Chapter 72
Chapter 72
ba ta zauna da kowa zaman lafiya a cikin gidan nan ba. Ni ce kawai ta zame min dole ni ma ɗin kuma na fara gajiya tun da daman Ubangijinmu ne ai kawai ya ba ya gajiya da mu Bayinsa". Ji na yi kaina ya yi mini dum jikina gabaɗaya ya ƙara sake wa, wani baƙin duhu da babu ko da ɗigon haske a cikinsa ya gilma ta cikin idanuna. Duk da idan zaune ji na yi kamar ina shirin faɗuwa ƙasa, hakan ya sanya ni yin zaman ƴar bori dirshan a ƙasa. Na juyo da kaina ina kallon fuskar Umma da tun da Umman Amira ta soma zancen ta yi ƙasa da idanunta hawaye su na ci gaba da zuba daga gare su. "Umma me yasa kika zauna haka har jinyar nan ta yi nisa, ba tare da kin nema maganinta ba"?". Kafin ta ba ni amsa Umma Amira ta yi caraf ta amshe zancen cikin faɗin"to ke kuwa Amatullah jinya ba dole sai da kuɗi ba, to haka kawai ake tashi a nema maganin ba tare da ko sisi ba?. Ko wancan aikin yanke ƙafan da aka yi Alhassan ɗan Gwaggonki da yake su ma ƴaƴan kirki ne irin albarka da suka kwankwaɗi tarbiyya a cikin kofin girmamawa shi ne ya yi ƙundunbala ya biya kuɗin aikin da na magungunan da aka rubuta haka nan ya yi mata siyayyar kayan abinci ya kawo, shi nake ɗan tsakura ina dafa mata har zuwa wannan lokacin da kika zo kika iske ta tana numfashi". "Innalillahi wa inna ilahirin raji'un!". Na furta cikin wani iriyar muryar mai tattare da tarin rauni saka kaina tsakanin tafukan hannayena tare da rushewa da wani matsanancin kuka mai tsanani. "Ba kuka za ki yi mata ba Amatullah addu'a za ki yi mata Allah ya kawo mata sauƙi da mafitan halin da take ciki. Idan kuma wannan jinyar ba na tashi ba ne to Allah ya sauƙaƙa mata tafiyar ya sa can ya fi mata nan kasancewa alkhairi a gare ta. Ki tashi ki fito waje ki ɗan sha iska don warin cikin ɗakin nan babu makawa sai ya kumbura miki ciki, ko kuma ya haifar miki da wani cutar mai zaman kanta". Umma Amira ta yi zancen ta na kai hannunta ta rufe hancinta tare da juya wa ta fice daga cikin ɗakin. Na tsinkayo amon Anty Zulaihatu cikin rarrashi ta na cewa"ba kuka za ki yi ba Amatullah addu'a za ki yi mata, sannan kuma a fara neman mafitan nema mata lafiya. Wanda daman akan hakan ki ka zo ki ka same mu, akwai wasu gidauniyar da suke ɗaukan nauyin majinya mussamman masu irin lalurarta a yi musu aiki kyauta, magani ma kuma kyauta. Tunin Yaya Alhassan ya saka sunanta kuma in sha Allah akwai cikakken yaƙinin cewar za a dace don haka ki kwantar da hankali komai ya yi farko zai yi ƙarshe da iznin Allah". Ban iya cewa da ita komai sa boda kukan da ya gama galabaitar da ni ainun, rurin da wayarta ya yi shi ya tilasta mata tashi ta fita daga cikin ɗakin don ta amsa ƙiran, ban ga laifinta don ta fita ba don tabbas zama ciki ɗakin sai ka kai zuciyarka nisa kuma sai hakan ya zama dole a gare ka watau ba ka da wani zaɓi. "Amatullah". Umma ta ƙira sunana da hakan ya sanya ni ɗaga kai ina kallon fuskarta, ta riƙo hannuna ta sanya cikin na ta. Hawaye suna gudu a bisa kuncinta ta ce"Amatullah kin ga yadda rayuwa ta yi da ni ko? Tun bayan rasuwar Manniru