Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 5

Chapter 5

Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel – Full Story 1,213 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

yi masa na rodi? Ke ma ai ware rana za ki yi ki je ki tare Alhajin wata ki fanshe abin da aka yi miki. Yo ai daman bariki alelen gero ne duk wanda bai iya ba kwaɓe masa take yi, don haka kowacce ta gama harkokin gabanta a watse na kashe wannan case ɗin". Tsimi-tsimi na ga kowacce ta ja jikinta ta koma ɗakinta bayan an gama jefawa juna harara da kallon uku saura kwata. Ni ma koma ciki na zauna ina ta jiran na ji an yi ƙiran sallan zuhur amma shuru kamar an aike Bawa garinsu. Ganin wankin hula yana neman kai ni dare na dauki ɗayan pure watern da na ajiye na fito na yi alwala da shi na shiga na yi sallan zuhur ina zaune inda na yi sallan La'aniyatu ta shigo, muka sakarwa juna murmushi kafin ta ce"har ya tafi kenan?". "Waye fa?" "Aminu mana tauraro mai wutsiya ganin ki ba alkhairi ba". Na saki taƙaitaccen murmushi ba tare da na ce da ita komai ba. "Kin ga mutumin kusan rabi da kwatan matan gidan nan shi ya kawo su, kuma duk wanda suka kwanta da shi ya biya su sai an cire masa nasa kason mai tsoka a ciki. Wani zubin har ɗaukan su yake yi ya kai su wajen manyan mutane su yi haramtacciyar mu'amala, akan kuɗi babu abin da ba zai iya aikatawa ba. Kuma ke ma ina tabbatar miki da cewar duk wannan rawan ƙafa da ɗawainiyyar da yake yi a kanki zzi fanshe su tsaf har da riba". Na yi shuru na kasa cewa komai sai can na furta"Allah ya kyauta shi kuma Allah ya ganar da shi". Ba ta amsa ba illa taɓe bakin da ta yi tana ɗauke kanta gefe guda. "Tun ɗazu ina ta zaune a nan ina jiran ƙiran salla amma shuru". "Ƙiran salla dai? To ai ko za ki shekara a nan ba za ki taɓa jin ƙiran salla ba. Tun daga farkon layin nan har ƙarshenta babu masallaci, islamiyya ko kuma wani majalasin da ake koyar da faɗin Allah da Manzonsa. Ke in taƙaice miki bayani babu wani ɗan arzikin da yake biyo wa a layin nan don duk mutumci da kimarka idan aka ganka a layin daga ranar ba za a ƙara yi maka kallon mutumci ba. Idan kin ji ana faɗin layin jahannama to layin nan kenan". [12/3, 2:54 PM] Aeesher: *DAFIN HARSHE* ©️ Maimuna Tijjani Iyam _________________________________ Page 4️⃣3️⃣ Na sauƙe ƙatuwar ajiyar zuciya ina dafe ƙirjina da ya bugawa tamkar zai faso nama da fatana ya bayyano waje, ta kalle ni ta saki murmushi"mamaki kike yi ko?". Na gyaɗa mata kaina da hakan ya ba ta daman zarcewa da faɗin"indai mamaki kike yi to yanzu kika fara don sai an wayi gari watarana kin daina ma jin mamakin wasu abubuwan". "Allah ya kyauta". Na furta a taƙaice ba ta amsa mini ba har sai da na ƙara cewa"don Allah yanzu ƙarfe nawa ne?". "Fitowa na daga ɗaki dai ƙarfe huɗu saura". Na yi zumbur na miƙe ina tada iƙaman sallan asr, har na iddar da sallan tana zaune tana kallona na shafa addu'ar da na yi kana na fuskanto ta. "Don Allah ina neman wani taimako". "Faɗi kanki tsaye, matuƙar zan iya to kin same shi kin huta". "Ina so na zagaya cikin unguwan nan don kafin wa'adin da Aminu ya ɗebar mini na ciyar da ni ya cika. Ina so na tsaya da ƙafafuna