Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 56

Chapter 56

Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel – Full Story 1,209 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

"Ya isa haka ya isa Amatullah". Hajiya Muhibbat ta dakatar da ni ba tare da na gama amaryar da zancen da yake kan harshena ba. "Mai zaman kanta? Kin san ma'anar wannan kalmar kuwa Amatullah? Kin ba ni mamaki matuƙar ina miki kallon mai hankali da nutsuwa wacce ba ruwanta ashe kallon biri nake yi miki ki na yi min na ayaba. A ƙananun shekarunki har kin san ki sanya ƙafa ki baro cikin gidan iyayenki ki zo inda ba ki san kowa ba kuma ba wanda ya san ki ki fara zaman kanki. Innalillahi wa inna ilahirin raji'un! Wace iriyar rayuwa ce muke rayuwa a cikin ta haka? Me yasa masifu da bala'i kala-kala ba za su baibaiye al'ummar mu ba?". Ta tsagaita tare da yarce ruwan ƙwalla da ya zubo daga idanunta kafin ta ɗaura daga inda ta tsaya. "Daga yau ba na son na ƙara ganin ki a kusa a gidan nan balle kuma ki tsaya a jikin gidan nan, na sallame ki ki ƙara gaba niyyar da taimakon da na yi Allah ya ba ni ladan niyya ke kuma idan mai shiryuwa ce Allah ya shirya ki. Ga kuɗin aikinki". Ta ƙare zancen tana zige jakarta ta ciro wasu kuɗaɗen da ko tsaya wa ƙidaya su ba ta yi ba, ta watso mini su a fuskana. Hawaye suna gudun famfalaƙi a bisa dandamalin kuncina na cira kai na dube ta sai da na fizgo numfashina da yake maƙale mini a ƙirji kafin na sama zarafin magana. "Duk magangunin akan turban gaskiya kike amma ke ma ina son na sanar da ke wani abun da ba ki sani ba. Kamar yadda rayuwata take cikin hatsari haka ke ma ta ki rayuwar da ta ƴaƴanki take cikin hatsari sanadin yarda da amincin da kika ɗaura akan mutane guda biyu da kike ganin sun fi kowa kusanci da ke a cikin wannan duniyar". Na ƙara taku uku na matso kusa da ita sosai da tun da na soma maganar take bi na da kallo cike da maɗaukakin mamaki da ya haɗu da al'ajabi. Kafin na yi magana ta ri ga ni. "Wasu mutane biyu kike magana a kai?". Na saki wani bushashshiyan dariyar da ba ta da alaƙa ta kusa ko ta nisa da nishaɗi kafin na furta"mutum na farko shi ne mijinki wanda a tsakanin gobe da jibi zai shigo cikin ƙasar nan ba tare da saninki ba, kuma ina da tabbacin har ya zo ya koma ba zai nema inda kike ke da ƴaƴanki ba. Sannan mutum na biyu ba kowa ba ne face Altine ƴar aikin da kika riƙe tamkar ƴar uwa kika busa mata iskar ƴancin yayin da ita kuma take amfani da yardar da kika yi mata take cutar da ke, ke da ƴaƴanki". Na ƙare zancen ina yi mata nuni da Altine da ƴar manuniyar ƴatsata. Ban gama rufe bakina na ji sauƙar wani gigitaccen mari a bisa kuncina har sai da na soma ganin gilmawar baƙin duhu a cikin idanuna, na yi tangal-tangal zan faɗi da ƙyar na iya sarrafa kaina na tsaya akan ƙafafuna. Ta cakomo wuyar hijabina ta riƙe tamau. "Ke har me ye kika sani akan mijina da za ki faɗa wannan maganar akan sa? Sannan yaushe kika zo cikin gidan nan da za ki gaya min wace ce Altine? Babu wani halinta wanda ban sani ba ta kai ta kawo ko ba ta furta magana da bakinta ba ina ya fahimtar abin da take nufin. Ina kika sama ƙwarin gwiwar