Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 58

Chapter 58

Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel – Full Story 1,211 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Washe gari da ƙyar na tashi sa boda daren jiya ban iya runtsawa da wuri, a makare na gabatar da sallan asubahi na zauna inda na yi sallan na yi shuru ina tunanin ta yadda ta fara gudanar da rayuwata a wannan gaɓar, sai dai kamar yadda Zinariya ta faɗa ne dole na tashi na yi yaƙin nema wa kaina ƴancin kai. Haka kuwa haka ba ta cika sati guda da tafiya ba sai da na zama babu wanda bai sanni ba a kaf cikin gidan, hatta baƙin da suke zuwa san sunana ko da kuwa ba su taɓa ganin fuskata ba. Na yi ƙaurin suna fiye da tunanin mai tunani ta yadda duk wani rashin mutunci da tijara na san farillai da sunnoninsu, har na kai munzalin da babu wanda yake rayuwa a cikin gidan da za a ƙira sunana ba tare da ya sha jinin jikinsa. Babu wanda ya isa ya nuna mini ɗan ƴatsa rashin mutuncin da nake yi ina sa yaƙinin ko Zinariya ce ta dawo ba za ta yi rabinsa. Faɗa da jagwal babu wanda ba na shiga, rigima kuwa ko ba da ni ake yi ba zan shiga na amshe balle kuma da ni ake yi. Yo wani ma ya yi rawa balle ɗan makiɗi. Duk tijara da kwashe-kwashen Aminu sai da ya zubar da makamansa ya duƙa a gabana ya sara mini. Har na kai lokacin da duk sa'ilin da aka kawo wata sabuwar yarinyar cikin gida waje na ake fara kawo ta na yi mata darasi. Sai dai duk barikin da nake bugawa babu wani na mijin da nake sake wa fuska balle na ba shi gangar jikina, haka nan duk shagalata ba na wasa da addini ko kaɗan du abin nake yi kuma a duk inda nake da na ji an yi ƙiran sallan zan bar abin da nake yi salla, haka nan azumin Litinin da alhamis ba ya taɓa wuce ni. Hakan nan ba a yin cikakkun kwanaki goma sha biyar ba tare da na sauƙe alƙur'ani ba, sadaka kuwa sai dai in ban sama taro da sisi ba. Wasa-wasa sai da Zinariya ta ci satikai biyar cur ba ta dawo ba, tun abin ba ya damu na har ya soma damuna. A duk lokacin da zan ce Aminu ya ƙira mini layinta a kashe yake lamarin ya yi matuƙar ɗaga mini hankali da jefa ni cikin cakwakiyar tunanin an ya kuwa lafiya?. [12/14, 12:30 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE* ©️ Maimuna Tijjani Iyam ___________________________________________ Page 6️⃣9️⃣ Haka nake kwana na tashi da tunanin halin da Zinariya take ciki, tabbas da na san garin Abuja ko kuma na taɓa zuwa cikinsa babu abin da zai hana ni tashi takanas na je neman Zinariya. Sai dai na ji an ce mini babban gari da ya tara manya da hamshaƙan mutane neman mutum a cikin irin wannan garin ba ƙaramin aiki ba ne. Ina ƙwance a ɗaki ina ta saƙa da warwara a cikin raina yayin da wani sashin zuciyata yake hasko mini rayuwarta ta baya mussamman yadda muka rayu da Abba, ta tabbata a gare ni ba ni da wani masoyin da ya wuce shi haka nan babu wani wanda zai nuna mini ƙauna kwatankwacin irin wanda ya gwada mini. Murmushi kawai na yi ina jinjina kaina don izuwa yanzu a zo bijiren da zuciyata ta bushe ta zama tamkar dutse wajen dake wa, babu abin da yake sani fargaba balle tsoro ko kuma tausayi haka nan hawaye ba za zuba daga idanuna. Maimaikon lokacin da suka shuɗe da ba na sanin sa'ilin da suke cin gashin kansu. Babu shiri na tashi