Chapter 1
Chapter 1
[12/3, 2:54 PM] Aeesher: *DAFIN HARSHE* ©️ Maimuna Tijjani Iyam _________________________________________ Page 4️⃣1️⃣ Na daɗe ina kukan har sai da na gaji don kaina na tashi na share hawayena, so nake yi na je na yi alwala na gabatar da salla amma ban san ta inda zan fara ba ga shi ina son shiga banɗaki na tsaftace jikina kafin na yi sallan. Ganin wankin hula yana neman ya kai ni dare ya sani tashi na fito waje, cike gidan yake da mutane jinsin maza da mata kowa yana harkan gabansa daga matan har mazan babu wani shigar arziki balle ta mutunci. Mafi yawan matan zani ne a jikinsu ɗaurin ƙirji mazan kuwa gajeren wando da ya tsaya daidai gwiwansu masu kunya daga ciki suka ƙara da singileti. Na fi mintuna biyar a tsaye a ƙofar ɗakin na kasa gaba na kasa baya illa bin kowa da nake yi da ido. "Madam lafiya kin yi tsaye sai ƙare mana kallo kike yi in ce dai lafiya ko?". Na yi an yi zancen a zafafe kamar za a rufe ni da duka, da sauri na waiga don ganin wanda ya yi furucin. Wata matashiyar budurwa ce tsaye ta riƙe ƙunta tana ƙare mi kallon tsaf kamar yadda ni ma nake bin ta da kallo. Kafin na ce wani abu ta daura mini mari na yi saurin dafe kuncina don ba ƙarya marin ya shige ni sosai har sai da na ji idanuna sun kawo ƙwalla. "Ke waye da har ina yi miki magana za ki tsaya kina kallona maimakon ki ba ni amsa? Yau sai kin faɗa min uban da ya tsaya miki a cikin gidan nan da har ya ba ki damar da za ki yi min wannan ɗiban albarkan". "Me na yi miki za ki mare ni?". Na yi zancen har izuwa lokacin ina dafe da kuncina, da alama tambayar ta fusata ta don sai da ta riƙe haɓa kafin ta furzo zancen. "Kan uban can! Lalle ba ki san da wacce kike magana da ita ba ne shi yasa kika tsaya a gabana ina faɗa ki na mayar mini da martani. To yau zan nuna miki ƙarshen barikinki da iya shegen da kike ji da shi". Ta kacumo wuyan hijabina ta riƙe tamau har sai na soma tari, duk cikin dandazon jama'ar tsakar gidan babu wanda ya taso balle ya kawo mini ɗauki. Kowa ya mayar da hankali kan abin da yake yi. "Me ye nake gani haka Baraka? Kashe ta za ki yi ko kuwa? Sakar ta na ce". Hajiya Babba ta yi zancen yayin da take fitowa daga ɗakinta ta fincike hannun Baraka daga jikina. "Baraka na sha gaya miki cewar ba na son rigima a cikin gidan nan. Babu wanda nake ajiye kara ya tsallake shi face ke don hakan ba za ka tara min ciwon kai ba. Yanzu ba sai an jima ba ki shiga ki haɗo duk abin da yake mallakinki ne ki fice ki bar min cikin gida, tun da ba kuɗi muka haɗa muka gina gidan tare da ke ba". Take jikin Baraka ya soma rawa ta zube a ƙasa ta na magiya. "Don girman Allah Hajiya ki rufa min asiri kar ki bari na tozarta na kunyata a idanun maƙiya. Kin san yanzu ƙiris ake jira ya faru a soma yamaɗiɗi da kai. Hajiya ki rufa min asiri wannan shi ne na farko kuma na ƙarshe". Cikin zafin rai Hajiya ta soma cewa"sanin kanki ne Baraka ni ba na yafiya kuma ba na sauƙa daga kan maganar da na riga na furta. Don haka ki shiga ki haɗo kayanki ki bar min cikin gidan, daman na sama wanda suke son ɗakin kuma har na dafe ƴan sulallana". Tana dasa aya a nan ta waigo kaina. "Ke kuma me ye kike buƙata?". Na yi ƙasa da kaina kafin na ce"banɗaki zan shiga, sai kuma ina so na yi alwala". Ta nuno ni da ƴar manuniyar ƴatsarta kafin ta furta"zan ɗaga miki ƙafa ne kawai saboda ke baƙuwa ce kuma Aminu ya kawo ki to za ki ci albarkacinsa. Zan ba ki ruwa da buta da bargon kwanciya wanda za ki yi amfani da shi, amma ina so ki sani kuma ki sa a cikin kanki cewa a gidan komai na sayarwa ne komai da kike ji da gani ke za ki nemawa kanki hatta ruwan wanke ido kin ji ni ko?". Jikina yana ɓari na ce"e na ji na gode sosai". Ba ta tanka mini ba ta shige ɗaki babu jimawa ta fito, ta ba ni bango, buta sabuwa sai kuma pure water guda uku. Na karɓa na durƙusa har ƙasa ina yi mata godiya, ba ta bi ta kaina ba ta yi shigewarta cikin ɗakinta bayan ta gama gindawaya Baraka gargaɗin kar ta kuma fitowa ta iske ta ba ta bar cikin gidan ba. Na shiga ciki na ajiye bangon na zuba ruwan guda biyu a butan na bar ɗaga na sha, na fito na rasa gane ina ne banɗakin don haka na isa wajen wasu mata na yi musu sallama. Maimakon su amsa sai na ga duk sun kafe ni da idanuna kamar wacce ta zo da wani sabon abu. "Don Allah ni baƙuwa ce a gidan nan yau na zo. Banɗaki nake nema ina so na shiga". Duk su ukun suka fashe da dariya har da tafa hannu suka mayar da ni kamar magiji da sun kalle ni sai su tuntsire da dariya. Haka na gaji da tsayiwa na bar wajen na koma can gefe na tsaya. "Ki na neman wani abun ne?". Na ji an furta a kusa da ni. Na ɗaga kaina ina ƙarewa wacce ta yi zancen kallo sanye take da hijabi fari irin wanda ake ƙira da sunan half sunna. Na ja dogon numfashi na fesar kafin na ce"ni baƙuwa ce banɗaki nake nema". Ta yalwata annurin fuskarta kafin ta ce"mu je mana to na nuna miki". Ta yi gaba ina bin ta a baya har muka isa bakin banɗakin ta yi mini ishara da hannunta alamar na shiga. Na sakeke na tsaya ganin mutane tsaye cirko-cirko a ƙofar banɗakin suna lamarin gabansa babu abin da ya sha musu kai. Fahimtar abin da nake nufi da abin da yake yi mini yawo cikin raina ya sa ta faɗin"kar ki damu ki shiga abin ki, zan tsaya miki a wajen babu wanda zai shigo kanki". Na waro idanuna waje cikin firgici na ce"a shigo kaina kuma?". "Kaɗan ne daga cikin abubuwan da mutanen cikin gidan nan za su iya aikata. Don haka ki shiga abin ki ina tsaye a nan babu wanda zai shigo". Na jinjina kaina ba don na gamsu da abin da ta ce da ni ba, na shiga banɗakin na yi abin da zan yi na fito sai dai duk a firgici nake. Na yi alwala muka dawo ciki na yi mata godiya sosai ta nuna mini babu komai na shige ɗakin da aka kai ni. A bisa tabarman na yi sallan magrib da isha'i ko da na shafa addu'ar da na yi na zauna, na zabga tagumi ina tunanin makomar rayuwata da yadda lamura suke sauyawa. Na daɗe a zaune har sau da dare ta yi nisa, kafin yunwa da ba kasancewa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98