nan?". "Tabbas ban san mijinki amma a yanzu na san abubuwan da ke ma kanki ba ka sani ba game da halinsa. Idan ba ki yarda da abin da nake faɗa ba za ki iya samunsa ranar juma'a a babbn otel ɗin da ke cikin garin Abuja. Batun Altine kuma za ki iya tambayar ƴaƴan idan tsoro bai hana su faɗa ba". Mamakin furucina ya sanya sakar mini hijabina da ta riƙe. "Saifullah ka kawar min da yarinyar daga gabana, tun kafin zuciya ta ɗebe ni na lahanta ta na kashe banza na kashe wofi. Ba na son na buɗe idona na gan ta a gabana". Sai a lokacin Saif ya yi magana da tun ɗazu yake tsaye a wajen yana bin mu da kallo ba tare da ya ce uffan ba. "Anty don Allah ki kwantar da hankali, mu saurare abin da za ta ce wataƙila mu dace da wani ilmin da mu kanmu ba mu san shi ba". "Saif babu wani mahalukin da zai tsaya a gabana ya sanar da ni wani hali na Saddam wanda zai Muhibba ban san shi ba, a cikin tsawon zaman da muka yi da shi. Balle kuma Altine duk ranar duniya take muke kwana mu tashi a cikin gidan nan, ka fitar min da yarinyar nan daga cikin gida". Cikin in-i-na Altine ta ce"wallahi ƙarya ma take yi min ba ni da wani mummunan halin da na ke ɓoye miki shi". Cikin ba da umarni Saif ya ce"Altine ɗauki su Aryan ki shiga ciki da su". "To ranka ya daɗe". Ta amsa da shi cikin bin umarni da girmamawa, ta kwashe su Aryan suka yi cikin gida. Zai yi magana na tar numfashinsa. "Zan fita ba sai ka fitar da ni ba, Hajiya ko ba ki ce da ni kar na ƙara zuwa cikin gidanki ba ni ma daman ina da niyyar sallamar kaina daga wannan aikin, sai dai ina mai ba ki shawara da ki nutsu ki yi nazarin abubuwan da na sanar dake yanzu. Ko ba daɗe ko ba jima watarana za ki neme ni ki kuma gode mini". Tas na ji ta kuma ɗauke ni da wani marin mai matuƙar sauti a karo na biyu. Na kai hannuna na dafe kuncina ina cije leɓena sa boda zafin marin da ya ratsa har cikin ƙoƙon kaina ya kuma raunana ƙarfin jiki da zuciyata. "Na gode ranki ya daɗe, na gode bisa halin girma da karamcin da kika nuna mini". Ina dasa aya a nan na sunkuya na kwashe kuɗin da ta watsa mini don na san su ɗin haƙƙina, na raba biyu na ɗauki ɗaya na damƙa mata ɗayan. "Na ɗauki iya haƙƙina ga ragowar dukiyarki". Ban jira abin da za ta ce mini ba na fi tafiyata ina tafe hawaye duk yadda na so sarrafa kaina wajen ganin na tsayar da ruwan hawayen da yake kwaranya daga kurmin idanuna lamarin ya gagare ni. Na buɗe ƙaramar ƙofar jikin gate ɗin zan fita muryar Baba Mai Gadi ta tilasta mini dakatawa. "Ƴar nan kar ki tafi ba tare da kin warware min ƙullin zantukan da na ji ku na musayarsu ba. Shin da gaske ne abin da Altine ta faɗa akan ki? Da gaske ke ɗin karuwa ce kuma zaman kanki kike yi?". Sai da ya yarce hawaye da suke tsare-tsare a kuncina kana na ce"e Baba duk abin da ka ji haka yake, zaman kaina nake yi a garin nan sannan a cikin gidan karuwai nake rayuwata". Ina gama faɗin haka na fice daga cikin gida fita irin wacce ba na fatan ko a cikin mafarki na dawo, fita irin wacce babu waiwaye har abada balle dawowa. Fita ita wacce take datse ko wani irin alaƙa da

Table of Contents

Chapters

98 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});