Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 81

Chapter 81

Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel – Full Story 1,208 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kafe shi da idanuna ina ganin tamkar mafarki nake yi ba a farke nake ba. "An ya ka san abin da bakinka yake furtawa kuwa? Ko kuwa dai ka mance wacce take tsaye a gabanka ne?". Ban jira amsar da zai ba ni ba na ci gaba da zancena cikin ƙonar zuciya da tafasan rai. "Idan ba ka gane ni na yi mata tuni ni ce fa Amatullah wannan ɗiyar da ka zargi tarbiyyarta. Wacce ta yi ciki ba tare da aure ba wacce ta tafi can uwa duniya ta yi rayuwa ba tare da tsawatarwan iyayen ba. Wacce ta yi zaman kanta a cikin tsakiyar gidan karuwai ta ci gashin kanta da kanta. Wannan yarinyar da ta mayar da ɗakin otel tamkar ɗakin kwananta, wannan yarinyar marar tarbiya da nutsuwa. Wannan yarinyar da kake shakku da kokonton kasancewar ta kusa da ahalinka". Na saki murmushin takaici kafin na ci gaba daga inda na tsaya. "Shin ko ka manta ku rayuwarku a tsaftace take? Ba ku da wani abun aibu a tattare da ku shin ka manta ikirarin da ka yi na cewar Allah a raba ku da kaidina?. Yadda kake mutumin ƙwarai kuma kamili ai da matar ƙwarai ka dace wacce ta fito daga gidan tarbiya da halin girma. Saifullah kar ka yaudari kanka da neman soyayyarta domin bayan rashin dacewan da muka yi da juna ba zan taɓa iya cusa sonka a cikin zuciyata da ka zama silar raunatata ba. Na roƙe ka idan ma ɓatan hanya ka yi ko kuma tuntuɓe harshe ka samu to kar ka ƙara zuwa ƙofar gidan nan, babu wani abun da ya rage tsakanina da ku". Na ƙare zancen cikin rauni ina haɗe hannayena wajen guda alamar, zai yi magana na katse masa hanzari. "Don Allah ka bar ƙofar gidan nan wallahi ba na ƙaunar ganinka. Ka yi wa girman Allah ka bar ƙofan gidan nan". "Na ji zan tafi amma don Allah ki ba ni ko da mintuna goma daga cikin lokacinki, ki saurare ni ki ji bayanin da zan yi miki. Ban zo wajen da nufin yaudara ko cutar da ke ba hasalima....". Na datse numfashinsa"ba zan taɓa sonka ba Saifullah, me yasa ba ka duba matsayina da na ka ba da suka yi hannun riga. Ƙwarya ta bi ƙwarya idan ta bi alwashi ai fashe wa za ta yi". "Na ji na yarda ba za ki so ni, amma ni dai ki ba ni dama ki saurare ni". Hannayena na saka na toshe kunnuwana da shi yayin da hawaye suke zuba daga idanuna kamar bakin indararo, ganin ba zan iya jimirin sauraron zantukansa da suke barazanar raba ni da nutsuwata ba, hakan ya tilasta mini juya wa na shige cikin gida da gudu. Na ci karo da Anty Sawwama ta na fito wa daga banɗakin ina jin ta tana tambayata ko lafiya na shigo gida da kuka, amma ban iya amsa mata ba. Kai tsaye ɗakin kwanana na nufa na kwanta ina kuka, babu irin tambayoyin da ba ta yi mini ba amma na dage ina ce mata babu komai ba don ta yarda ba haka ta haƙura ta ƙyale ni. Daren ranar ban iya runtsa wa sai da dare ta raba cikin baccin na ji ana ƙiran sunana na tashi na zauna ina ƙara kasa kunne na ji dai tabbas sunana ake ƙira a tsakar gidan. Zumbur na yi na miƙe ina murtsike idanuna na buɗe ƙofar ɗakin na fito waje inda nake jin sautin ƙiran yana tashi. Ina fito wa na ga tsakar gidan ya yi haske sosai tamkar ba dare ba, na kai dubana inda nake ji