Chapter 94
Chapter 94
kin ga yadda Allah ya yi da mu ko? Aure tsakanina da ke ba zai yiyuwa. Ƙaddara ta shata mana layi a tsakaninmu ta yi mana katanga daga cika burinmu na mallakan juna a matsayin ma'aurata. Sai dai daman kullum a cikin roƙon Allah muke yi ya yi mana zaɓi mafi zama alkhairi a gare mu, tun da hakan ya wanzu a tsakaninmu sai mu ɗauka cewar hakan ne alkhairi a gare mu bakiɗaya da mu da iyayenmu har ma da al'umma". Ya ɗan tsagaita kafin ya ci gaba daga inda ya tsaya"Allah ne shaida cewan na so ki tsananin son da ban taɓa zato ko tunanin zan iya yi wa wata ɗiya mace ba, na yi burin aurenki na yi ɗamarar kasacewa da ke har ƙarshen rayuwa amma Allah bai nufa faruwan hakan ba, ina yi miki fata da addu'ar samun miji na gari wanda ya fi ni komai da komai wanda zai kula da ke ya riƙe ki amana kuma bisa adalci. Idan ki ka sama wanda zai zo ki ya ƙaunace ki domin Allah tabbas zan kasance cikin kwanciyar hankali a duk inda nake, wataƙila wannan shi ne zuwa na a ƙarshe cikin gidan nan da zummar zuwa wajen ki mu yi hirar saurayi da budurwa, sai dai na zo a matsayin wanda ya zo ziyara da kuma sada zumunci". Sai a lokacin hawaye suka zubo daga idanuna sa'ilin da na ga ya miƙe na kuma tabbatar da cewa da gaske tafiyan zan yi, tafiyan da yake daidai da tarwatsewar tubalin ginin da na yi wa rayuwa. "Shi kenan tafiya za ka yi? Shi ke nan komai ya zo ƙarshe a tsakaninmu? Daman haka soyayyar take? Da na san haka ne da ban fara da na san hakan zafin rabuwan yake da ban saki jiki mun saba da kai ba Saif. Sai dai haka Allah ya ƙaddara yadda kake yi mini fatan alkhairi ni ma ina yi maka irin wannan fatan". Sai da na miƙe tsaye na zo gabansa na tsaya mu na kallon juna kana na ci gaba da maganar cikin zubar da hawayen da nake jin sauƙar su a bisa fatan fuskana kamar ana watsa mini garwashin wuta. "Tabbas na shaida cewar kai ɗin mutumin kirki kuma mutumin ƙwarai, ka sama matsayi a cikin zuciyata irin matsayin da babu wani ɗa na mijin da ya taɓa samun irinsa. Saifullah ina sonka amma ƙaddara ta tsara dole mu haƙura da juna". Kukan da ya gama cin ƙarfina ya tursass mini yin shuru ba don na rasa abin faɗa ba. "Wallahi Amatullah da akwai wani hanyar da mu iya yin aure tabbas da zai na bi wannan hanyar, amma dole mu haƙura sa boda maslahan rayuwarmu da kuma ƴaƴan da za mu haifa har ma da kwanciyar hankali iyaye da ƴan uwanmu. Kar mu bari soyayya da burin mallakan junanmu ya rufe mana idanuna har mun jefa rayuwar ƴaƴan da za mu haifa cikin garari, wallahi cutar nan cuta ce mai matuƙar wahala ga kuma ɗawainiyya. Ina sonki wannan dalilin ya sanya ba zan iya jefa rayuwarki cikin ƙuncin ba, Amatullah ba don ba na sonki zan tafi sai don maslahan rayuwarmu kuma ina fatan Anty ma ta fahimci hakan. Allah ya ba ki miji na gari wanda zai ƙauna ce ki domin Allah". Yana dasa aya a nan ya juya ya fice daga cikin falon da kallo na bi shi har ya fita kafin na durƙushe akan gwiwoyina ina wani irin azababben kuka mai ciwo. Har sai da Anty Zulaihatu ta fito ta same ni a wajen ita kuka ni kuka haka muka mayar da gidan tamkar gidan mutuwa, sai bayan