Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 87

Chapter 87

Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel – Full Story 1,209 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

game da Altine wanda hakan ya faru ne ta dalilinki. Amatullah kin zama silar bayyanar haske a cikin rayuwarmu kin cuce rayuwar su Ayan daga zalunci, cutarwa da kuma ha'incin da Atline ta daɗe tana aikatawa gare su ta ƙarƙashin ƙasa. Tabbas idan abubuwa ya daidaita ma Anty Muhibbat za ta zo da kanta ta yi miki godiya har gida sai dai a yanzu ta ce kunyarki take yi". "Wani irin kunya ke nan?". "Kunyan abubuwan da ta yi miki mana". Na saki taƙaitaccen murmushin da ya tsaya iya kan leɓena kafin na ce"don Allah ka sanar da ita cewar tarin alkhairan ta gare ni sun shafe komai. Ta riƙe n bisa gaskiya da kuma zuciya ɗaya ba ta taɓa yi mini wani abun cutarwa ba don haka bai kamata ta ji kunyata ba". Da alama ya ji daɗin zantukan da na jero don ina jin yadda yake ta sauƙe ajiyan zuciya wani na bin wani. "In sha Allah zan sanar da saƙonki a kumnuwanta". "Amma da san da cewa ka na zuwa gidanmu?". Cike da ƙwarin gwiwa ya mai do mini da amsa"ƙwarai kuwa hasalima ita ta ba ni ƙwarin gwiwan tunkaranki don ita ma kanta ta yaba da nutsuwa, hankali da kuma riƙon amananki". Lamau na yi tamkar mai bacci har sai da na ji ya ci gaba da maganan"amma ko zan iya sanin dalilin ƙiran da ake yi min na gaggawa kafin goben?". "Me kake ci na ba ka na zuba? Allah dai kawai ya kai mu goben ko ma mene ne ai za ka ji". "Haka ne kam". Mun ɗan taɓa hira kafin muka yi sallama da wuri na kwanta, don ina so na tashi na yi sallan dare kamar yadda na saba. Washe gari ban sanar da kowa zancen zuwan Saifullah sai dai kawai ina zaune a ɗaki Anty Sawwama ta ɗago labulen ɗakin. "Sai ki fito ki na baƙi". Gabaɗaya na manta da cewar mun yi magana da Saifullah mussamman da na ji ta ce baƙi maimakon ta ce baƙo. "Wasu baƙi kuwa? Ba wasu baƙin da muka yi da su za su waje na yau". "In ki ka fito ai za ki gan su, a nan ne za ki gane kin san da zuwansu ko akasin haka". Ta dasa aya a nan ta saki labulen ta yi ficewar ta, ta bar ni saƙa da warwara a cikin raina. Haka na tashi na saka hijabina na fito ina saka ƙafana a cikin falon Ayan da Aryan suka rugo da gudu har suna karo da juna suka rungume ƙafafuna. Tsugunawa na yi a gabansu ina shafa fuskokinsu don tabbas Allah ya jarabce ni da wani irin zafafan ƙaunar yaran wanda hakan ya samu asali daga soyayyar da nake yi wa duk wasu ƴan biyu musamman masu kama iri kwabo da kwabo ɗin nan. "Yaushe ku ka zo?". "Ba mu daɗe da zuwa ba, tare da Uncle Saif muka zo mu. Kuma Umminma ta ce in mun zo mu gaishe da ke sosai sosai". Aryan ya yi zancen har yana kwaikwayon muryar Umminsu. "Ina amsa wa ni ma in kun koma ku ce ina gaishe ta". Kansu suka gyaɗa mini alamar sun ji da hakan ya sa ni tashi tsaye na riƙon hannunsu muka ƙarisa cikin falon, Yaya Alhassan ne da Umar sai kuma Anty Sawwama yayin da gefe guda kuma Saif ne zaune Muhammad Taufik yana kusa da shi suke ke nan a cikin falon. Sai da na zauna na gaishe su suka amsa take na ji tausayi da tunanin halin da Muhammad