ba tare da na bi hanyar da ragowar sauran mutanen gidan nan suka bi ba". "Za ki sha wahala ne kawai don a kaf unguwan ba na tunanin za ki sama aikin da za ki kare mutumcinki da shi. Idan har kin san cewar ba bariki kika fito yi ba me yasa tun farko kika baro gaban iyayenki?". Na ja dogon numfashi na fesar kafin na furta"wannan wani labari ne mai zaman kansa watarana zan ba ki labarina. Yanzu dai ina so na fita don na lura zama bai kama ni ba". "Bari na duba idan Ummanta ta yi bacci sai mu fita na raka ki". Ba ta jira abin da zancen ba ta tashi ta fita da sauri, babu jimawa ta dawo" mu yi sauri mu fita, ta yi bacci na san kuma ba za ta tashi ba wataƙila sai nan da zuwa dare. Don ta shawo ta yi tatil". Na yi sakeke ina kallonta ganin ba ni da niyyan motsawa ya sa ta jan hannuna ta jijjiga ni na dawo cikin hayyacina daga kogin mamakin da na faɗa, ta ɗauki ɗan makullin ta muka fito ta ja ƙofan ɗakin ta rufe da makulin muka fita a zaure muka yi kiciɓus da wasu samari su biyu suna shigowa. Kamar za mu gogi juna da su amma duk da hakan sun ƙi matsawa sai ma ƙara matso mu da suke yi. "Gambo ka ba ni hanya na wuce tun kafin na yi maka rashi mutumci mai wasali". Ya fashe da dariya"to ki yi mana wani dare ne jamage mai gani ba La'aniyatu? Ni fa babu wani nau'in rashin mutumcin da ban ga ni ba, to don kin yi na ki a matsayinki na ƙaramar ƴar bariki ma ai ba zai yi nasarar ɗaɗani da ƙasa ba". Ɗayan ya saki tsaki yana banka mana harara"ni wallahi na rasa abin da ka gani a jikin wannan ƙwailan yarinyar da ka ji ka nace mata. Na rantse da Sarkin dake busan numfashi ko a yau na yi niyyan kwanciya da yarinyar nan babu makawa sai na yi ko da amincewarta ko babu. Bar ganin wai uwarki tana ba ki tsaro da kariya yarinya". "Kanku ake ji wai mahaukaci ya faɗa rijiya ya ce ni wanka na nake yi". La'aniyatu ta yi zancen cikin matsanancin ɓacin ran tana jan hannuna muak raɓa ta gefensu muka wuce tun da muka fito ba ta ce da ni komai kuma ba mu fasa tafiya ba kamar yadda ba ta sanar da ni inda muka nufa ba. Sai da muka yi nisa kafin na ce"na ga kaman ranki ya ɓaci bisa abin da samarin can suka yi miki ko?". "Kar ki damu zan koya musu hankali ɗaya bayan ɗaya". Na saci kallonta kafin na ce"su waye ne su ɗin? Sannan me yasa suke cin irin wannan alwashin a kanki?". Ta ja dogon numfashi ta fesar sai da ta shafe wasu mintuna ba ta yi magana ba. "Ki yi haƙuri idan abin da na faɗa ya sosa miki rai ko kuma ba ki ji daɗinsa ba". "Kar ki damu babu komai. Ba kowa ba ne su ɗin face irin ƴan iskan garin da suke taruwa a cikin gidanmu, gani suke yi don kasancewata ƴar magajiyar karuwai da ƴan daudu shikenan ni ma ƴar iska ce ba su san cewar baƙar tukunya ta kan iya fitar da farin tuwo ba". Na jinjina kaina alamar gamsuwa da dukkan zantukanta"haka ne kam kin san lamarin mutane sai haƙuri". "Kin gan ni nan tun da na yi wayau na iya bambamce tsakanin launin fari da baƙi daidai da rana guda ban taɓa jin rayuwar da mahaifiyata take yi yana burge ni ba. Tun ina ƙarama na tashi da tsana da ƙyaman irin rayuwar da take yi, tun

Table of Contents

Chapters

98 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});