sallan magrib Yaya Alhassan da Amir suka dawo Anty Zulaihatu ta shaida musu abin da yake faru, lamarin ya jijjiga su ainun don da aka sanar da su zancen Yaya Alhassan sai da ya nema wajen ya zauna sa boda jirin da yake ɗibansa. Sai da suka yi da gaske kafin suka fahimtar da Anty Sawwama illolin da yake tattare da duk wani aure da aka gina shi akan irin wanan turban, daren ranar mun sha kuka har sai da muka goge wa Allah, Anty Sawwama ta ce tun da haka ya kasance Yaya Alhassan ya ƙira gobe gobe su zo su amshi kayansu da suka kawo. Haka kuwa aka yi aka mayar musu da kayan. Ranar Amira da Mansur suka zo muka wuni muna jajantawa juna lamarin sai bayan sallan magri suka tafi, na shiga damuwa matuƙa mussamman idan na ɗaga wayata ban iske ƙiran Saif sai na ji duk duniyar ta yi mini zafi har na rasa inda zan tsoma kaina na yi salama. Haka zan zagaya na shiga banɗaki na yi kuka na gode wa Allah na wanke fuskana kana na fito. Tun bayan faruwan lamarin ba ma yin dogon magana da Saif sau ɗaya muke yin waya da shi a wuni shi ma da safe ne sai ƙira ni, mu gaisa ya ce daman ya ƙira don ya ji lafiyata shi kenan kuma sai washe gari, Hajiya Muhibbat ma ta ƙira muka jajanta lamarin sosai har da kukanmu shaɓe-shaɓe tamkar waɗanda aka yi wa wani gagarumin rasuwa. Haka aka yi sati biyu da faruwar lamarin lokacin da Allah ya nufa saura sati ɗaya a yi bikin, a daren wani ranan juma'a Anty Sawwama ta tara mu a falo gabaɗayanmu bayan sallan magrib har da mijin Anty Zulaihatu da ya zo ɗaukan ta kasancewar ranar ta wuni a gida. Amir ne ya buɗe taron da addu'a kafin Anty Sawwama ta soma amayar da dalilin da ya sa ta tara mu duka a wajen. "Na tara ku a nan ne gabaɗaya sa boda na sanar da ku hukuncin da na yanke wanda nake tunani da hashashe zai zamo alkhairi gare mu ba ki ɗaya. Amatullah amana ce a gare ni sannan zan ƙara jadadda muku ko bayan raina ku riƙe ta amana ku yi dukkan abin da zai faranta mata rai don neman rahamar Allah kasacewarta marainiya. Ko a iya rashin iyayenta aka tsaya haƙiƙa Amatu ta shiga jarabawar rayuwa balle kuma a haɗa da ragowar jarabawan da ta faɗa a cikin rayuwarta, ina so na yanke hukuncin da nake da yaƙinin cewar ba zai cutar da ɗaya daga cikin mu, ina so lokacin da aka sanya auren Amatullah kar a ɗaga shi". "Auren Amatullah kuma? Ta sama wani mijin ne?". Amir ya yi zancen cikin tsagwaron mamakin da ya bayyana har a cikin furucinsa. Anty Zulaihatu ma ta amshe zancen"Umma aure yanzu kam sai dai mu yi addu'ar Allah ya kawo mata miji na gari". "Ni ma dai haka nake gani, in sha Allah miji ɗaya dai kam Allah ba zai hana ta ba". Yaya Mu'azzam ya sanya baki cikin maganan a karo na farko, Yaya Alhassan k bai iya cewa komai illa ƙasa da ya yi da kansa har zuwa lokacin da Anty Sawwama ta ɗaura da zancen. "Ina so a cikin daren nan a ɗaura auren Alhassan da Amatullah bayan an an iddar da sallan isha'i. Alla ba shi sai ta tare a lokacin da aka sanya bikin watau sati mai zuwa". Ina da yaƙinin duk cikinmu babu wanda ya yi zaton abin da zai fito daga bakin Anty Sawwama
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98