamkar za ta shiɗe. Duniya ke nan juyi-juyi in ji kwaɗo da ya ji sa a cikin ruwan zafi tsamo-tsamo. Wai yau ruwan da Umma za ta ji ƙa maƙoshinta da shi ne yake neman gagararta, a lokutan bayan ko don gudun rigima da tijararta dole mutum ya kamfata ya ba ta ko da kuwa babu cikakken niyya sai ga shi yau reshe yana neman juyewa da mujiya. "Amatullahi mu je na ba ki ruwan sai ki kai mata ta sha". Idanuna cike da hawaye na ɗago kai ina kallon matar Ustazu Abdulwahab da take tsaye a gabana, ta amshi kofin hannuna ta je ta ciko mini shi da ruwa taf ta kawo mini na amsa, motsa leɓena nake yi da zummar son furzar da kalaman godiya gare ta sai dai na kasa. Fahimtar hakan ya sanya ta faɗin"ba damu ba sai kin gode min ba Amatullah, ki yi maza ki kai mata ta sha ga shi har yanzu tarin bai lafa ba". Kaina kawai na jinjina mata na juya da sauri na koma cikin ɗakinmu na ba wa Umma ruwa ta ɗan sha amma duk da haka tarin bai lafa ba. Jikina yana rawa na soma karanto wani yanki daga cikin yankokin Alqur'ani mai girma tofawa a cikin ruwan kana na ba ta sha. Kamar yankan wuƙa take tarin ya tsaya kamar an yi ruwa an ɗauke, na din ga jeranta mata sannu wani na bin wani tare da gyara mata zamanta tare da sanya mata matashi a bayanta ta yadda za ta ji daɗin zaman. "Umma haka tarin yake yi miki haka kamar zai raba ki da numfashinki?". Ta gyaɗa mini kanta ta na ƙoƙarin yalwata fuskarta da murmushin ƙarfin hali. "Umma dole mu tafi asibiti a duba ki, don a gano ainihin abin da yake damun ki. Zama haka ba zai yiyu ba bari na je na dubo Anty Zulaihatu ta zo ta". Na yi zancen ina miƙe wa tsaye zan fice ta riƙo hannuna hakan ya sa na waigo ina kallonta da ido ta yi mini alama akan na dawo na zauna na kuma yi kamar ta buƙata. "Amatullah ina ji a jikina wannan jinyar ba na tashi ba ne abokin tafiya ne, ki yafe min duk abubuwan da na yi miki, na san da cewar duk halin da kika faɗa ni ce sila DAFIN HARSHEna ne sila. Kaicona! Ba na tunanin akwai wani maganin da zan sha na sama sauƙi ko da kuwa na sama sauƙin ma to iya na gangar jikina ne, amma ciwon da yake cikin zuciyata yafiyarki gare ni kawai zai warkar da wannan gyambon". "Umma kin wuce komai a wajena haka zalika kin fin ƙarfin komai. Wallahi wani ne ya yi mini ba daidai ba ki ka ce na yafe masa to an gama maganar ke nan balle kuma ke da kanki. Umma na yafe miki duniya da lahira Allah ya yafe mana baki ɗaya amma don Allah ki bari a kai ki asibiti, a nema miki magani". Ina gama maganan na tashi na fita ina fitowa na hango Anty Zulaihatu tana shigo hannunta riƙe da baƙin leda. Na yi hanzarin isa gare ta"Anty Zulaihatu don Allah ki zo mu kai Umma asibiti". Da sauri muka isa cikin ɗakin, muka haɗa muka rawa mu tafi asibiti Umma ta ce ba za ta je ba har Yaya Alhassan muka ƙira a waya ya zo ya saka baki amma ta ƙeƙashe ƙasa ta ƙi yarda. Yaya Alhassan ya ce a bar ta zuwa gobe ko za ta sauƙo ko kuma a ƙira likitan ya duba ta a gida, tare da Anty Zulaihatu muka share ɗakin muka tsaftace ko'ina. Muka yi wa Umma wanka muka sauya mata kaya. Sai dab da magrib Anty Zulaihatu ta koma gida sa boda a ranar mijinta zai dawo. Haka na zauna na Umma na tisa ta a gaba na din ga karato mata karatun Alkur'ani da nufin ko za ta sama nutsuwa a cikin ranta. "Amatullah Allah ya miki albarka". Babu shiri na tsaya daga karatun da nake yi ba tare da na zo gaɓar da ya dace na tsaya a ƙa'idance ba. "Umma me ye ki ka ce?". "Ce wa na yi Allah ya yi miki albarka". Ban iya amsa wa da kalaman baki ba, illa jan jikin da na yi na isa kusa da ita, hawayen farin ciki da murna su na zuba daga idanuna, ba zan iya tuna ranar da Umma ta taɓa sa mini albarka a kaf cikin rayuwata ba. "Umma na gode, ke ma don Allah ki yafe mini kura-kuren da na yi miki". Ta sa hannu ta shafo kaina"ba ki taɓa ɓata min ba Amatullah, Allah ya raya ki". "Amin ya Allah". Na amsa da shi ina kwantar da kaina a bisa kafaɗunta ina ta sauƙe ajiyan zuciya tamkar wacce ta yi gudun ceton rai. Sanadin albarkan da Umma ta sanya mini na ji na manta da dukkan damuwata har na ji wani nutsuwa ya mamaye mini ruhina. Ina zaune a haka ban san lokacin da bacci ya sace ni ba. Muryar Umma shi ya yi silar farkar da ni daga baccin da ya ci idona. "Ki tashi ki rufe mana ƙofa, sanyi ya fara sauƙa". Firgitit! Na buɗe idanuna ina kallon cikin ɗakin da duhu ya mamaye ko'ina alamar dare ya daɗe da yi. Na lalumi wayar da yake wajena na kunna haskenta tare da duba lokaci da ya nuna mini ƙarfe goma sha ɗaya da rabi na dare. "Subhanallahi! Umma kin ga har dare ta yi". Na yi zancen ina tashi na sassauƙe labulen tagogin sannan na rufe ƙofan ɗakin, na zo na zauna a nutse na soma faɗin"ni kuwa Umma ina kayan cikin falon suke na ga har cikin ɗakin babu komai. Daga tabarman nan fa sai ƙunshin kayan sakawanki". "Na sayar da komai da yake cikin ɗaki da falon nan, duk kuɗin su ƙare akan jinyata kafin Alhassan ya kawo min ɗauki. Amatullah tabbas Sawwama da ƴaƴanta su cika cikakkun masoya a gare mu, don ba kowa ba ne za a yi masa abin da na yi Alhassan kowa har ya dube ni da idon rahama a lokacin da nake buƙatar taimako daga gare sa". Kalamanta suka sanya jikina yin sanyi ƙalau na taƙaita zance ta hanyar gyara mata wajen da za ta kwanta na kwantar da ita bayan na yi mata alwala da ruwan goran da Yaya Alhassan ya kawo mana ɗazu da ya zo shi, na shafe mata jikinta da addu'a ni ma na kwanta a gefenta. Sai dai bacci ya ƙi ziyartar idanuna haka na yi ta tunani masu nauyi, kafin wasu hawayen tausayin kanmu da yadda rayuwa ta mayar da mu ya fara zuba daga idona. Ina ma wanda ya mutu yana dawowa tabbas da sai na bayar da duk wasu abubuwan da na mallaka a cikin duniya, don kawai Abba

Table of Contents

Chapters

98 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});