daga kwanciyar da na yi sa boda hayaniyar da na ji yana tashi a tsakar gidan ana ta ruwan shariya tamkar dangin maguzawa. Diro wa na yi daga kan katifar Zinariya da nake kwance na bayyano waje. "To ƴaƴan kaji dangin karnuka wani gurmin kuma aka haɗo da sanyin safiyar nan?". Na yi zancen yayin da nake iso wa inda na ga su a tsaye cirko-cirko tamkar sun haɗiyi taɓarma. "Wai don tsabar iskanci da rainin wayon mutanen cikin gidan nan, na ɗaura girki daga na fito na shiga banɗaki na dawo na samu an sace tukunyar gabaɗaya, sa boda rashin ta kunya da tsiya. Wallahi a fito mini Sabuwar yarinyar da aka kawo da na bi ya mata littafin sirrin zaman bariki babi-babi, kuma aka yi karati yarinyar kanta yana ɗauka uwa uba kuma a wayenta ta shigo harkar. "Ke Kyawawa shi ne kika hargitsa gidan haka da sassafen nan? Ko da yake ban ga laifinki ba a ɗauke tukunya sukutum ai dole ki tada jijiyoyin wuya. Yarinya ci gaba da masifa har sai an fito miki da kayanki ai bala'i da masifa babu uwar wacce ta kashe". Ina rufe bakina Aminu da shigowar sa ke nan ya amshe zancen"ina gaida uwar haɗa gurmi, yarinyar nan kin san kan tsiya kuma kin san wassulanta. Kin san har yanzu kaina ya ƙasa yarda cewar ki na da haddar alƙur'ani a cikin wannan kan nakin". Na saki shewa har da tafa hannu kana na ce"ai kuwa ya kamata ka yarda don yadda nake murza wulaƙanci na tofar. Haka nake sarrafa ayoyin cin alƙur'ani yayin rera su". Ya kwashe da dariya mai sauti"Mahaddaciya ga sani ga ilmi kuma ga shagala". Ban ce da shi komai illa murmushin da na sakar masa yayin da nake juya wa na koma cikin ɗakin. Na zauna na yi shuru tunanai kala-kala suna ziyartar cikin kwanyanta, tun da na sa ka ƙafata na fito daga cikin gidanmu daidai da rana guda ban taɓa jin ina son na ƙara kallon fuskar Umma ba balle har na yi kewarta ko na ji sha'awar son kasancewa a tare da ita, kamar yadda nake ji a cikin ƴan kwanakin. Wani tsananin kewarta da son ganinta nake yi. Haka na wuni ina wannan tunanin bayan na yi sallan asr na kwanta a nan inda na yi sallan, take wani bacci mai nauyin gaske ya yi awon gaba da ni. Irin da baccin da zan iya bugan ƙirji na ce rabo na da bacci cikin kwanciyar hankali irin sa tun kafin rasuwan Abba. A firgice na farka jikina gabaɗaya yana karkarwa ga wani uban zuffan da ya jiƙa mini jiki lajab kamar wacce aka kwarawa ruwa. Ƙirjina ya na dakan lugudan-lugudan tara-tara tara cikin daƙiƙu tara. Na buɗe baki zan kurma ihu sai kuma na yi hanzarin tufe bakina da tafukan hannayena. Allah ya ba ni ikon karato addu'ar da ta yi nasarar fara zuba kaina a cikin wannan rikitaccen yanayin mai kama da almara. "Hasbunallahu wa ni'iman wakil". Na furta har izuwa lokacin ilahirin jikina yana rawa sa boda munin mafarkin da na yi da Ummata. Mafarki na yi wai ga ni ga ita a gaban Allah ya na yi masa hisabi yayin da yake tuhumarta akan amanarta da ya ba ta ta yi masa riƙon sakainan kashi ta kuma wofartar da nauyin da yake bi sa wuyanta, wai Ummata ta gaza kare kanta Mala'ikun azaba suka saka mata sarƙan wuta su ka nannaɗe mata jikinta suka jefa can cikin ƙasan wuta, ina ji ta na ihu ta na kururuwar neman ceto da agaji na yunƙura zan je na taimaka mata

Table of Contents

Chapters

98 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});