Chapter 68
Chapter 68
kika shiga lokaci guda fa kika fita daga cikin hayyacinki, babu wani wanda zai gan ki a wannan lokacin ya tsammata miki za ki ƙara yin numfashi ko da na sakon ɗaya ne a cikin wannan duniyar. Waɗannan mutanen da suka ikirarin cewar su ƴan uwanki ne su ne suka kawo ki asibiti tare da ni aka yi komai don jiya har sai dare kafin na bar cikin asibitin nan, don Likitotin sun ce babu wanda zai kwana a wajenki. Waɗannan mutane sun nuna miki ƙauna mai ƙarfi da ta amsa sunanta, a dai cikin wannan duniyar da muke rayuwa a cikinsa da mutanen kirki suka yi ƙaranci da wuya a sama masu kirki da tausayinsu. Daman ki na da ƴan uwa maza ne? Don a labarin da kika ba ni kin ce ke ce ɗiya ɗaya tal a wajen iyayenki?". Na furzar da iska mai zafi daga bakina kafin na soma ba ta amshoshin tambayoyinta. "Tabbas kam yadda suka ce su ɗin ƴan uwana ne, sai dai ba muharramaina ba ne. Mahaifiyarsu ce yayar mahaifina uwa ɗaya uba ɗaya. Mai farin kayan shi ne Yaya Alhassan wanda aka so haɗa ni aure da shi ɗayan kuma ƙaninsa ne Amir wanda yake bin bayansa, idan ba ki manta ba su ma na ba ki labarinsu". Cike da mamaki ta riƙe haɓa"yanzu Amatullah wannan zankaɗeɗen saurayin kika ƙi aura? Shi kuwa me ye laifinsa? Ga shi da kyau, ga ƙira da kuma kwarjini da ɗin da ɗawa ga kuma daɗin murya". Jinjina kawai na yi ba tare da na ce da ita uffan ba don na lura da yanayinta ko da na cewa wani abu, ba lalle ba ne ta fahimta balle har ta fahimci halin da zuciyata take ciki. "To yanzu me ye dalilin wannan zuwan da suka yi? Don fa sai da aka ɗeba ƴan kallo tsakaninsu da Hajiya Babba ta yi musu tijara mai wasali, wannan ƙaramin har sai da ya fusata ainun don har sai da ya yi yunƙurin kai mata mari Aminu ya amshe cikin faɗan. Nan ta tada tijarar sai an biya ta kuɗin hayan ɗakinta da kika zauna a cikin kaf, Aminu ya bijiro da na shi buƙatar sai da aka biya shi wai kuɗin ɗawainiyyar ciyar da ke da ya yi a lokutan baya. Take suka karɓa lamban asusunsu suka tura musu kuɗin, kafin Hajiya ta bari suka kawo ki wannan asibitin ta kuma gindaya musu sharaɗin yadda suka fita da ke a cikin gidan nan, to su tabbatar da cewar kin fita ke nan har abada ko kin dawo sai dai ki nema wani masauƙin amma dai ba cikin gidanta ba". Cike da damuwar da yake barazanar tarwatsa zuciyar da take kwance a cikin ƙirjina, na kai hannuna na dafe kaina da yake sarawa da ƙarfi. "Innalillahi wa inna ilahirin raji'un! Me yasa Hajiya kuwa za ta yi mini haka?". "Babu wani dalili illa na baƙin ciki da tsanar da ta yi miki tun farko, mussamman da kika ƙi bin layin da ragowar ƴan matanta suke bi. Ga ki da diri da kuma sura komai cif-cif kin ga kuwa ai da kin ba da kai bori ya hau ba ƙaramin harka za a buga da ke". "Ai kuwa in sha Allahu na bar cikin gidanta ke nan har abada". Zinariya ta yi hanzarin tarar numfashina"ban ga ne kin bar gidan har abada ba ina za ki koma ke nan?". Na kwashe duk yadda muka yi da su Yaya Alhassan na sanar da ita, ina gama ba ta bayanin kawai na ga ta fashe da kuka sosai lamarin da ni ma ya saka ni kuka muka rungume junanmu babu