Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 97

Chapter 97

Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel – Full Story 1,203 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ɗayyaba. Sai da ya haɗa mini da magiya da lallashi kafin na iya cin kazar amarcin da ya shigo da ita, jikina gau ya ɗau zafi sa boda zazzaɓin da ya rufe ni ga shi dare ya yi balle ya je ya sayo mini magana, amma duk da hakan bai saduda ba ya ɗaga waya wai zai ƙira wani abokinsa mai chemist in bai rufe ba ya je ya karɓo mini magana. Da ƙyar na hana sa fita ta hanyar muna masa cewa na ji sauƙi haka muka kwanta washe gari shi ya tashe ni sallan asubahi nan inda na yi sallan na kwanta baccin huce gajiyan da na kwasa ban tashi ba har sai da gari ya yi haske wannan ɗin ma shi ya tashi ni ya ce na je na wanka na zo na ci abinci sai na sha magani don har ya fita ya amso mini. Kunya ya mamaye ni matuƙar don ni gabaɗaya ma na mance da cewar yanzu ni matar aure ce shi yasa na kwanta na sha baccina hankali kwance. Tashi na yi na wanka da ruwan zafin da ya sanya mini na zo muka ci abincin da ya girka kana na sha maganin bai fita har sai da dangi da ƴan uwa suka fara zuwa gidan nan ma sai da ya Amira da Anty Zulaihatu sun zo kana ya fita bayan ya shaida musu cewar ku kula da ni don ba na jin daɗi. Nan fa suka haɗe kai suka din ga yi mini tsiya zolaya kam babu irin wanda ba su yi mini ba. Sai da suka yi sallan magrib suka tafi bayan sun yi mini nasiha mai ratsa jiki da kashe zuciya, shawarwari kuwa sun ba ni shi daidai gwargwado sun kuma ɗaura ni akan hanyar da ta dace. Haka har na cika sati a cikin gidan aure Yaya Alhassan ne yake yi mana girkin safe duk yadda zan tashi da wuri don na yi aikina to fa sai ya riga ni, sai dai mu yi aikin tare, haka tun ina jin kunyarsa har na saki jikina mussamman da na ga yadda yake ta faɗi tashi wajen ganin ya kyautata mini ba dare ba rana, dole ni ma na yi azaman faranta masa na watsar da komai na rumgumi mijina da kuma laluman hanyar da zan bi in faranta masa rai. Haka rayuwa ta ci gaba da tafiya kwanciyar hankali da nutsuwa suka tabbata a gare ni, cikin ɗan ƙanƙanin lokaci na yi ƙiba na murmure fatana ta yi kyau har wani sheƙi nake yi kamar bayan kifi. Duk da ba nida haske amma fatata ta yi farau ta washe. Zuciya babu wani damuwa haka nan raina fari ƙal tamkar zaiba. Ranar da na cika sati huɗu muka yi baƙi Saifullah da Muhammad Taufik suka zo wani abun mamakin har da Sheik Dawood sun wuni suna tattaunawa da Yaya Alhassan, ni kam kunya ta hana ni sakat tun da na fito muka gaisa ban ƙara koda wullagawa ta cikin falon sai da za su tafi Yaya Alhassan ya zo ƙira ni. Tabbas ba na buƙatar sai an faɗa mini da kalmomin baki idanuna kawai sun nuna mini cewar Sheik ya sauya don mun sha ruwan addu'o'i da albarka daga gare sa, ya ɗauki Naira dubu asiri ya ba ni da za su tafi. Haƙiƙa Yaya Alhassan ya cika mijin marainiyan da ya ambata kuma ya cika dukkanin alƙawarin da ya yi mini a darenmu na farko, ya inganta rayuwata matuƙa da kuɗin sadakina na shiga harkan kasuwanci atamfofi nake sayar wa da duk wasu nau'in kayan sawan mata, likkafa ta ci gaba don