Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 2

Chapter 2

Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel – Full Story 1,222 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ƙanwar uwata ba ta dawo da ni cikin hayyacina. Na dafe cikina da hancina suke kukan yunwa na waigo da nufi ɗauko ledar da Aminu ya kawo mini na ga waje wayam babu shi babu alamarsa. Ta yi zumbur na miƙe ina ta waige-waige amma ban ga komai ba hatta pure water guda ɗayan da na ajiye ban gani ba. Na durƙushe akan gwiwoyina ina shararo kuka da dukan ƙarfina, ga wani yunwan da nake fama da shi kamar ƴaƴan hanjin cikina za su tsintsinke, tun ina durƙushe sai da na kwanta a ƙasa na dinga juyi riƙe da cikina da yake murɗawa. Na kasa yin bacci tsabar yunwan da yake nuƙurƙusata take wani zazzaɓi mai zafi da ratsa jiki ya rufe ni na koma sauƙe numfshi da ƙyar. Da wani irin kuzari Anty Sawwama ta wayi gari ranar ta fito waje ta soma kici-kicin haɗa wuta domin ɗaura abin kari, tana cikin aikin Umar a fito ya iske ta ya durƙusa har ƙasa ya gaishe ta ta amsa fuskarta ɗauke da walwala, tare Yaya Alhassan da Amir ma suka fito suka tsuguna suka gaishe ta ta amsa tare da sanya musu albakar da addu'ar Allah ya datar da su a cikin wunin wannan ranar. "Umma ke da kanki za ki yi girkin ba za ki ba ri Asma'un ta zo ta taya ki ba". "Har yaushe zan jira zuwan Asma'u ita ma da sai ta gamo aikin gidansu kafin ta zo. Ina so yau na yi girki na musamman ga Amatullah don tun gabannin faruwar wannan lamarin babu wani abin da take ci na kirki". Ta ja dogon gashin ta fesar kafin ta ci gaba"wallahi yanzu ba ni da wani burin da ya wuce ganin Amatullah cikin farin ciki. Ba ni da wani sauran buri da ya zarce na ga rayuwarta ta gyaru wanda ya aikata mata wannan aika-aikan kuma a hukunta shi daidai da abin da ya aikata". Cikin jimami Amir ya furta"ai wallahi da zan ga wannan mutumin sai na yi masa lakanin da ko uwar da yi naƙudarsa, idan ta gan shi ba za ta shaida sa ba". "Babu wannan maganar Amir amma tabbas doka za ta yi aiki akan sa. Ba ma shi kaɗai ba hatta matar da aka yi abun a cikin gidanta sai ta ɗanɗana kuɗanta". "Hakan shi ne daidai, Allah ya datar da mu". Anty Sawwama ta yi furucin da duk suka amsa da amin, tare suka yi aikin don daman ta sabar da su akan hakan, sai da suka gama haɗa komai aka tattare wajen Umar ya shimfiɗa tabarma aka jera kayan karin kumallo. "Bari na je na taso ta". Anty Sawwama ta yi zancen tana tashi ta nufi ɗaki wayam ta tarar da ɗakin babu kowa, take ta dafe ƙirjinta cikin tsananin tashin hankali ta dudduba ɗakin hatta katifa sai da ta ɗaga. A fito jikinta yana ta rawa su Yaya Alhassan duk suka taso suna tambayar lafiya. "Ba ta ciki ban ga Amatullah ba ta cikin ɗakin". "Ba ta ciki kuma Umma?". Yaya Alhassan ya yi zancen yana faɗawa cikin ɗakin, shi ma babu inda bai duba ba amma wayam babu ko alama haka ya fito jikinsa a sanyaye aka karaɗe ko'ina a cikin gidan. Banɗaki, kicin, ɗakin ajiya babu inda ba duba ba. Suka tsaya cirko-cirko kowa da abin da yake saƙawa a cikin ransa. "To Umma ko ta fita ne ba mu sani ba?". "Amir ina za taje? Wani gida ta sani a cikin unguwan nan? Wajen waye za ta fita ta je ta?". Cikin damuwa Yaya Alhassan ya ce"Umma