nake ta haɗuwa da jarabawa kala-kala daga wannan sai wannan kamar wacce aka saka wa hannu a cikin lamarin. A da na yi zaton barin sa cikin duniya zai ba ni wani dama ne da zan ci duniyata da tsinke sakace ta yadda zan sakata na kuma wala sai dai ashe kallon tsire nake yi wa rogo, na wofantar da ke sosai na ƙunsawa dangin Manniru ƙunci da baƙin ciki ba wai don ba na ƙaunar ki ba. Duk abin da na yi na yi sa da nufin ƙuntatawa Sawwama da kuma ƴaƴanta sai dai ban sani ba ashe wuƙa na ɗauka na daɓa wa kaina ba tare da na sani ba rashin Manniru ya sa ni fahimci komai isa, izza da taƙamar mace dole ta na buƙatar jagorancin na miji a cikin rayuwarta. Rashin Manniru ya sa ni na fahimci dole akwai wasu buƙatun da komai gata da azurkinki a cikin duniya ba za ki taɓa iya biya wa kanki su ba, rashin Manniru ya sa ni na fahimci duk macen da take zaune ba tare da wani tsayayyen na miji a cikin rayuwarta ba walau uba, miji ko kuma ƴaƴa to ita da hanyar Zamfara ɗaya suke a ɓangaren rashin tsaro. Amatullahi tun da wannan jinyar ta same ni babu ranar da garin Allah zai waye ba tare da na yi kukan rashinki ba lokuta da yawa na kan zauna na yi tunanin a wani irin hali na jefa rayuwarki a cikin yanzu? Tabbas Manniru ya yi gaskiya da ya ce DAFIN HARSHE ya fi dafin da ke tattare da bakin maciji da duk wani dabba mai cutarwa ga lafiyan ɗan Adam, mussamman kuwa bakin uwa don kamar yadda duk addu'ar da ta yi wa ƴaƴanta Allah yake amsar sa haka nan idan ta furta mummunan kalma gare su, sai hakan ya yi tasiri akan su ko ba daɗe ko ba jima ƙarshe kuwa ita za a bari da cizon ɗan yatsa. Kowa ya juya min baya a cikin gidan sai dai daidai da rana ɗaya ban taɓa ganin laifinsu bisa hakan ba tun da ni ma a lokutan baya ban rangwanta musu. Idan na ga yadda ƴaƴansu suke yi musu hidima ko da kowa hidimar aikace-aikacen cikin gida ne sai na ji hawaye su na zubo wa daga cikin idanuna tunaninki da na halin da na je da rayuwarki a ciki sai ya dawo min sabo dal a cikin raina". Dole ta tsagaita sa boda tari mai ƙarfi da ya sarƙafe ta, lokaci guda ya fitar da ita daga cikin hayyacinta. Na ɗauki kofin da yake na zaba ma da gudu waje da nufin ɗebo mata ruwa, har na buɗe rangan zan ɗebo ruwan na ji an riƙe mini hannuna. "Kar ki sake ki haramta min ruwan da nake sha kuma nake ibada da shi, ta hanyar soma min wannan ƙazamin kofin marar tsafta da ya fito daga cikin ɗakin wulaƙantacciyar matan can da ba ta san mutuncin ɗan Adam ba". Cak! Na tsaya ina bin matar da kallo don a tsawon zamana a cikin gidan ban taɓa ganin fuskarta a cikin gidan ba, ko da kuwa a zuwan baƙunta ne. Muryata ta na rawa na ce"don Allah ki yi haƙuri ki ba ni ruwan nan ko kaɗan ne, na kai mata ta sha tari ya sarƙafe ta ga shi nan ma ki na jin sautinta". Na ƙare zancen wasu hawayen su na gudu a fuskana. Tsaki ta buga mini tare da sa dukkannin ƙarfinta ta ture ni Allah ya rufa mini asiri ban kai ƙasa ba ta rufe rangan kirif, ta tsaya a wajen tare da riƙe ƙugu tana jijiigawa. Numfashi mai
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98