sautin yana tashi idanuna suka sauƙa akan fuskan Hajiya Babba. Take ilahirin jikina ya soma rawa tamkar ana jona mini wutan lantarki na nuna da yar manuniyar yatsana bakina ya na rawa na ce"Hajiya Babba ke ce ki ka biyo ni nan?". Lu na ji na yi baya na zube a ƙasa yayin da kaina ya bugu da dutse, tun idanuna suna gano mini fuskarta dishi-dishi har sai da suka rufe gabaɗaya, daga lokacin ban ƙara sanin inda kaina yake ba balle fahimtar abubuwan da suke wanzuwa. [12/24, 3:41 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE* ©️ Maimuna Tijjani Iyam ___________________________________ Page 7️⃣8️⃣ A hankali na soma buɗe idanuna da suka yi mini nauyin gaske kaina ya yi dum tamkar wacce aka yi wa ajiya dutse, hankalina yana dawowa jikina abin da ya faru ya dawo mini cikin kwanyata tiryan-tiryan, take na zabure ina rafka salati tare da runtse idanuna da matuƙar ƙarfi ina ta batutuwa mara sa kan gado. "Hajiya Babba me ye na yi miki za ki biyo ni har cikin gidan nan? A zamana da ke ko da wasa ban cutar da ke ba don Allah ke ma kar ki cutar da ni ko da kwantankwacin misƙala zarratin ne". Ji da na yi an dafo kafaɗana shi ya dawo da ni cikin hyayancina na buɗe runtsatstsun idanuna na kafe Anty Sawwama da su da take zaune kusa da ni, ganinta kusa da ni ya sani ƙanƙame ta a jikina tsaf ina zubar da hawaye tamkar an kunna burɗaɗɗan fanfo. "Uwata ki nutsu ki kwantar da hankali, babu wani abun da zai faru face alkhairi da iznin Allah. Babu wanda ya isa ya cutar da ke duk abin da kika ga ya faru da ke to daman haka Allah ya ƙaddara zai faru". Luf na yi a jikinta ina mayar da numfashi tamkar wacce ta yi wani gagarumin aikin wahala, mun daɗe a haka kafin ta ɗago ni daga cikinta ta tambaye ni abin da yake faru na kwashe komai na sanar da ita, haƙiƙa na hangi tashin hankali da tsoro kwance a cikin ƙwayan idanunta sai dai ta dannan duk yanayin da take ciki. A cikin daren ta ƙira Yaya Alhassan ya zo ta sanar da shi komai, ina kwance na ɗaura kaina akan cinyarta yayin da na lumshe idanuna tamkar mai bacci sai dai a farke nake don ina sauraron dukkan abin da suke tattaunawa. Cike da tarin damuwan da yake tattare da furucin bakinta Anty Sawwama take faɗin"tsoro ɗaya kar wannan matar ta sabauta yarinyar nan, ina tsoron har ta juya mata hankalinta ko ma ta raba ta da shi gabaɗaya, don irin waɗannan matan ababen tsoro ne". "Umma in sha Allah babu abin da ta isa ta yi wa Amatullah, gobe idan Allah ya kai mu zan je har can garin Jafarin mu yi ta ni da ita, in ta kama ma har ƴan sanda zan saka cikin lamarin". Anty Sawwama ta yi hanzarin taran numfashinsa"kar ka sake ka aikata wannan kuskuren Alhassan. Wani hujja kake da shi da za ka je har cikin gidan ka tunkare ta da wannan zancen? Ka san girman irin wannan lamarin kuwa? Hmm! Addu'a ita kaɗai ce mafita a gare mu". Shuru Yaya Alhassan ya yi har ta kai aya bai ce komai ba sai can ya ce"to yanzu Umma mene ne abin yi? Me ya kamata mu yi?". Ta saki sakakken ajiyar zuciyan da har sai da na ji sautin fitarsa kafin ta sama damar furta abin da yake kwance a ƙasan ranta. "Ina tunanin idan Allah ya kai mu gobe mu ƙira Malamai su zo, a kewaye

Table of Contents

Chapters

98 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});