har lefe nake haɗawa mai rai da motsi na fita kunya. Kan ka ce kwabo rayuwa ta sauya jin daɗi ya zauna mana ni da mijina ba mu da wani burin da ya wuce faranta wa juna, na ƙara waye wa da samun ilmin zaman duniya da kuma mu'amala mutanen cikinta. Ranar ina zaune kwatsam sai ga Hajiya Muhibbat a cikin gidana tsabar farin ciki sai da na rasa inda zan tsoma ta mun sha hiran yaushe gamo da ita, tare da ba wa juna labarin bayan rabuwa nan take shaida mini cewar mijinta Saddam zai ƙara aure kuma Zinariya ce matar da zai aura, don ita da kanta ma ta shige masa gaba wajen neman auren, don ta fahimci suna don junansu kuma ba za su iya rabu wa, sannan Saifullah ma zai angwance da babbar jika a gun Sheik Dawood, na yi musu murna matuƙa da lokacin auren ya yi Yaya Alhassan da su Amir suka je su domin shaida ɗaurin auren. Sati ɗaya tsakani Amira ta haihu sai dai ɗiyar ba ta zo da raina ba. Ni kam haihuwar ta yi jinkiri don sai na shekara ɗaya da rabi a gidan aure kafin na haifi ɗa na miji santalele da shi, da sati ya gayayo ya ci sunan Abbana ana yi masa alkunya da Abul-khair watansa biyar a duniya aka yi bikin Amir da ya angwance da ƙanwar mijin Anty Zulaihatu mun sha biki don tare wa na yi a gidan Anty Sawwama, haka Yaya Alhassan ya gama fushinsa har ya sauƙo don kansa, a rage saura Umar kawai wanda kullum nake yi masa tsiya da cewar sai mun daina ba shi abinci. Lokacin auren Muhammad Taufik gayya muka yi muka je mu bikin iyalan Sheikh suka karrama mu matuƙa har muka je muka dawo mu na jinjina halin girma da dattaku irin na su. Na zamo abar alfahari ga mijina iyayen da kuma ƴan uwa har ma da matan cikin unguwan da nake, a ko a kan hanya nake tafiya na ga uwa tana furta munanan furuci ga ɗanta, sai na dakata na sanar da ita illar hakan a wasu lokatan har na kan yanko wani sashi na cikin tarihi don hakan ya sama iznina a gare su. Don tabbas na ishe kowa misali cewar DAFIN HARSHE mussamman na uwa akan ƴaƴanta ya fi dafin maciji illa don shi kassara rayuwa yake yi gabaɗaya. Har gida Saifullah da Muhammad Taufik suka kawo mini matanyensu, Zinariya ma sa ta rikiɗa ta koma sunanta na yanka watau Maryam ta kawo mini mun sha kuka ni da ita, mussamman da ta labarta mini cikin tsananin da ta fuskata da barazana daga wajen Hajiya Babba a yayin da ta yi ƙoƙarin sauya rayuwa, ta ce da ni har hauka sai da ta sa ta yi hauka tuburan har sai an ɗaure ta da mari don in ta bazama ta fice daga cikin gida to fa sai lokacin da Allah ya nufa. Da taimakon Allah da kuma addu'o'i ta sama sauƙi har hankalinta ya dawo jikinta. Ranar wata juma'a mun dawo daga gidan Anty Sawwama da muka kai mata wuni, ina gaba Yaya Alhassan yana baya yayin da yake riƙe da Abul-khair a hannunsa, na zaro makullin daga cikin jakata na buɗe ƙofar falon muka shiga ciki a nan cikin falon muka yada zango. Na amshi Abul-khair da ya fara bacci na je na kwantar da shi kana na dawo. Kusa da shi na zauna na tisa shi a gaba ina kallonsa har sai ya yi magana. "Ke lafiyanki kuwa wannan kallon kamar za ki cinye ni?". Taƙaitaccen murmushi

Table of Contents

Chapters

98 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});