Taufik zai shirga bayan na aikata abin da zuciyata take ingiza ni na yi. A zahiri hankalina yana kan su Ayan da suke ta zuba mini suturu sai dai hankalina yana kan hirar da su Yaya Alhassan suke yi, har zuwa lokacin da Saif ya ce zai je ya kai Muhammad Taukif filin jirgi don jirgin ƙarfe goma sha ɗayan rana zai bi zuwa cikin Abuja. Ya yi sallama da Anty Sawwama yayin take ta sa masa albarka da yi masa addu'ar Allah ya sauƙe shi lafiya. A nutse muyarta can ƙasan maƙoshina na furta"Allah ya sauƙe ku lafiya mun gode da ziyara". Caraf idanuna suka sauƙa cikin na Muhammad Taukif, shi ya fara janye na sa idanun ya na amsa da kalmar Amir yayin da suke fice wa daga cikin falon. Na kwashe su Ayan muka shige cikin ɗakin har muka fito na ɗaura girkin rana na gama na yi alwalan sallan zuhur na yi sallan, ina zaune kan sallayan yayin da su Ayan suke gefe na suka cin abincin da na saka musu. Na ji wayata ta soma ruri na yi hanzarin ɗauka tare da ɗaga ƙiran, maimakon amsa sallamar da na yi sai ji na yi an sauƙe ajiyar numfashi mai ƙarfin sauti. "Ina ga dai matar nan kin manta da cewar ki na da baƙo ko?". Na dafe goshina kafin na ce"afuwan na ji tunanin ba ka dawo ba ne ai". "Na dawo ina ƙofan gida ina jiranki za ki fito ne ko kuma na shigo?". Da sauri na ce"A'a ka tsaya a nan zan fito". Sai da na yi maganan sai kuma ni da kaina na ji kunya na katse ƙiran na tashi na je wajen ajiye kayana na ɗauko jakar da na sanya memory card ɗin nan a cikin na ɗauka. "Ku zauna a nan ba ri yanzu na je na dawo kun ji". "To". Suka haɗe baki wajen amsa wa da hakan ya ba ni damar fita, ban iske kowa a falo ba hakan ya ba ni salama da nutsuwar fice wa wajen kaina tsaye. Ina fitowa na hango shi tsaye a jikin motarsa yana latsa wayarsa. Da sallama ɗauke a bakina ya amsa mini yana ɗago kai tare da kafe ni da ido bayan ya mayar da wayan cikin aljihunsa. "Ki bar Bawan Allah Saifullahi marayan Allah yana ta jiranki a cikin rana". Na sadda kaina ƙasa"ai ka dawo da ka shigo ciki". "Kayya! Wallahi kunyar Anty nake yi shi yasa kawai na tsaya a nan, yanzu dai ina sauraronki don jiya na kwana cikin zaƙuwa". Na ɗan tsagaita kafin na miƙa masa memory card ɗin da yake hannuna ya karɓa yana jujjuya shi a hannunsa. "Wannan fa na mene ne?". "Ina so idan ka je gida ka nutsu ka saurare abin da yake cikinsa da zaran ka gama saurara sai ka ƙira ni mu yi magana". Shuru ya yi kallona kamar mai nazari ko kuma son gano wani abu, sai can ya ce"to shi ke nan ba matsala". Ya ƙare zancen yana cira wa a cikin aljihunsa. "Yanzu za ku wuce ne?". Ya waro idanununsa tar a kaina"to fa! Kora da hali ake yi mana ke nan? To shiga ki kwaso min su mu wuce". Kunya ya lulluɓe ni har sai da na rufe fuskana da tafukan hannayena. "Ba fa haka nake nufi ba, na ga su Ayan abinci suke ci ne shi yasa na tambaya". "Su sun sama karramawa ke nan tun da har girki aka yi musu. Saɓanin ni ɗan marayan Allah da aka shanya ni a tsakiyar rana aka manta da kashi na". "Wallahi Yaya Saif ba haka ba ne ban san ka dawo ba ne.....". Ban ƙarisa zancen ba

Table of Contents

Chapters

98 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});