ki kwantar da hankalinki in Sha Allah babu wani abun da zai faru, bari mu fita mu duba. Da yarda Allah Amatullah za ta dawo cikin aminci". Ya juya yana kallon Umar"ka zauna tare da ita bari mu je da Amir". Yana gama faɗin haka suka fita, haka suka karaɗe cikin gari duk inda suke tunanin za a dace sai da suka je amma ba yi dace ba. Bayan sallan asr lilis suka dawo gida. Anty Sawwama tana ganin shigowan su ta miƙe"ya na gan ku haka ina ita Amatullah ɗin?". Ba su amsa mata ba sai da suka ƙariso suka zauna suna. Duk su biyun suka kasa cewa komai illa kallon juna da suke yi. "Alhassan ka buɗe baki ka yi min magana mana. Ina Amatullah take?". "Umma babu inda ba mu duba ba amma ba mu same ta ba. Duk inda muke tunanin da a dace mun je, kaina gabaɗaya ya kulle ina Amatullah za ta je wanda ba za ta iya sanar da ɗaya daga cikinmu ba?". Da hanzari Amir ya ce"to ko wajen Ummanta ta je?". Anty Sawwama ta jijjiga kanta alamar a'a"ba ta je wajen mahaifiyarta ba don wannan ƙawar tatan da suke gida ɗaya Amira ta zo nan gidan wajen ta. Wanda hakan yake nuni da cewar ba ta je can ba, kuma na ƙira Zulaihatu ma ta ce ba ta je wajen ta". "Innalillahi wa inna ilahirin raji'un! To ina Amatullah ta shiga?". Haka suka zauna jimgum-jimgum kamar masu karɓan gaisuwar mutuwa, babu abin da Yaya Alhassan yake yi face ƙiran wayan dangi yana tambayar su ko suna tare da Amatullah. Amma duk wanda ya ƙira ba a dacewa. Ya sauƙe ɓoyayyar ajiyar zuciya yana zare wayan daga kunnensa tare da faɗin"Umma ba a dace ba, ba ta je wajen su ba". "Innalillahi wa inna ilahirin raji'un! Umar ɗauko min hijabina na fita neman yarinyar nan don zama bai kama kama ni ba". Da sauri Yaya Alhassan ya riƙo hannunta ya zaunar da ita"don Allah Umma ki kwantar da hankalinki kin san fa kina da hawan jini. Bai kamata ki fita ba a wannan halin da kike ciki, ki bari mu mu je mu nemo ta a duk inda ta shiga". Ta kafe shi da ido"Alhassan jiya cikinku akwai wanda ya yi magana da ita ne?". Ya sadda kansa ƙasa"ni ne na yi magana da ita ƙarshe". "Wani magana suka tattaunawa da ita?". "Umma maganar da muka yi da ke ne. Kuma ban mata dole ba na ba ta daman ta je ta yi tunani kafin ta yanke ko wani irin hukunci". Ta ɗan jim kafin ta ce"Allah ya sa ba abin da nake tunani ba ne ya faru". "Umma me ye kike tunani?". "Wataƙila ta gujewa aurenka ne Alhassan". Ya waro idanunsa waje"me ye zai sa Amatullah gujewa aurena? Umma shin ina da wani aibun ne?". Ta dafa kansa"ba ta da wani aibu Alhassan amma wannan hashashe ne kawai na zuciyata wanda ba na fatan hakan ya kasance". A sanyaye ya furta"to Umma bari mu je mu ƙara duba. Amma don Allah ki kwantar da hankalinki". Murmushi kawai ta sakar masa suka tashi suka fita ba su dawo ba sai bayan sallan isha'i suka shigo cikin gidan cikin mutuwar jiki. "Ba a gan ta ba ko?". Anty Sawwama ta furta yayin da suke shigowa cikin gidan. Sai da suka zauna kana Amir ya yi ƙarfin halin faɗin"Umma ba a dace ba". Ta sauƙe tagwayen ajiyar zuciya kafin ta ce"Amatullah amana ce a gare ni ba zan so duk abin da zai cutar da ita. Yanzu ban san halin da take ciki ba". "Umma ni babu abin da nake tunani

Table of Contents

Chapters

98 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});