mai lallashin wani a cikinmu. Ni na fara yin ƙarfin halin tsagaita na wa kukan na ɗago kanta ina share mata hawayen fuskanta tare da faɗin"zan koma gida Zinariya Allah ya yanke mini wannan zaman ƙasƙanci da wulaƙancin. Ke ma ina mai ba ki shawara ki yi wa kanki karatun ta nutsu ki koma gida, na tabbatar da cewar iyayenki za su amshe ki". Cikin muryar kukan da ya gama galabaitar da ita ta ce da ni"Amatullah ba zai yiyu yanzu in ce zan koma gida ba in kuma na yi yunƙurin hakan to ina mai tabbatar miki da cewar sai dai a komar da gawata. Sa boda mun riga da mun shiga cikin ƙungiya mun kuma yarda za mu yi biyayya ga dukkan dokoki da sharaɗoɗinta duk wanda ya ce zai fita to ɗayan biyu ne ko dai ya haukace ko kuma ya bar cikin duniyar gabaɗaya. Ke ma da ba kya cikin ƙungiyar ina jiye miki tsoron abin da Hajiya Babba za ta iya yi a kanki mussamman yadda suka yi musayar yawu da ƴan uwanki". Gabaɗaya jikina ya yi sanyi ƙalau na kasa cewa komai har sai da ta ci gaba da maganar"ke dai Allah ya ƙaddara ba za ki saɓa masa ba ta hanyar keɓe wa da wani ɗa na mijin da ba halal ɗinki, ƙaddarar rayuwa a barikin ce kawai a kanki amma babu ƙaddarar saɓawa Ubangiji. Na taya ki murna da ba ki bari sheiɗan ya yi nasara akan yi ba haka nan ba ki taka rawa a lokacin da yake buga gangar sheɗancinsa ba, za ki koma gidan iyayenki cikin aminci da kuma mutunci Amatullah. Ga wannan wayar ki tafi da ita idan kin nutsu ki ba wa ƴan uwanki su saurari abin da yake ciki na san cewa za su fahimce ki". Tana gama maganan ta riƙo hannuna ta damƙa mini wayar yayin da ta fashe da wani kuka da ni ma ya tursasa hawaye kwaranya daga idanuna. Ban iya ce mata ko kanzil ba har zuwa lokacin da Yaya Alhassan suka dawo cikin ɗakin tare da Likitan ya duba ni ya kuma tabbatar da cewar jikina ya yi sauƙi ya rubuta mana sallama tare da wasu magungunan da ya ce lalle a saye su, kuma na fara amfani da su da gaggawa. Haka muka fito har cikin haraban asibitin hannuna saƙale cikin na Zinariya, da Yaya Alhassan yake ta yi mata nasihar ta tuba da koma zuwa ga Allah da ya kasance gafurul rahim. Kanta kawai take gyaɗa masa don da ni da ita mun an cewa akwai ɓoyayyan matsalan da bala'in da yake tattare da hakan. Ko da muka zo rabuwa da ita ji na yi tamkar raina zai bar gangar jikina. Haka muka sha kukanmu Amir ya din ga ba mu haƙuri da ƙyar muka saki hannun juna, haka muka rabu muka hau adaidaita muka nufi tasha, muna isa muka saka motar garinmu ba mu yi mintuna goma ba ta shiga muka soma tafiya. Tun da muka soma tafiya ƙirjina yake bugawa har muka isa cikin garin, ina fitowa daga cikin motar na ji gabana ya faɗi da har sai da na runtse idanuna, muka tara adaidaita muka shiga na lura har zuwa wanna lokacin Yaya Alhassan fushi yake yi da ni hatta magana ma sama-sama yake yi mini shi ma sai ya zama dole ne. Mu na iso ƙofar gidan Anty Sawwama na ji wani zazzafan zazzaɓi ya lulluɓe wajen gabaɗaya ya sauya miki tamkar wacce ta yi shekaru goma cur da barin cikin gidan, da ƙyar nake ɗaga ƙafata da na
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98